Ba
abin da macen da ta kwaso yara take so sai ta sami namijin da zai riƙe su
tsakani da Allah, ya kuma sa ido a kan yaranta. Sai dai ba nan gizo yake saƙa
ba! Duk wanda zai zo neman aurenta za ka iske yana da wasu yaran a gabansa…
Zan
Ƙara Aure 07:
Gaskiya Mai Ɗaci
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
Mace
ba ma ita kaɗai ba duk wanda ya rabu da abokin zamansa dalilin saki ko mutuwa
bayan da yana jin dadin zama da shi zai so a ce ya kuma samun kamarsa ko ma
sama da shi, zai yi kyau mace ta sa idon lura sosai a batummu na yau, yana da
wahala amma shi ne gaskiya, na taba yin wannan maganar a baya sai zawarawan
suka zaci ban son riƙon dan wani ne, sam ba haka take ba, na dai nuna kuskuren
da 'yan uwan miji suke yi na barin mace da yaran dan uwansu, ko na macen da
take dagewa sai an bar mata yaran, a ƙarshe ta yi ta zagin an ƙi taimaka mata.
Wani
sa'in tabbas macen ke hanawa, ƙila abin da 'yan uwan mutum ke hangowa kenan su
dage kan ba zai auri 'yar gidan wane ba don ba su da mutunci, in mutum ya koma
ga Allah kamata ya yi 'yan uwansa su kula da tarbiyar yaransa, mace ba za ta
iya ba da duk abin da ake buƙata na tarbiyya ba, matsalar ba ta kudi ce kawai
ba, akwai gudummuwar da namiji ke badawa game da tarbiyyar yara, mace ba ta iya
ba da shi, kamar dai yadda namijin bai iya ba da na macen.
Yanzu
in mutum ya rasu sai ka ga mace ta kwaso yara kaf dinsu ta nufi gidan ubanta da
su, wata ma ko rabuwa ta yi da mijin abin da ke faruwa kenan, wai ba za ta bar
su a cutar da su ba, tana ganin za ta tarbiyyantar da su ita kaɗai har su zama
mutane, sai dai da yake ba aikinta ba ne takan sha mugunyar wahala har a kai ga
ta fitar da abin da yake cikinta, wata ta yi zagin 'yan uwan mijin wai sun ƙi
taimaka mata, babban abin haushi ma wace mijin na da rai ta kwashe yaran ta
tafi da su, shi ya auro wata matar tana haihuwa masa suna rayuwa cikin kwanciyar
hankali, ke kina ta famar wahala da yara sun hana ki yin wani auren, ga
mummunar tarbiyyar ƙin mahaifinsu kin dasa musu.
Ba
abin da macen da ta kwaso yara take so sai ta sami namijin da zai riƙe su
tsakani da Allah, ya kuma sa ido a kan yaranta. Sai dai ba nan gizo yake saƙa
ba! Duk wanda zai zo neman aurenta za ka iske yana da wasu yaran a gabansa,
akwai buƙatar samun yalwataccen matsuguni na yaranta da nasa gaba daya, sai
abinci da sutura, 'yan matsalolin yau da kullum duk suna ciki, ga kudin
makarantar yara na boko da Islamiya, ƙila makarantar ma sai sun hau mota.
Abin
lura a ciki wadannan yaran lokaci guda kika taho masa da su, kin ga akwai
matsala in bai shirya yadda zai gwama zarafin tarbiyyan ba, za ki ga maza da
dama suna tambayar in bazawarar da suka gani tana da yara a gabanta, ba ƙyamar
ruƙon dan wani ba ne, damar da za a riƙe din ne, wani yana da shi wani babu, ni
dai na taba ganin wanda ya auri wata mai da daya babba, ya shigar da shi cikin
iyalansa a ƙarshe ya aura masa ƙanwarsa ya ajiye su a gidansa, sannan na taba
ganin wanda maƙwabcinsa ya rasu ya bar mata 3, ya tambayi ta farkon, babbar
kenan, dake da 'ya'ya 6 ko za ta aure shi, ta ƙi, ya tambayi ta biyu mai 'ya'ya
4, ita ma ta ƙi, sai yarinyar mai jini a jika ga hasken fata da yara biyu, bai
neme ta ba, don ba ta da abin da yake nema, wato taimakon marayun.
Ba
labari aka ba ni ba, na rayu da shi wuri guda na san shi ba sanin shanu ba,
'yar uwa zan ba ki shawara; ki yi haƙuri ki bar yarannan a wurin mahaifinsu in
auren ne ya rabu, zancen kishiya sau nawa tana azabtar da yara su zo su taimake
ta da ma yaranta a ƙarshe? In ma mutuwa mijinki ya yi ki bar wa 'yan uwansa,
wallahi ba mai hana wani arziƙin da Allah ya tsaga masa, kuma ke ma kina tare
da yaranki a duk inda suke, lokacin ne ma za su so ki sosai, don in sun zo inda
kike za su daban, kuma za ki yi musu duk abin da za ki iya.
Abin
sirri ne, in kika bar su a gidansu wanda duk ya zo tambaya za a ce kina da yara
amma suna gidan ubansu, nan da nan za ki sami miji, dole dai uwa ta amsa
sunanta koda uwar gwaza ce, kamar yadda na ce ne kina gidan mijinki za ki riƙa
taimakonsu sama da yadda suke gabanki, sannan za su riƙa zuwa wurinki kullum
kina ganinsu kina kwantar musu da hankali, wannan fa in kin yi niyyar sake aure
kenan, ba mazan ne babu ba dabara ce ba ki da ita, wani namiji ne zai zo
gidanku ya gan ki da yara a gaba kuma ki ce gidansa za ku duka? Wallahi na ga
wace mutanen kirki suke ta zuwa mata amma duk in suka bincika suka ji tana da
yara kowa sai ya kama gabansa, ita kuma tana ta kukan ba sa zama, bayan abin da
ke koransu na tare da ita.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.