Ticker

6/recent/ticker-posts

Na Tunkari Tsautsayi Da Shirin Yaƙi (Amma Tawakkali Ta Faɗakar Ni)


Waƙar jaje ga Dr. Yakubu Aliyu Gobir game da hatsarin mota da ya yi ranar Laraba, 10 ga watan Janairu, 2018

1.      Na yi shirin adda da wuƙaƙe,
Na ɗau gariyo hannuna.
2.      Na ɗau sandata da kulake,
Na saɓa takkwabi gefena,

3.      Na ɗau mashina da na gada,
Tsitaka na nan hannuna.

4.      Barandamina na wasa shi,
Na ɗau kibbau a kwarina.

5.      Majaujawa na ɗau wannan,
Text Box: www.amsoshi.comAl’amuda na sanya gefena.

6.      Na ɗau baka na riƙe zarto,
Gatari na nan hannuna.

7.      Na sha ɗamarar kayan sulke,
Babbar garkuwa ke hannuna.

8.      Na yo huci, zumbur zabura,
Na bar Sakkwato dangina.

9.      In na yi taku sai an girgiza,
Za ka ga ramin sawu na.

10.  In na hau dutse sai ya dangaza,
Za ka ga garin bayana.

11.  In na bi daji sai ya bushe,
Za ka ga tsirrai sun ƙuna.

12.  Idan na bi kogi sai ya tsotse,
Tsabar zafin ƙalbina.

13.  Idan na ga tsuntsu sai ya faɗo,
Don hucin numfashina.

14.  Yau dai ko ni ko ita,
Ta taɓa gefen rayina.

15.  Ba mai ba ni baki in tsaya,
Ana tsoron zafin raina.


16.  Ina tafiya sai na yi birki,
Abin mamaki a gabana.

17.  Tsohuwa da rufi na gani,
Ta tare hanya wurin bi na.

18.  Na ɗano kibiya na taɓe baka,
Na saita ta da mashin hannuna.

19.  Na zaro takobina ɗin nan,
Na ɗaga sandar dukana.

20.  Text Box: www.amsoshi.comKan na ɗau sauran kaya,
Kalamanta sukash shiga kunnena.

21.  “Idan ka kar ni gidan duniya,
Lahira tabbas ka ƙuna!

22.  Ni sunana ikilasi,
Tawakkali kuwa laƙabina.

23.  Kana da buƙatar taimako,
Ka bi ni ka ji su kalamaina.

24.  Ka yi shirin yaƙi na gani,
Bai taimakonka tunanina.

25.  Tsautsayi da kake nema,
Tai tafiyarta wurin kwana.

26.  Sannan jakadar Allah ce,
Ba ta da laifi ɗan ɗana.

27.  Tsautsayi da kake kallo,
Ba ta dare sai dai rana.

28.  Domin idan ta ziyarce ka,
Ga kai Allah na ƙauna.

29.  Ka san tana rikiɗar siffa,
Fara ko baƙa mummuna.”

30.  Na zare ido na shiga thinking,
Don su biyu ne a tunanina.


31.  Muguwa mai baƙin kaya,
Ita ats tsautsayi guna.

32.  Mai zuwa da farin kaya,
Nasara sunanta tunanina.

33.  Ikilasi sai ta yi ɗan tari,
Ta katse dukka tunanina.

34.  “Mace ɗaya ce ba biyu ba,
Takan sauya ne ɗan ɗana.

35.  In dai gajarce ma zance,
Ɗiya ce ‘ya ta cikina.

36.  A har kullum in ta zo ta,
Text Box: www.amsoshi.comBurinta ana tuna sunana.

37.  Idan ma an manta iklas,
Tawakkali duk ɗai na.

38.  Idan ta zo da farin kaya,
An fi yin tunanina.

39.  Idan ta sanya baƙin kaya,
Akan ma manta sunana.

40.  Ga shi kamar kai a yanzu,
Feɗes! Ka manta zancena.”

41.  Na yo ‘yar ajiyar zuci,
Kalaman sun tafa ƙalbina.

42.  Na mai da kibau cikin kwari,
Na sauƙe kayan yaƙina.

43.  Ta yi murmushi ta matso kusa,
Ta yo furucin ƙarshe guna:

44.  “Duk wani mai so ya tsira,
Ya bibiyi dukka kalamaina.

45.  Ya je makaranta biɗar saura,
Malam ya san zancena.


46.  Manta ni baƙin jahilci ne,
Dole ake tuna sunana.

47.  Ƙaryata ni ko kafirci ne,
Dole a yarda da zancena.

48.  Ziyarar ‘yata tilas ne,
Kasance cikin ko-ta-kwana.

49.  Ba shirin yin yaƙi ba,
Shirin tunanin sunana.

50.  Ni ko zan zo a gareka,
In shiga cikin zuci in zauna.

51.  In sanyaya maka tunani,
In sa ka ji rai ya bar ƙuna.”

52.  Tana faɗin haka sai ta ɓace,
Ɓat! Ba ta a gabana.

53.  Na yi lankwat na yo kasaƙe,
Kalaman sun shiga rayina.

54.  Ashe lallai na yo wauta,
Na so fita addinina.

55.  Dalilin ma kenan da ya sa,
Text Box: www.amsoshi.comNa manta gishiri girkina.

56.  Na fara baiti tor-tor-tor,
Ba godiyan mahaliccina.

57.  Na fara waƙa sar-sar-sar,
Ba salatin mazona.

58.  Yafe Allah na tuba,
Sallu alaihi manzona.

59.  Daɗo tsira da amincinka,
Gare shi macecin rayina.

60.  Saka da iyalai da sahabbai,
Da masu bin sa da ƙauna.


61.  Na yi addu’a ya Allah,
Ƙara lafiya da tsawon kwana.

62.  Ga malam tare da imani,
A. Y. Gobir limamina.

63.  Ƙara masa arziki da buɗi,
Da juriyar addinina.

64.  Shiryar da zuriya tasa,
Su zam mariƙa addinina.

65.  Da mu da shi da iyalanmu,
Ka sa ranar ƙarshen kwana-

66.  Furucin ƙarshe daga bakinmu,
Shahada ce mai hana ƙuna.

67.  Text Box: www.amsoshi.comAmin Allahu ka amsa,
Ba don mu ba maƙagina.

68.  To a nan zan ja birki,
Na tattare duk ‘yan kayana.

69.  Abu-Ubaida ɗa ga Sani,
Ga matambayin sunana.

70.  Yawan baitukanta saba’in ne.
Mi ta nazari dangina.

Post a Comment

3 Comments

Post your comment or ask a question.