Ticker

6/recent/ticker-posts

Ta’aziyyar Limamin Bunza Alhaji Usman Ta Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza

www.amsoshi.com

  1. Na kiri Allah ahadun jigona,
Shi wuturin nan xaya mai ikona,

Sarkin jinqai ga dukan talikkai.

 

  1. Na yi salati ga ma’aikin qarshe,


Alayenai da Sahabbai tarshe,

Tabi’ainai a saka duk bai xai.

 

  1. Yau kuma babbar magana tas saman,


Dole amayo ta zama ta daman,

Zo kusa in xan gutsura ma daidai.

 

  1. Ni dai halin mutuwa nad duba,


Ba ta da yaro haka balle babba,

Ba ta kure kan wa’adi ko tausai.

 

  1. Ta ishe mai naquda ta hau kanta,


Ba a ga xa babu uwar ta kwanta,

Shi xan yaye da gudu tar rittai.

 

  1. Mai wayo ta qi bari nai wasa,


Shi babane ta rufe labarinsa,

Barde a tsakan waqaci tag girsai.

 

  1. Ta tuqe Nomau kakar aikinai,


Mai mulki na tsakiyar ikonai,

Tai masa yanka ciki shi xai rainai.

 

  1. Je ga fatake su gaya ma zance,


Kamin zango wani yal lalace,

Ga kaya tarshe ga raqummanai.

 

 

  1. ‘Yan wasa sun tafi dubo Shago,


Dubo Xankurja giye gojirgo,

Xanwasa Garba ga labarinai.

 

  1. Tajirrai sun ka zamo goronta,


Dubi su Qaruna zuwa Xantata,

Sai labarinsu ga bakin dubbai.

 

  1. Don ilmi Bil’amu bai tsere ba,


Yau Salafus Saalihu ba su ne ba,

Ga mu gurabunsu muna gardanmai.

 

  1. Sha’irran gaske su Hassanunmu,


Alfaa Zaazii madahan jigonmu,

Sai dai adu’ar rahama don jinqai.

 

  1. In ta zo ba makawa sai kwance,


Ga mai rai ya yi zugum lalace,

Wa ka kiranai ya ji ya amsa mai?

 

  1. Al’amarin mautu akwai ban tsoro,


Tamkar zaki ya dakako taro,

Wa ka tsayawa ya ga mai kamamai?

 

  1. Duk fitina ta ishe al’ummarmu,


Take mu yi zoru ga malummanmu,

Don su kuranye muna alhininai.

 

  1. In ta zo su muka ba aikinta,


Su ke wanka su yi likkafanta,

Su ke salla, adu’a don jinqai.

 

 

 

  1. Yau ta zo babu sani ba sabo,


Ta hana kowanmu tsayawa tarbo,

Domin ta faxa gidan limammai.

 

  1. Wanga rashi namu zama nai babba,


Ba mu da jigon da ya furce baba,

Liman Usman jama’a sun shaidai.

 

  1. Babu kasala da nawa ba wasa,


Mamu sun shaidi irin halinsa,

Bai makara wa ka tsayi dakonai?

 

  1. Bai da mazauni bayan zaurensa,


Sai masalaci na tsare jam’insa,

Ham mutuwa taz zaka ta iske mai.

 

  1. Manu daxai bai da mazaunin tsince,


Zaurenai za ka ga kainai noce,

Gun Qur’aninsa shina bitanai.

 

  1. Bai da abokin rigima ko gaba,


Bai tava sa kai fitanar dangi ba,

Ko a gidanai take bai bobotai.

 

  1. Mai iya kainai yake mai kamewa,


Mai haqurin gaske mazan jurewa,

Babu kwaxai wa ka tavin irlinai?

 

  1. Annashawatai ta kiran salla ta,


In mukhtarinta ya xan tsatsanta,

Zai ciri sandarsa zuwa aikinai.

 

  1. Mai ladabi ne da kulawa sosai,


Mai fikira ne ga sanin xalibbai,

Kowa sunansa yake xoramai.

 

  1. Ba ya da jin kai da cikawar baki,


Bai da xabi’ar da ka sa ai tsaki,

Zaven Allah mutuwar ban tausai.

  1. Shakundun ne ga kiyaye doka,


Ba ku gamamma ka ga ya sha toka,

Shi ke gaisheka ga al’adatai.

 

  1. Ba ku gamamma ya qi tunkararka,


Ba ka hasara ya qi jajantarka,

Mai kirki ne a fagen jin tausai.

 

  1. Manu ruwa masu kwarare sannu,


Tun yaranta da halin yag ginu,

Har mutuwa taz zaka tax xau rainai.

 

  1. Ba don mutuwa hutawa ce ba,


Ba don ita ce qarshen mai rai ba,

Da mun zarge ta da cin haqqinai.

