Tsakure:
Ƙa’idojin rubutu dokoki ne ko ladubban da ya
kamata mai rubutu ya kiyaye wajen rubutunsa. Shi ya sa harshen Hausa kamar sauran
harsuna da suka bunƙasa yana da nasa ƙa’idojin da aka shimfiɗa
domin rubuta shi tsawon lokaci, musamman a tsarin rubutun boko. An gudanar da tarurruka
a mabambantan wurare bisa manufar daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa, tun daga shekarar 1966 zuwa 1980. Ire-iren waɗannan
taruka su suka haifar da ƙa’idojin rubutun da
ake amfani da su tun bayan yarjejeniyar da aka cim ma a taron Yamai na ƙasar Nijar a shekarar 1980. Tsawon shekaru
talatin da tara (1980-2019) daga waccan yarjejeniyar, an sami gudummawar masana
da manazarta da dama (Yahaya, 1988; Sa’id, 2004; Bunza, 2002 da sauransu) wajen
ɗabbaƙa ƙa’idojin rubutun Hausa cikin littattafan da
suka wallafa. Sai dai duk da wannan ƙoƙari, rubutun Hausa na fuskantar barazana da
karan-tsaye daga masu tu’ammali da rubutun. Saboda haka wannan takarda ta waiwayi
jiya ta fuskar tarurrukan daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa da aka gudanar tun daga Bamako a shekarar 1966 zuwa Yamai a shekarar
1980 da zummar jaddada irin waɗannan taruka a matsayin kafa ta daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa domin amfanin yau da
gobe. Takardar ta haska fitilar samar da mafita ga barazanar da rubutun Hausa ke
fuskanta sakamakon bijire wa tsayayyun ƙa’idojin
rubutun Hausa da wasu ke yi a rubutunsu.
Tarurrukan Daidaita
Ƙa’idojin Rubutun Hausa Cikin Tarihi Daga
Bamako Zuwa Kaduna: Ina Aka Fito? Ina Ake? Ina Aka Dosa?
Na
Abdullahi Mujaheed
Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna
Waya: +2348069299109, +2348156747550
i-mel:mujaheedabdullahi@gmail. com
Da
Musa Rayyanu Sulaiman
Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna
Waya: +2348030977378
i-mel: rayyanlere@gmail. com
1.0
Gabatarwa
Ilimin rubutu, wato amfani da zayyana wasu
alamomi a kan takarda, ko a kan wani abu mai bagire don sadar da magana wadda ɗan’Adam ya fi faɗin ta da fatar baki, a ji shi da kunne,
ya samu ne ga ɗan’Adam a wani lokaci mai tsawo, kuma ana amfani da alamomin
rubutu iri-iri ne a sassa daban-daban na duniya, (Yahaya, 1988:1). A tarihi an fara rubuta Hausa
cikin ajami[1] ne, tun kafin
Turawan mulkin mallaka su zo ƙasar Hausa. Shi ya sa ko da Turawa suka
zo, wasunsu sai da suka yi amfani da rubutun ajami kafin dasa tsarin rubutun boko
a ƙasar Hausa. An daɗe ana rubutun Hausa cikin boko ta bin hanyoyi
mabambanta musamman ta fuskar haɗawa da raba kalmomi da sarrafa wasu sautukan
da babu su a harshen Ingilishin da aka ari baƙaƙensa
wajen ɗora lafazin Hausar. Wannan ya haifar da yunƙuri
ta fuskoki daban-daban domin daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa, ciki kuwa har da
tarurruka a lokuta mabambanta. Wannan takarda ta bi zaren tarihi ne ta waiwayi waɗannan tarurruka tare da jaddada muhimmancin
cigaba da gudanar da ire-irensu domin tabbatar da daidaito a rubutun Hausa musamman
a wannan ƙarni na 21 da ilimin karatu da rubutu ya
yawaita cikin al’umma, sa’annan kuma rubutun Hausa ke fuskantar barazana ta kauce
wa ƙa’idojin rubutun, walau da gangan ko cikin
rashin sani.
2.0
Hausa Cikin Rubutun Boko: Ina Aka Fito?
A ƙasar
Hausa an fara rubutu da ajamin Hausa tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka[2].
