Ticker

6/recent/ticker-posts

Ganin Ido Nassi Ne Da Babu Ƙila-Wa-Ƙala


Waƙar ƙwar biyar ce, babban amsa amonta “wa” yawan baitocinta saba’in da ɗiya (71). An kammala ta ranar Larba 8/01/2014 a kan hanya tsakanin Katsina zuwa Sakkwato. Burinta kakkaɓe ƙura ga ‘yan kurakuran da suka gabata na rikicin ganin watan Ramala na shekarun 2012, 2013 da 2014. A shari’armu, yaƙinin ganin wata ya kore kowane irin tawili. Ana dogara da yaƙinin gani a kawar da maganar kowa, komai nauyinsa a sikelin zamaninsa. Idan ganin ido ƙuru-ƙuru ya tabbata zancen kalanda da kwamfuta da hisabi ba su da gurbin zama in ji Manzon Allah (SAW). Ƙaryata yaƙini domin sauraren umurnin wani ko wasu cin dugadugan Manzon Allah (SAW) ne. Fatawa da tawili da ƙiyasi da duba zuwa ga al’adar ƙasa/jama’a na siyasar shugabancinta duk ganin yaƙini ya haramtar da su. Dogara ga ganin ƙasa mai tsarki ko kirdadon ibadojin da ake gudanarwa ciki na tsayuwar Arfa da yanka ba ya da madogara ga littafin Allah da Hadisan ManzonSa (SAW). Kawar da kai ga yaƙinin ganin wata a kan kowane irin dalili saki zari kama tozo ne. Annabi (SAW) bai ɓoye komai a saƙon manzancinsa ba. Da wane dalili za ka bar umurninsa ka bi sabaninsa?
 -------------------------------------
-------------------------------------
1.       Na kiri sarkin da shi kaɗai aka wa bauta,
          Na yi salati ya zamto tsanin adu’ata,
Duk ahalil baiti ban rage ba ga tsarinta,
Na sa ashabu ko guda kar ka musanta,
          Haskensu ya barkace duhun da ka cutarwa.

2.       Allah Ya yo samai ƙasai bisa tsarinSa,
Yai rana Yai wata nujumu a gefensa,
Yaƙ ƙago gizagizai suna shawaginsa,
Duk faɗin duniyarmu can ga hukuncinSa,
          Ɗawafi taka yi da mu tutut babu tsayawa.

3.       Aikin rana ta rarrabe kwanukkanmu,
Don ga ibada mu rarrabe lokuttanmu,
Taurari an ka yo ƙawa ga sama’unmu,
Sannan aka yo wata ya zan jagoranmu,
          Kwanakkin shekaranmu nan muka ganewa.

4.       Rana kwana guda rawanta ka ƙarewa,
Taurari ko cikin dare suka haskawa,
Hasken rana gizagizai ke karyawa,
In sun ishe jinjirin wata sai makewa,
          Nan aka rigima ga lisafin tantancewa.

5.       Sunan farkon wata Hilalu ga littafai,
Wato ɗan jinjiri ga farkon dubi nai,
In ya yi rabi ga kwanakinsa na ƙirganai,
Nan sunanai Badar ga hasken zatinai,
          Dan nan ya zamo Ƙamar Shahar gun ƙirgawa.

6.       Kuwwar da ake ga jinjiri don murnar sa,
Ga baki hangahan ido na dubin sa,
Mata taɓi da yara na ta rawa gun sa,
Shi ne aslain Hilalu can gun hilarsa,
          An shiga sabon wata da fatar morewa.

7.       Kwana ashirin da goma su ne ƙolinsa,
In yai ashirin da ukku sau ukku ƙidanSa,
Ya cika sunna sahihiya ba a musunSa,
Nace bisa lisafi ga farkon dubin sa,
Kowane adadi ka kai garai babu musawa.