 

  1. Dubi irin qarshen zamaninmu,


Duk da irin munin halayyarmu,

Liman girmansa yana nan kainai.

 

  1. Bai yi takaici na hawan qarhe ba,


Bai tava shawar shi shigo mota ba,

Bai aje ko keke ba domin kainai.

 

  1. Bai da gida ban da gidan gadonai,


Aunaka tai daidai jallinai,

Haw wa’adi yay yi shi nan kainai.

 

  1. Bai tava sha’awar rigimar xinki ba,


Don haka bai yarda shiga Fati ba,

Ba shi jawabi a ci zuququnai.

 

 

 

  1. Ba ya da buri na zama hababba,


Ko haasave, a yi ba su gane ba,

Sin’ara hauru sake sai suruttai.

 

  1. Mai imani kake duk mun shaida,


Taka-tsantsan da kake mun yarda,

Ka tafi ka bar mu da tarihinai.

 

  1. Mai son Allah shi tsare haqqinSa,


Mai son Manzo (SAW) ya fake sunnarsa,

Nassi ne tabbace gun Maisammai.

 

  1. Liman Usmanu mazan gyarawa,


Babu jiyewa da yawan kushewa,

Bai da zurewa gaba an shaida mai.

 

  1. Baban Ummar bawan Allah ne,


Bai da masoka ga mutum ko wane,

Mai halayen manyan shehunnai.

 

  1. Wafatinai wata ilhaama ce,


Ta haxa kanunmu shuru ba zance,

An sallace shi gaba xai, bai xai.

 

  1. Wagga ishara magana ce tarshe,


Shi na qwarai ko ya mullo kirshe,

Mai imani bai tsamar bi nai.

 

  1. Mugu ko ya naxe maqoqonai,


Ko da giginya yaka tasbihinai,

Wa ka kula mai, ya yi alhininai?

 

  1. Don haka mai rai ya kiyaye sosai,


Kar ya yi wasar riqe imaninai,

Shaidun jama’a Allah bai qi nai.

 

  1. Don haka kurin ni mai ilmi ne,


Ko ce wa ni babban shehe ne,

Ba shi da rana a yi aikin daidai.

  1. Ga liman bai yi zama shehe ba,


Bai da xariqa bai shiga hizbi ba,

Amma ya samu cikawa daidai.

 

  1. Kowa ya yarda da addininai,


Mu duka mun yarda da imaninai,

Ba mu da suka ga irin sabgatai.

 

  1. Roqon da mukai a wajen mai jinqai,


Wannan da ya yo sama, yay yo qassai,

Yai maka rahama a cikin taskaTai.

 

  1. Allah kukanmu ga limaminmu,


Yadda yabonai ya bi alqaryarmu,

Can ga hisabi ka cike mudunai.

 

  1. Babbar qaunarmu ga aljannarKa,


Har can Firdausi Ka sa bawanKa,

Tare da maban ga da ke roqamai.

 

  1. In ka ce: “Kun”, “Fayakun” tilas ne,


Muddin Ka yarda abin diimun ne,

Mun ce: “Amin!” Ya Sarkin sammai.

 

  1. Dakanta mai neman ganewa,


Liman Usman a wajen nunawa,

Ba dogo ne ba ga talittatai.

 

  1. Shi matsakaicin mutume ne daidai,


Tamkar Saninsa zubin qiratai,

Amadu shi ko ga fari yas satai.

 

 

 

  1. Malami shi yay yi aron fuskarsa,


Ali ka tangam ga irin zatinsa,

Xan’auta Bello baqi yac cutai.

 

  1. Can ga xuminai Sa’a ta gane shi,


Ummaru aka ba natsuwar halinshi,

Ba rigima babu yawan suruttai.

 

  1. Liman Usman suturatai riga,


Sai rawaninai malagi gefen ga,

Kaftani ba shi cikin tsarinai.

 

  1. Takalminai faxe ne ko yaushe,


Bai xangarfa rigimar ‘yan tashe,

Ba shi da kuri ga irin tsarinai.

 

  1. Haurunai sun cika baki daidai,


Baki daidai da tsawon fuskatai,

Gemu daidai ga zubin kuncenai.

 

  1. Gun tafiya bai cika yin miqo ba,


Bai yin sauri kuma bai toge ba,

Sannu yake yi tafiyar malammai.

 

  1. Kambilinai daidai zatinai,


Bai da tsawo ba ya da gwaffa kainai,

Xan siriri ga zubin siffatai.

 

  1. Na’ibbainai ta’aziyya gun ku,


Ladannai sai ku tsare aikinku,

Nai muku tanzanko da fatar jinqai.

 

  1. Tammat Allah ka ji kukan Ali,


Share hawayensa ka sa mai kwalli,

Kai shi a Firdausi cikin limammai.

 

 

 

 

 

https://www.amsoshi.com/contact-us/

Post a Comment

0 Comments