Ticker

6/recent/ticker-posts

Makarkashiya: Ta Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza

www.amsoshi.com
  1. Allah na kiraye ka,


Salati nikai wa manzonKa,

Ga Sayyidina ma’aikinKa,

Muhammadu mai gari Makka,

Aminu mazan nagarta.

 

  1. Bayani nai nufin sak’a,


Cikin lafazi na mai wak’a,

Saboda kuranye gaggak’a,

Wuyanmu da an ka sa sark’a,

A kan tsananin mugunta.

 

  1. A yau mu d’ai ake dako,


Da mui zance a sa tarko,

A hau bisa kanmu ba tsaiko,

A sa muna tarnak’in iko,

Gabanmu da baya cuta.

 

  1. Musiba babba nah hanga,


Aboki tsaya ka d’an waiga,

K’asarmu tana cikin sabga,

Na rud’ani da damaga,

Da babu irinsa wauta.

 

 

 

 

 

  1. Ga tarihi na tarayya,


Zama aka yi na soyayya,

Idan aka fara jayayya,

Gabaci za a ba hanya,

A tabbata an tuk’e ta.

 

  1. A bar fitina ta gawurta,


Ana kallo ta k’asaita,

A jefa k’asa ga ragaita,

‘Diyanta a sa su tozarta,

Saboda d’iyan mak’wabta.

 

  1. A kan tsabar munafucci,


Da makircin k’abilanci,

A ware k’asa da ‘bangarci,

A sa mu cikin agolanci,

Da yin hijirar barin ta.

 

  1. Muna kallo a k’ware mu,


A yo gayya a yak’e mu,

Ana ta kashe matasanmu,

A watse dukan biranenmu,

A sa mu cikin asuta.

 

  1. Musiba duk a ce mu ne,


Idan aka hango mun gane,

A gayyato masu jan kunne,

A ce musu ga su can su ne,

Su bud’e wuta da hauka.

 

 

 

 

 

  1. K’asa duka an ka wa miki,


Mutan ciki na da jan aiki,

A tilasta su yin raki,

A kwana a tashi ba girki,

K’asa tilas barin ta.

 

  1. Buk’atar masu yak’anmu,


Gaban a raba su k’ware mu,

A karkashe masu k’azonmu,

A tarwatsa arziki namu,

Su tura d’iyanmu bauta.

 

  1. Takaici na gidan soja,


Mazajen rungumar danja,

Muk’ami sai d’iyan Neja,

‘Diyanmu a ba su masinja,

Wad’ansu su zan kurata.

 

  1. Tsaro da shirin k’asa tamu,


Suna hannun magabtanmu,

Muna kallo a k’ware mu,

Mu kasa tsayi da k’arfinmu,

Mu tabbata an kwatanta.

 

  1. Ina aka kai mu ‘yan boko,


Sarakai masu jin iko,

Da ‘yan d’amarar dakon ciko,

Birai su mayar da mu soko,

K’ashi ya kashe mahauta.

 

  1. A bi mu ana ta mammara,


Mu fad’i ana ta shusshura,

Mu kama shi’ba da bankaura,

A d’auko Igwa mu d’au gora,

A kanmu ake daka ta.

 

  1. Irin rigimar da ke Delta,


Ta k’are babu algaita,

A ba su kud’i su sai mota,

Tukuici han na ragaita,

Su zub da jinin mak’wabta.

 

  1. A ce musu ‘yan bid’an ‘yanci,


A ba su dukan muhimmanci,

Da albashi na sagarci

Su k’asura sui ta shashanci,

Batunsu ake mutunta.

 

  1. Arewa batunmu k’arya ne,


Da mui magana a ce mu ne,

Jininmu zubansa daidai ne,

Batun diyyarmu shirme ne,

Wa ka biyan k’azanta?

 

  1. Mafarin yin fa’addanci,


K’asa ta halasta zalunci,

A dinga mutunta cin hanci,

A ja d’amarar k’abilanci,

Bala’i ya rufe ta.

 

 

 

 

 

  1. Idan aka fara ha’inci,


Hana wa d’iyan k’asa ‘yanci,

Da ‘bangarci da bambanci,

Da gardancin ak’idanci,

K’asa tuni an kashe ta.

 

  1. Matasa an ka wa fanho,


Su zabura ce kakai shaho,

Suna kuwa suna eho!

Su jikkita babu mai hoho,

Kisan kai an halasta.

 

  1. Abinda ka ba ni mamaki,


A ofis can wajen aiki,

Kujera ta zamo gunki,

A kan ta a d’ora yin raki,

Na kare martaabarta.

 

  1. Saboda a nan ake sata,


A tara kud’i a k’asaita,

A jefa k’asa ga ragaita,

Talauci duk shi dame ta,

Ta nakkasa gun mak’wabta.

 

  1. A sa marashi da mai samu,


Suna kwana cikin gammu,

Matasa har da mai gemu,

Su takura ba wurin kamu,

K’asa duka an fusata.

 

  1. Matasa an ka cuce su,


Ga ilmi an ka k’ware su,

Ga aiki babu mai ba su,

Siyasa taf farauto su,

A dole su je kiran ta.