Hanya ta biyu da aka ɗora lafazin Hausa a kai ita ce ta yin amfani
da baƙaƙen
Latin wanda ake kira boko. Rubutun boko tsarin rubutun abacada ne wato baƙaƙe
da wasula a jere wanda ya samo asali daga Latin,
wato harshen Romawa kimanin shekaru 3, 131 da suka wuce[3].
Asalin rubutun boko na Romawa ne kuma yanzu da shi Turawan Italiya da Faransa da
Fotugal da Ingila da sauransu suke amfani,
(Yahaya, 1988).
A ƙasar
Denmark ta Turai ce aka fara rubuta kalmomin Hausa cikin rubutun boko, inda wani
Baturen Denmark mai suna B. G Neighbuhr ya riƙa
rubuta kalmomin Hausa yayin da yake koyon Hausa. Misali yakan rubuta kalmomi kamar
haka:
-
dudsji maimakon dutse
-
ghurassa maimakon gurasa
-
berni maimakon birni
Turawan Mishan ne suka fara ƙarfafa
boko da rubuta littattafai. Domin kuwa tarihi ya nuna cewa Turawan bincike da na
Mishan sun rubuta harsunan Afirka da dama ta yin amfani da baƙaƙen
Latin ciki har da Hausa. Waɗannan Turawa sun fara ziyartar Afirka ta
yamma a cikin Ƙ18 ƙarƙashin
wata ƙungiya mai suna Ƙungiyar Gano Afirka.
Har ila yau, a cikin Ƙungiyar
Gano Afirka da wasu ƙungiyoyin addinin Kirista na ƙasashen
Turai sun cigaba da aiko Turawa daban-daban tun daga Ƙ18
zuwa Ƙ19 domin binciken al’adu da harsuna da kuma
yaɗa
addinin Kirista a Afirka ta yamma. Daga cikin irin waɗannan Turawa da suka yi rubuce-rubuce cikin
harshen Hausa farkon Ƙ19 babu kamar Henrich Barth da James Frederick
Schon. Daga cikin littattafan da Barth ya rubuta akwai;
i.
Collection of Ɓocabularies of Central African Languages (1862)
ii.
Traɓels and Discoɓeries
in North and Central Africa
(3Ɓols),
(195759), da sauransu.
Shi kuwa J. F Schon ya zo Afirka ne ƙarƙashin
ƙungiyar yaɗa addinin Kirista mai suna ‘Church Missionary Society’ kuma ya rubuta
littattafai kan harshen Hausa da wasu harsunan Afirka, kaɗan daga cikinsu akwai;
i.
Ɓocabulary
of the Hausa Language
(1843)
ii.
Dictionaries of the Hausa Language (1876)
iii.
Grammer of the Hausa Language (1862)
iv.
Hausa Reading Book (1877)
v.
Magana Hausa (1885), da sauransu.
A shekarar 1891, Turawa sun kafa wata Ƙungiyar Hausa domin tunawa da wani jami’in yaɗa addinin Kirista mai suna Reɓ. John Alfred Robinson. Wannan ƙungiyar
ce ta aiko Charles Henry Robinson ƙasar Hausa domin nazarin Hausa da adabin
Hausa, shi kuma ya rubuta Nahawun Hausa
da ƙamusu mai ɗauke da sassa na Ingilishi zuwa Hausa da
kuma Hausa zuwa Ingilishi.
Akwai wasu Turawan da suka yi rubuce-rubuce
cikin Hausar boko kafin Ƙ20 waɗanda suka haɗa da William Baikie wanda ya rubuta Letafi Zabura (1881) da J. Lippert ya rubuta
Hausa (1886) da kuma J. Numa Rat ya rubuta
The Elements of the Hausa Language (1889), (Yahaya, 1988; Bakura, 2018; Bunza, 2018).
Wannan ya sake jaddada cewa tun kafin Turawan
mulkin mallaka, Turawa masu bincike da masu yaɗa addinin Kirista daga ƙasashen
Ingila da Faransa da Jamus da Denmark sun yi amfani da baƙaƙen
Latin sun yi rubuce-rubuce cikin Hausa. A lokacin da suke waɗannan rubuce-rubuce, Hausawa ba su fara
rubuta Hausa cikin boko ba kuma Hausawa ba su san ma akwai wani irin rubutu na boko
ba, sai da Turawan mulkin mallaka suka kafa makarantun boko a ƙasar
Hausa.