8.       In ka ga ya hau ka sake duba hisabinka,
In ya kasa ka ƙara bin lisafinka,
Gano adadi ka bar kula da kalandarka,
Manta da bugun ƙasa da ‘yar kwamfutarka,
Annabi (SAW) ne yai hani da furucin ƙyaccewa.

9.       Nassi ya ce, ganin ido shi ne zance,
Duk wani ba shi ba anka hau an ragaice,
Kway yi ibada da shi ku ce, ta lalace,
Ya shiga saki zari dole ko zai dabirce,
Ya sake asali ya kama reshen rushewa.

10.     In an ga wata farin gani walkan ke nan,
Duk wasu ‘yan kame-kame an daina dan nan,
Ba sauran jinkirin ibada das san nan,
Hujja ce yanke dakata nan shi ke nan,
Duk wani uzuri gare ka nan za shi tuƙewa.

11.     Shaida ga tsayinsa adili ɗaya hujja ne,
Yardadde kamili abin so ga mutane,
Mai imani da gaskiya da aƙida ne,
In ya ce, ya gani ga nassi hujja ne,
Sarki ya sanar da muminai ga hukuntarwa.
12.     In su biyu sun ka zo ga sarki shaidarwa,
Babu sananne cikinsu kan tantancewa,
Ko adalcinsu ya buwaya ga ganewa,
Nassi ya ce Amiru na jinkintarwa,
Har wani shaidu ya samu don daidaitawa.

13.     Tantance adili yana can ga sarakai,
Haƙƙinsu su tanado na sunna malammai,
Masu riƙon gaskiya na Allah adillai,
Domin su yi bincike na rarrabe adillai,
Kowace matsala ya zan suna gaba ga kulawa.

14.     Ba a musun adili ga shaidun shaidarwa,
Tabbata zancensa wajibi ne kamawa,
Ba hurumin dakata wa sarki ga sanarwa,
Ɗa’a sarki ka yi a nan ba ya musawa,
Shi zai jagora nan ga ɗauka da ajewa.

15.     Ɗan bidi’a, fasiƙi da Kotiyo shashasha,
Shaidunsu ana gudun sa don aikin assha!
Don an ƙi batunsu don suna aikata assha!
Ba su da ikon su sha ruwa su yi mashasha,
Kamun bakinsu dole ne babu ragawa.

16.     Wanda ya kai kansa fada domin ya yi shaidu,
Ko aka tura shi don ya je tabbata shaidu,
Sarki a tufakkurinsa yas soke shaidu,
Ta tabbata nana sai biɗan sabon shaidu,
Shaidan bai izgili ya sha ko farawa.

17.     Wanda ya shaide shi adili bisa ilminsa,
Yaj ji bayaninsa fada gun iƙirarinsa,
Ɗaukar azumi yakai a nan ga hukuncinsa,
Ilmin sarki daban saninsa daban gun sa,
Inkarin fada bai hana masa ɗaukawa.

18.     Soke shaida ga mai hukunci a kiyaye,
Rubba yakan zo rashin sanin abu kai waye,
Ko ko siyasa walau adawa ta iyaye,
Mai dahuwa shi da masu banda da ‘yan soye,
Sirrin raɗaɗin wuta gashi suka iskewa.

19.     Muddin ka gan shi ka kiyaye da wata ne,
Ko kai ɗai kag gane shi taro na mutane,
Hujja ta hau ka babu zancen kai wane?
Lura yaƙinin gani a komai haujja ne,
Ba wata hujjar da ke gabansa ga shaidarwa.

20.     Sai nassin Mustafiida  taro na mutane,
Masu yawa ko’ina a birni zazzaune,
Sun ka yi kuwwar hilalu hannu na nune,
Ko labari a ko’ina yab bi birane,
Ba zancen bincike a nan sai ɗaukawa.

21.     Ko da a cikinsu adilai ga fasiƙƙai,
Ga malammai ƙalilatan ga jahillai,
Ko cunkoson da ba a rarrabe halinai,
Ba a buƙatar a kai su zauren hakimmai,
Tanyonsu ciri a kai ga ɗauka da ajewa.

