Ban
sani ba in namiji yana da karatun da zai iya gamsar da mace kan cewa auren mata
fiye da ɗaya yana da amfani a
zaman-takewa ko zai iya amfanar da ita, galibi ƙetar da suke magana a kai
Zan
Ƙara Aure // 04: A Wa Aka Taimaka?
Baban Manar Alƙasim
Zauren
Markazus Sunnah
A
zahiri in mutum ya ce yana son ya yi aure kuma aka ba shi to shi aka taimaka
mawa, wannan aka sani kowa a kan haka ya tafi, shi ya sa muke ganin cewa in
mace ta fara cewa tana son mutum kamar ta tallata kanta ne, wasu ma suna ganin
zubar da ƙima ne, sai dai akwai wata falsafa ta daban, misali namiji don ya
makara bai dawo gida ba da wahala ka ga an rikice, sai dai tsoron abubuwan dake
faru a yau na garkuwa da sauransu, amma mace dole a san ina za ta? Me za ta yi?
Yaushe za ta dawo? Ina ta tsaya? Da wa ta fita?
Duk
wata uwa da take rainon yara mata ba ta da kwanciyar hankali, akwai wace ko
gida ba ta iya fita saboda tsaro, an kai lokacin da uwa take ƙoƙarin tsare
'ya'yanta mata daga 'yan uwansu a cikin gida don kar su la'anta mata su, na
taba jin wata na cewa hatta uban ba abin yarda ba ne a wannan zamanin da muke
ciki, abu ya kai abu kenan, to in aka sami wasu za su dauke miki wannan
zullumin da rashin barcin dare saboda wa'azi da jan kunnen da kike yi wa aka
taimaka mawa kenan? Ana auren biyu, uku, hudu har yanzu ga matannan, to in kuma
kowani namiji mace daya kacal zai aura ya za a yi kenan? Ko su 'yan bokon da
suka ƙi auren mata biyu sun fara dari-dari da ra'ayin cewa 'ya'yansu sai mai
mata daya, don in suka tsaya kan haka ƙarshe a bar musu 'ya'yansu.
Wani
abin dariya da na taba kawowa a wani dan shiri nawa mai taken "KA JI
MUNAFUKI" wannan gani na yi, yadda uwa ta saka diyarta a gaba tana zagi
don diyar tata ta ce ba za ta zauna ba, wai maigidanta ya dage sai ya ƙara
aure, uwar ta zage ta kab, inda ta shiga ba tanan take fitowa ba, a ƙarshe
diyar ta nuna mata cewa babanta yana neman ƙawarta, nan take lamarin ya canja,
uwar ta bar fadan ta koma zagin maigidanta wato uban yarinyar, duk da cewa da
tana gaya mata mahimmancin auren mata biyu ne ko fiye.
Ban
sani ba in namiji yana da karatun da zai iya gamsar da mace kan cewa auren mata
fiye da ɗaya yana da amfani a
zaman-takewa ko zai iya amfanar da ita, galibi ƙetar da suke magana a kai in ka
dubi hujjojinsu za ka fahimci cewa suna nufin namiji yana cikin talauci da
rashin kudi mace na ta haƙuri tana tafiya da shi a haka, lokacin da ya sami
sarari a maimakon ta huta cikin arziƙinsa sai kuma ya je ya dauko mata kishiyar
da in ba ta dage ba za ta kore ta, ƙetar namiji kenan, akwai wata mata da na ga
zaman lafiyan da take yi da kishiyarta na tambaye ta ta fada min cewa ita ta ba
wa mijin shawarar ya aure ta, don ƙawarta ce, da dai na matsa sai na ji dalili
sai ta ce to ai ita ma tana da yara mata a gabanta, kuma tana da kyakkyawar
sha'awar ta ga ta aurar da su, in kowani namiji zai auri mace guda ta ina
yaranta za su sami shiga?
Gaskiya
tana da hankali, don ba duka aka zama daya ba, yau dinnan muka yi wa wata
yarinya fada, kamar yadda babarta ta nema, uwayenta su hudu ne a wajen ubanta,
amma ma'aunin da take auna kowane namiji da shi shi ne ba za ta auri mai mata
ba, kuma dole a yi sharadi da mijin kan cewa in ta aure shi ba zai sake auro
wata ba, ko ada lokacin da matan suke ƙaranci wannan alƙawarin yana da matuƙar
wahala, bare yanzu da matan suka ninka mazan ko dai wajen haihuwa ko yawan
mace-mace dake aukawa a matattarar mazan gaba daya, Larabawa masu hankali a
cikinsu sun koma auren zumunci, yadda uwayen za su tattauna a tsakankaninsu
sannan su hada yaran don dai a sami sauƙi.
Abin
takaici mu yanzu sai muka fara fahimtar ƙalu-balen a kaikaice, muna ganin auren
shi ne matsala, mai mata ba dole ne ba ya ƙara, ƙarin ma rashin hankali ne ko
rashin adalci, sauƙaƙa sadaki yadda za a yi auren kuma zubar da ƙimar mace ne,
auren hadaka da kwamitin Hisba a Kano suka faro ba komai ba ne illa saukar da
darajar 'ya mace, yadda za a hada su kamar tumaki a rana guda a tura su, idan
ka lura da mai wannan maganar sai ka ga kodai mace ce da auren ya yi mata
hijira ta komo yaƙinsa, ko wace take zaune lafiya da mijinta ba ta son wata
macen ta sami irin abin da take samu, duka dai kuskure ne, yaushe za ki tara
yara a gabanki kuma ki ce kar maza su ƙara aure?
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.