3. 0 Tarurrukan
Daidaita Ƙa’idojin Rubutun Hausa Daga Bamako Zuwa
Yamai: Ina Ake?
Batun
daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa ya samo asali tun
a shekarar 1912. A wannan shekarar ne, Hanns Ɓischer
(Ɗan
Hausa) ya rubuta wani littafi mai suna Rules for Hausa Spelling inda ya zayyana
ƙa’idojin
rubutun Hausa a cikinsa, ya kuma bayyana irin kalmomin da suka kamata a raba da
waɗanda suka kamata a haɗa.
Sa’annan ya sauya ƙa’idojin
rubuta waɗannan sautuka kamar
haka:
-
Maimakon b, a rubuta ‘b, wato ɓ
-
Maimakon d, a rubuta ‘d, wato ɗ
-
Maimakon k, a rubuta ‘k, wato ƙ
Waɗannan
ƙa’idojin,
su Mr. G. P Bargery ya bi wajen rubuta ƙamusunsa mai suna ‘Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Ɓocabulary.
’ Har ila yau kwamitin daidaita Ƙa’idojin
Rubutun Hausa na shekarar 1932, ƙarƙashin
jagorancin Farfesa D. Westermann ya shafe kusan shekara 5 kafin
cim ma yarjejeniyar yi wa b da d da k ƙugiya
suka koma ɓ
da ɗ
da ƙ, maimakon ɗige-ɗigen
da Hanns Ɓischer
ɗin ya kawo a cikin littafin
nasa, (Yahaya, 1988:126; Malumfashi da Mujaheed,
2018). An fitar
da rahoton kwamitin mai suna Hausa Orthography wanda aka buga a mujallar
gwamnati a shekarar 1938, (Ɓatagarawa,
2019).
Bayan wannan yunƙuri
kuma sai kafa Hukumar Hausa a shekarar 1955 wadda jigonta shi ne daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa. Wannan hukuma ta yi ayyuka da dama waɗanda suka haɗa da:
-
Tabbatar
da littafin ‘Rules for Hausa Spelling’
na Hanns Ɓischer
(Ɗan Hausa).
-
Cim ma yarjejeniya na daidaita wasu nahawun Hausa.
-
Tsara
littafi da ya ƙunshi yadda ake rubuta ararrun kalmomi.
-
Fito
da keɓaɓɓun kalmomi (Glossary Of Technical Terms).
(Yahaya, 1988).
Daga bisani kuma sai batun shirya tarurruka
domin daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa ta tusgo, inda hukumomi
irin su Hukumar Ilimi ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO) da Majalisar Haɗin Kan Afirka (O. A. U) suka shirya tarurruka
a mabambantan wurare da lokuta har sau huɗu; a Bamako ta ƙasar
Mali da Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya da Jami’ar Bayero ta Kano a Nijeriya da kuma
Yamai ta Jamhuriyar Nijar, tun daga shekarar 1966 zuwa shekarar 1980, (Yahaya, 1988; Ɓatagarawa,
2019).
Yahaya (1988), ya bayyana cewa duk da an
buga ƙa’idojin rubutun Hausa cikin littafin Hausa
Spelling wanda hukumar NORLA ta buga a shekarar 1958, da kuma gyare-gyaren
da Hukumar Hausa ta yi wa ƙa’idojin aka buga a mujallar gwamnati, mutane
sun cigaba da rubuta kalmomin Hausa barkatai musamman batun rabawa da haɗa kalmomi da kuma rubuta kalmomi da baƙaƙe
iri daban-daban. Wannan matsalar ce ta haifar da gudanar da tarurruka domin duba
waɗannan
ƙa’idoji da yi masu gyare-gyare ta yadda
za su sami karɓuwa har su bi jikin mutane. An gudanar da tarurrukan ne kamar
haka:
i.
Bamako
na ƙasar Mali, daga 28 ga watan Fabrairu zuwa
5 ga watan Maris na shekarar 1966.
ii.