22.     Zancen adadi na Mustafida  a kula shi,
In sun kai ukku sun wadata a nassinshi,
Dan nan kuma hat tawaatiri ga hukuncinshi,
Ba hujjan shan ruwa da an ji jawabinshi,
An shiga Ramadhaana babu zancen kutsawa.

23.     In gumma alaikumu  in irin haka ta auku,
Ƙauyenku gizagizai su mamaye sashenku,
Ba sarari ko’ina sama’u a lungunku,
Nassi ya ce ku ƙaddara ga ƙidayanku,
Don tabbata gaskiya ta ɗauka da ajewa.

24.     Nassin ingumma  can wurin tawilinsa,
An yi umurni da faƙdarun  bisa nassinsa,
Nan masana sun ka ce ana kirdadonsa,
In babban girgije ya make gefensa,
Ƙaddartawa akai tsayinsa ga ƙirgawa.

25.     Wansu mazaje ganinsu ba haka nan ne ba,
Sun ce masana fagen hisabi su yi kwamba,
Sai sun rabe kainuwa da kifi bisa ɗamba,
Sun ce a bi lisafinsu ba saɓo ne ba,
Muddin an kasa ittifaƙin ganowa.

26.     Manyan mutaƙaddimina sun soke batun nan,
An ga hadisin hanin hisabi ga batun nan,
Zancen faƙdar lahu ga kulkin nassin nan
Mujmal  sunansa can Ussulu  a fannin nan,
Kurman nassi fashinsa nassi aka sa wa.

27.     Manzo ya ce ku ƙaddara ya yi talatin,
Wato ku cike ƙida ku kuble shi talatin,
Shi ne nassi mufassirun  dakanta min,
Ya soke turaddudun  da ƙaulaani  ɗaɗa min,
Babu khilaafun gare ta, ba ta da ruɗarwa.

28.     Zancen a bi shugaba ku gane bayaninsa,
Wato babban Amiru koko waƙlinsa,
Alƙali ne gare ku ko mufti kansa,
In an rikice ga lisafi aka zo kansa,
Ƙaulin da ya tabbatas garai aka komawa.

29.     Hatta da ganin mutum guda in ya yarda,
Ɗa’a aka yi garai a mai da ruwa randa,
Sunnarsa ya ta da kat-ta-kwana da ‘yan sanda,
Ƙauye da birni a kai sanarwa da takarda,
Ta tabbata ba musu ga ɗauka da ajewa.

30.     In sarki ɗai ya gan shi ba shaidu gunsa,
Kamun bakinsa dole ne ga hukuncinsa,
Su ko jama’ar gari su bar shi da aikinsa,
Ba ya da nassin matsa wa ko da bawansa,
Nassi ne yanke Ummahaatu  ka nunawa.

31.     Sarki ya samu binciken shaidun baƙo,
          Ko majahuli da yat taho bayyana saƙo,
Koko Ibinis sabili mai rataya ƙoƙo,
Tsoho mai hurhurar gira zo dudduƙo,
          Sarki na bincikarku don tantancewa.

32.     Shaidu ba rantsuwa yake ga bayani ba,
Ba zana mai wata akai ya yi sharhi ba,
Ba kwanakkin wata ake son ya faɗi ba,
Ba mintocin ganin wata za ya faɗi ba,
          Ba mu da nassin ƙididdigar ga ta ƙuƙewa.

33.     Nassi bai ƙayyade wa shaidu lotto ba,
Ko bayan azzahar ya zo bai latti ba,
Kanun baki akai da ranko Ɗanbaba,
Ga abu sahalan a mai da shi babbar gaba,
          An rarraba kawunanmu mun kasa haɗewa.

34.     Ba wata falala ga mai ganinsa a nassance,
Manzo dai bai ganai ba mun gan shi rubuce,
Labari an ka ba shi yak kuwa tantance,
Yay yi umurni a kama baki a azunce,
Sunna sauƙi gare ta ba ta da kushewa.