 

  1. Da nan aka sa su ‘yab banga,


A ba su giya su sha daga,

Su gigice da damaga,

Fasadi ga shi an shirga,

K’asa sama har k’asanta.

 

  1. Ganin an rena k’urarmu,


A banzantar da wayonmu,

A ta da fad’a k’asashenmu,

Saboda a karya k’arfinmu,

Da ganganci da cuta.

 

  1. A ofis an ci k’arfinmu,


Siyasa an galale mu,

Yawan jama’a a cuce mu,

Muk’amai an ka kore mum,

Kujerin an ka k’wata.

 

  1. Muna kallo mu zan le’bo,


Tufanmu kad’ai ka yin ra’bo,

A kwashe zuma mu d’au so’bo,

Da an gamu sai a ce, Ja’b’bo,

Ina Mudi da Auta?

 

 

 

 

 

  1. A nai muna izgilin raini,


Ganin an samu zamani,

Siyasa mai bak’in muni,

Da mai gemu da mai huni,

A tabbata an talauta.

 

  1. A yau mabiya ga alk’ibla,


Musulmi masu yin salla,

Ake ta yi wa kisan gilla,

Saboda muna fad’in Allah,

Ka tsari mai nagarta.

 

  1. Siyasa ce gidan tasku,


Zaman ciki babu dottaku,

Da mai rawani da mai diku,

Kwad’ai ya rufe k’wak’walwarku,

Ku zan manyan macuta.

 

  1. Ku jefa k’asa a Basasa,


Tsaro ya zamo barafasa,

Ta’addanci ya bunk’asa,

Dukan tsarinta an rusa,

Musiba ta rufe ta.

 

  1. Haba jama’a mu hankalta,


K’asa ta k’are muzanta,

Zaman tuni an ga wallenta,

Mutane sun galabaita,

Suna ta shirin barin ta.

 

  1. Ku dubi irin halin maiki,


Da yag gamu shi da gauraki,

Wurin tad’i da hankaki,

Gaban jimina yana raki,

Sanin ya ‘barka cuta.

 

  1. Biri in yai kuren reshe,


Dabaru nasa sun rushe,

Irin tsololuwar baushe,

Da ya fad’o yana mushe,

Su angulu za su zabta.

 

  1. Musulmi wanda yad dace,


Shahada langa’bunai ce,

Ya sha romo ya d’au kwalce,

Da likkafaninsa zai zarce,

Cikin murnan zuwan ta.

 

  1. Kisa bai k’are Imani,


Zaman rai na da zamani,

Akwai shi a kowane k’arni,

Da shi aka maganin raini,

Shiga Aljanna kyauta.

 

  1. Ganin mu za a rinjaya,


Ake yin martanin gayya,

Na k’one yara har manya,

Da rodubulo a kan hanya,

A firgita masu bin ta.

 

 

 

 

 

  1. A turbud’e bom k’asashenmu,


Ya karkashe ‘yan uwan namu,

A bi mu ana ta kamo mum,

Da hujjoji na zarginmu,

Da an ka shira na cuta.

 

  1. Mutum da gidansa an bi shi,


Ya yunk’urto a harbe shi,

Ya mik’a wuya a d’aure shi,

A runtuma gun iyalanshi,

Da yin fyad’e da ‘bata.

 

  1. Gabanka a harbe tsohonka,


Walau a kashe iyalanka,

A sa ‘ya’yanka yin shirka,

A sa ka rutsi na cin fuska,

Da tun tuni an hukunta.

 

  1. Muna ji Borno ta watse,


Gaba d’aya Yobe ta motse,

Na Bauchi gabansu ya katse,

K’asar Adamawa ta gintse,

Filato an kashe ta.

 

  1. Kano ta sha harin girshi,


Kaduna karen ka wa habshi,

Jahar Nasarawa sai nishi,

Abuja kwatsam yake tashi,

A kama gudu a kwalta.

 

  1. Gusau a wajen manomanta,


Kaza sashen makyayanta,

Bala’in ya malale ta,

Rahotannin musibunta,

Abin sai an tak’aita.

 

  1. K’asar Katsinanmu an yi hari,


Da gawakki gudan tari,

Abin ya kasance labari,

Hukuma ba ta inkari,

Da tunkarar macuta.

 

  1. A Sakkwato an yi mai muni,


Awon ya furce mizani,

Zuma sun harbi mai gani,

Kare ya shuri k’ur’ani,

Ruwa su kashe masunta.

 

  1. Ina kuka zacci zai tsere?


K’asa can da tana kore,

Hamada ta bi ta share,

Ina wani wanda zai more,

Zama ya ci gajiyarta?

 

  1. Mak’ark’ashiya shirin manyan,


A tunkud’a yara jayayya,

Da son a ga masu rinjaya,

A ba kowa makamayya,

Su karkashe kai da wauta.

 

 

 

 

 

  1. Tammat kun ji k’arshen ta,


Mak’ark’ashiya ga sunanta,

Alu d’an Bunza yay yi ta,

Masar aka nome k’wazonta,

Kano aka kai tuk’inta.

 

https://www.amsoshi.com/contact-us/

Post a Comment

0 Comments