Jami’ar
Ahmadu Bello, Zariya, ranar 21 ga watan Yuni na shekarar 1970.
iii.
Cibiyar
Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano, a watan Satumba na shekarar 1972.
iv.
Cibiyar
Nazarin Harshe da Tarihi ta Sarrafa Adabin Baka[5]
ƙarƙashin
inuwar Majalisar Haɗa Kan Afirka (O. A. U), daga ranar 7 zuwa
12 ga watan Janairu na shekarar 1980. (Yahaya,
1988; Ɓatagarawa, 2019).
Waɗannan tarurruka sun yi alfanu sosai wajen
fasalta karɓaɓɓen tsarin da ya samar da ƙa’idojin
rubutun Hausa. Domin a ƙarshen tarurrukan, an tsara tare da tace
duk ƙa’idojin rubutun Hausa, aka rattaɓa su dalla-dalla cikin rahoton taron ƙarshe
na birnin Yamai ta Jamhuriyar Nijar domin amfani da su (ƙa’idojin)
wajen rubuce-rubuce cikin Hausa.
Ƙa’idojin
da aka fitar sun ƙunshi karɓaɓɓun baƙaƙe
da wasulla manya da ƙanana da kuma auren wasali da tagwayen baƙaƙe.
Sai kuma yadda ake rubuta manya da ƙananan baƙaƙe
a wuraren da suka dace, da baƙaƙen
nasaba da dangantaka da sauransu, (Yahaya,
1988).
4. 0 Tafiyar Shekaru 39 Daga Yamai Zuwa Kaduna
(1980-2019): Ina Aka Dosa?
Daga abin da ya gabata, an fahimci cewa
an ɗauki
dogon lokaci kafin a kai ga matsaya kan ƙa’idojin
rubutun Hausa da aka yarda da su a shekarar 1980. Idan aka lura da irin ƙoƙarin
da magabata suka yi za a ga cewa tarurrukan da aka yi domin tattauna batun ƙa’idojin
rubutun Hausa sun haifi ɗa mai ido. Musamman ta la’akari da yadda
aka samar da daidaito tsakanin ƙasar Nijar da ƙasar
Nijeriya a wuraren da suka sami bambance-bambance wajen rubutunsu.
Wannan ya nuna cewa batun ƙa’idojin
rubutu al’amari ne da yake buƙatar hannu da yawa da kuma sake bita lokaci
bayan lokaci domin tabbatar da daidaito. Alal misali, cikin shekaru 14 Daga 1966
zuwa 1980, an gudanar da tarurruka domin daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa har sau 4, cikin ƙasashe uku na Hausawa da kuma ma’abota Hausar.
Kuma an gudanar da tarurrukan ne tare da masu-ruwa-da-tsaki a harkar rubutun Hausa;
tun daga masana da manazarta da marubuta da kuma gudummawar hukumomi na gida da
na ƙasashen waje irin su O. A. U da UNESCO. Sai dai me? Tsawon shekaru
39, tun daga shekarar 1980 zuwa 2019, ba a sake gudanar da irin wannan taro ba,
duk kuwa da ana samun ɓullar sababbin kalmomi da ɓullar sabubba da suke haifar da kauce wa
ƙa’idojin rubutun Hausa. Ga kuma matsalar
rashin daidaito wajen rubutu musamman a kafafen watsa labarai da kuma hawan ƙawara
da wasu marubutan suke yi wa rubutun Hausa[6].
Wannan takarda tana da fahimtar cewa, ta
hanyar shirya tarurrukan ƙara wa juna sani a kai- a kai, musamman
a kan ƙa’idojin rubutun Hausa kacokam ne hanya
mafi sauƙi da kuma muhimmanci wajen daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa da kuma jaddada shi da yayata shi, har masu tu’ammali da rubutun na
Hausa su lura kuma su amshi ƙa’idojin har su bi jiki.
Saboda haka, Sashen Harsunan Nijeriya Da
Kimiyar Harshe na Jami’ar Jihar Kaduna a wannan karon, ya yi susa a gurbin ƙaiƙayi.