35.     Ku ‘yan sai mun gani ku gyara fahintarku,
Hujjarku guda ku ce kuna da ƙidayanku,
In makuwa tas shigo shi wa zai fid da ku?
Wacce ko an gani ku kama ƙidayanku?
          Don Allah ‘yan’uwa mu zan sassautawa.

36.     Kai ko mai dargaza tsaya ji bayanina,
Uttazu gaya wa ƙungiyarku ta bar ɓanna,
Soke ganin adili gare mu bala’i na,
Kore ganin mustafiida jawo fitina na,
An yi fito-na-fito da Manzon shiryawa.

37.     Don sarki bai gani ba ba a musun shaidu,
Ga Manzo bai gani ba yaƙ ƙarfafa shaidu,
To wace hujja gare ka kan ƙaryata shaidu?
Kun hana sarki ya ji shi don ƙulla makidu,
Hurmin Ramadhaana kun ka kai mu ga ketawa.

38.     Nassi bai yarda an gani a ƙi ɗauka ba,
Bai ce sarki ka ba da iznin ɗauka ba,
Bai ba wata ƙungiya kafa ga hukunci ba,
Suumuu yac ce wa afɗiruu  malam babba,
Muddin an gan shi an gama ba fasawa.

39.     Ga wata hikimar rashin sani can ga Nataro,
Wai mu haɗe kanmu don mu ba maƙiya tsoro,
Ɗaukarmu a tare, gun ajewa mu bi taro,
Ba a ƙiyasi wurin da nassi yai tooro,
Balle fatawa ta shisshigin ƙin ƙarawa.

40.     Ban ga haɗin kai ga goge nassin sunna ba,
Ba wata hikima na karkacewa shari’a ba,
Ban ga karatu ga wanda yaƙ ƙi Hadisi ba,
Ni ban ga barazana ga taron zunubi ba,
Son rai yat tarwatsa mu mun kasa kulawa.

41.     Ɗan taron ƙungiyarmu ko na ɗariƙarmu,
Bai ijma’in da za shi kore farillarmu,
Mun shaidi ganin wata da yara da manyanmu,
Sarkinmu ya tabbatar ya yarda da ƙaulinmu,
Hujja ce babba shan ruwanmu da ɗaukawa.

42.     Mai ce wa ba a shan ruwa ba a ajewa,
Ba mu hadisin da kag gani mai gansarwa,
Wanda ya kore ganin yaƙini korewa,
Yac ce Lamiɗo na da hujjar sokewa,
Ko da an gan shi ba a ɗauke da ajewa.

43.     Mai fatawar ƙaryatar da taro hanyanka,
Ɗan guntun bincikenka ne ke ruɗa ka,
Shaiɗan ya yaudare ka ya ci amanarka,
Ya kai ka faɗa da gardama da Nabiyunka,
Ka bi hadisai kana ta faman sokewa.

44.     Masu ganin babu adili sai jama’arsu,
Sai wani ɗan ƙungiyarsu ko na ɗariƙarsu,
Ko wani ɗan mazhabarsu mai bin son ransu,
Wanda ya ce babu mumini sai danginsu,
Ya rufe ƙofar zama da shi tattaunawa.

45.     An ga wata lokacin Umar bisa mulkinai,
Bayan an sha ruwa bayani yas mai,
An ka gabatar da masu shaidu fadatai,
Bai ƙaryata kowane ba can ga hukuncinai,
Ko mun fi Umar riƙo ga sunna da kulawa.

46.     Baba Hadisin Kuraibu babbar hujja ce,
Muddin an gan shi lisafi ya lalace,
Shi aka aiki da shi a bar sauran zance,
An kai ƙarshe, ganin yaƙini ne dace,
Modibbo da Maigari su huta da sanarwa.

47.     Babbar hujja ganin yaƙini na mutane,
Ko ƙittawan gira ya ɓoye gun nune,
Muddin an gan shi ba batun sake tunane,
Muminnan ƙauye haa kazaa har na birane,
An hujjance su ba kalami na daɗawa.

48.     In farali yac cika walau ya zo ba ɗai,
Muddin an gan shi lisafi ya zo bai ɗai,
Ya zama raba gardama a miƙa wuya bai ɗai,
Wanda ya ce ba a yi shi kawo hadisinai,
Wanda ya soke ganin yaƙini sokewa.

49.     In an ga wata ganin yaƙini na idanu,
Ya zama hujja ga ‘yan Adam har aljannu,
Masu walankeluwa da nassi ku bi sannu,
Ƙarya furta ta dole ne runtse idanu,
Bil’amu yau ko yana da rai wa ka kulawa?

50.     Kore yaƙini ga malami ya zan hauka,
Sake karatun sani ka kyautata nahawunka,
Don ka ga ana zuwa wurin tafsirinka,
‘Yan banga na kururuwa ga bayaninka,
Sai ka ga ka furce malamai duka ganewa.

51.     Don ka yi zama Masar da Sudan ga karatu,
An kai ka Madina don shahada ta rubutu,
Wai kai a ganinka ka yi manyan makarantu,
Ko wai zance ka ce ina yay yi karatu?
An koma cin ido da sunan koyarwa.

52.     Mu a sama’un garinmu Bunza Madinanmu,
Nan Misirar Bunza ɗaukacin Sudaninmu,
Nan mun ka ganai ƙuru-ƙuru a sama’unmu,
Mun ka yi ɗa’a ga annabinmu abin son mu,
Mun ga yaƙini ƙiri-ƙiri ba mu sakewa.

53.     In an ga wata haƙiƙatan an shaida shi,
Duk wani zance na Mazhaba sai a aje shi,
Babu ɗariƙar da za ta soke hukuncin shi,
Balle wata ƙungiya ta ce ta kore shi,
In dai Allah ake nufi bisa shiryarwa.

54.     A banzanta ganin ido a bi shi a rafashe,
A ture batun adilai a rungumi ‘yan tashe,
A barkata nassi da falsafa ai ta hasashe,
A ɗau komfuta a bar hadisai tattarshe,
          A ƙago kalandar ganin wata ai ta bugawa.

55.     A sa ƙattan kafirai cikin addininmu,
          Da ƙwarorin jahilanmu don a ci irlinmu,
Da malaman fada karnukan zamaninmu,
A ba su na ƙosai su firgita mu su watse mu,
          A ci muna fuska ƙiri-ƙiri babu ragawa.

56.     Ganin Makka daban ganin ƙasarmu daban ne shi,
Kaman nisan Andolas Khurastani zubin shi,
Ga nassi kowanmu zai tsaya ga ganin kanshi,
Bayanin da Kuraibu yay yi in mun gane shi,
          Ba za mu yi ɗa’a ga masu ƙaga kalanda ba.

57.     Muna nan rana kataa, a Makka ishaa’i ce,
          Da sallarmu da shan ruwanmu in ka tantance,
Akwai saɓani na lokaci a haƙiƙance,
A ce mu haɗe duk mu zan guda an dabirce,
          A mai da gabas yamma babu nassi na riƙawa.

58.     Katafashen ɗalibi akwai shi da ban tausai,
          Burakallin malami takaici ka kashi nai,
Sakakken mabiyi da hankali za a kira nai,
Zuma in yai gardama wuta aka ruga mai,
          Hayaƙi shi yi turnuƙu a huta da laɓewa.

59.     Da kai nike Rikitazu shugaban masu zaƙewa,
Na cin irlin muminai da kai su ga kokawa,
Bala’in ya kai ga limamai wa ka tsayawa?
A tarwatsa mamu da ladanai babu kulawa,
          A kan maagin cefane da naira ta kashewa.