Domin kuwa duk da cewa taron ba domin daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa ba ne kawai, a’a, taron ƙara wa juna sani ne kan ƙa’idojin
rubutun Hausa da daidaitacciyar Hausa da kuma abin da ya shafi kalmomin Hausa, duk
da haka taron ya samar da wata kafa ta tattauna batutuwan da suka shafi ƙa’idojin
rubutun Hausa tare da samar da wata taska da za a iya laluba domin sake fasalta
ƙa’idojin rubutun Hausa, domin tabbatar da
daidaito wajen rubutun Hausa a wannan ƙarni na 21.
5.0 Kammalawa
A wannan takarda an tattauna batun rubutun
Hausa ne, musamman abin da ya shafi tarurrukan da aka gudanar domin daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa cikin tarihi. An bayyana yadda aka fara rubutun Hausa cikin harrufan
Latin (boko) da kuma yadda aka shimfiɗa wa rubutun Hausa ƙa’idoji
bayan tarurrukan da aka gudanar har sau huɗu tun daga shekarar 1966 zuwa yau. Daga
ƙarshe aka yi tsokaci kan muhimmancin cigaba
da gudanar da irin waɗannan tarurruka domin sabuntawa da kuma
daidaita sababbin ƙa’idojin rubutun Hausa, musamman a wuraren
da akan sami bambance-bambance tsakanin masu tu’ammali da rubutun Hausa a fagen
nazari da kafafen watsa labarai da hukumomin gwamnati da masu zaman kansu da ma
ɗaiɗaikun mutane. Takardar ta jaddada cewa wannan
taro da Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyar Harshe na Jami’ar Jihar Kaduna ya gudanar, duk da ba a kan ƙa’idojin
rubutu ba ne zalla, amma ya zo a daidai lokacin da ake buƙata
domin ya zama kamar wata matattakala ce da za ta samar da tsanin da zai zama dabashirin
shirya ire-iren waɗannan tarurruka domin daidaita ƙa’idojin
rubutun Hausa a wannan ƙarni na 21. Domin an yi irin wannan yunƙuri
a baya an ga alfanunsa. Kenan waiwayen jiya, zai ba yau damar fasalta gobe da jibi.
[1] Salon rubutun ajami wanda Hausawa suka ara
sunansa ‘Magrabiyyi’. Shi ne salon rubutun da ya fi yaɗuwa a Afirka ta yamma, shi ne irin rubutun
mutanen Maroko da Tunisiya da Libiya da sauransu, (Yahaya, 1988).
[2] Turawa irin su Adam Mischlish da Robinson
da Lerouɗ, duk sun amfani da ajami a cikin ƙamusan da suka rubuta.
[3] Yahaya
(1988) ya ce tsawon lokacin ya kai kimanin shekaru 3, 100 a shekarar 1988. Daga
1988 zuwa yau 2019 an samu shekara 31. Kenan yanzu tsawon lokacin ya kai kimanin
shekaru 3, 131.
[5] Wato Centre
for Linguistic and Historical Studies by Oral Traditions.
[6] Batun ƙa’idojin
rubutun Hausa yana fuskantar matsaloli da bambance-bambance wajen rubuta wasu sautuka
da kuma wajen rabawa da haɗa wasu kalmomi, duk da cewa masana suna damuwa wajen daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa, saboda fito da ma’ana
wajen rubutu da kuma kauce wa shan wahala wajen karatu. Shi ya sa masana irin
su Bunza, 2002 da Sa’id, 2004 da Ɓatagarawa 2018 da sauransu, duk sun yi
rubuce-rubuce da dama kan ƙa’idojin rubutun Hausa. Amma duk da
haka, har yau, wasu ƙa’idojin ba su gama bin jiki ba. Saboda haka, yana da
muhimmanci a yi la’akari da kowa da kowa wajen daidaita ƙa’idojin rubutu; masana da manazarta da
kuma masu tu’ammali da harshen musamman a yankunan karkara. Hakan kuwa na iya
samuwa ne kawai ta hanyar gabatar da tarurruka na musamman domin daidaita ƙa’idojin rubutun Hausa.
1 Comments
Masha ALLAH!!!
ReplyDeleteGaskiya munyi babban Rashi wlh
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.