60.     Bala’in ga da kun ka ɓangalo rusheshe ne,
Jidalin da ya takaro gudan tiƙeƙe ne,
Fasadin da ya faru wa mutum! Jibgege ne,
Ta’adin da ya yunƙuro gudan makeke ne,
          Saboda tuwon alkama a kai mu ga kokawa.

61.     Da cin zarafin muminai da ɓata aƙidarsu,
          A tozartasshe su haa ka zaa cin fuskarsu,
A ko wofintar da su da cin zuƙuƙunsu,
Da safe da maraice ƙunniya cin namansu,
          Saboda yaƙinin ganin wata babu musawa.

62.     Idan sarki bai ga ni ba bai ji bayani ba,
Da yai cigiya har shigan dare ba a dace ba,
Ba zai zama hujja ta ƙulle ƙofar shaida ba,
Haƙiƙan yanayin ƙasa guda ba ɗai ne ba,
          Fa ba makawa dole jinkirin saurarawa.

63.     Shaidu ko da da rana yaz zo da bayani,
          Sunna ta ce a dole ne ba shi sukuni,
In an ka ji gaskiya ana sake tunani,
Ba a damo gungurum na manyan dodanni,
          Ga addini ba a soka son rai da suƙewa.

64.     A sa addini zama siyasar saɓi-zarce,
Da Pidipi ta shigo shi duk ya lalace,
Da fadanci ya rufe shi duk an dabirce,
Da an tsoma kwaɗai cikinsa duk an sagarce,
Ana haɗa mabiya faɗa buƙatar holewa.

65.     Salon sa sarki cikin batun ga akwai zamba,
Fa ba don an so shi an ka sa shi ga aikin ba,
Ga masalatai muna ta yi bai shaida ba,
Yau mun ga wutar gashinmu tun ba mu shirya ba,
Mun dudduƙo mu samu hanyar tserewa!

66.     Mu ka kiran duniya ta kawo hujjarta,
Da nassin aya walau hadisi a kwatanta,
Su koma ‘yan baya gaskiya sun ture ta,
Don kwaɗayin duniya su mara wa macuta,
Ana ta kashin ‘yan uwansu ba mai cetarwa.
 
67.     Uttazu kiro muƙaddami bari suka tai,
Haba ɗan gargajiya tsaya bari suruttai,
Da Modibbo na unguwa a soro malammai,
Fa Shaiɗan ya ci mu ya kamata mu bore mai,
Dole haɗin kanmu lokaci na ta wucewa.

68.     Masu ɗariƙa da ‘yan Izala hayyanku,
Ga maƙiya can suna hararar lunguku,
Kun zama kifi kuna ta cin kanku da kanku,
Kun zama BOKO HARAM ga masu ƙiyayyarku,
Safe da maraice sai kashi sai ɗaurewa.

69.     Wai kai kurinka tun da ka bi ɗarikarka,
Kai ka doronka ƙungiyarka ka ruɗa ka,
Ko tinƙaho da mazhaba ga aƙidarka,
Ga maƙiya sun yi ƙungiya sun sha toka,
Ku da ƙasashenku sai kisa sai korewa.

70.     Hadda siyasar ga makira an ɗebe ku,
Duk wani aikin tsaron ƙasa an fid da ku,
Kun zama almajirai ga baital malinku,
An gayyato duniya a taru a watse ku,
Kun kasa tufakkarin dubaru na riƙawa.

71.     Allah cece mu kuk ka dubi dabararmu,
Mun san in don halinmu sai mun ci bonenmu,
Ali Muhamman na Bunza ne mai waƙarmu,
Jikan Inta Imamu mai auren Danmu,
Dogo angon Gadaje manyan koyarwa.
 
                   Aliyu M. Bunza
                Umaru Musa ‘Yar’Adua University,
Katsina
8/01/2014 Larba
Daga Katsina zuwa Sakkwato

Post a Comment

0 Comments