Ticker

6/recent/ticker-posts

Wakar Kudi Ta Nasiru G. Ahmad

1. Rabbi ban iko na tsara,

    Baituka kar nai gazawa.


2. Yau batu zan kan "Nuƙudu" 

    Ko ko "Money" ba sakewa.


 3.Mallakar su tana da daɗi,

    Duniya ba mai musawa.


4. Laƙani na farin jini ne,

    Ba ƙiyayya sai biyewa.


  5.Maganin huce takaici,

     Duniyar ga kana sakewa.


6. Duk batunka abin yabo ne,

    Aibukanka suna ɓacewa.


7. Kai da Sarki har su Gwamna,

    Sai abota ba rabewa.


8. Dukka faɗin duniyar nan,

    Za ka je lale anai wa.


9. Dukka yare za ka ji shI,

    Don ko Naira ta iyawa.


10. A gida ba babba sai kai,

      Duk batunka ba a ƙiyawa.


11. 'Yan uwa su taho gare ka,

       Lamarinka suna yabawa.


12. Fa'idojin ba su ƙirgo,

      In da "Money" ka hayewa!


13. Aibuka zan bayyana su,

       Don dukanmu mu zam kulawa.


14. Kar ka manta akwai hisabi,

       Kan abin da ka mallakawa.


15. Shin ta yaya kab biɗe su?

      Haka yadda ka zan kashewa.


16. In ka tara sai ka koma,

       Fargabar su zamo ɓacewa,


17. Ga ɓarayi na fakon ka,

       Ko ina ka yi ba sakewa.


  18. Hankalinka yana gare su,

        Ko da yaushe kana tunawa.


19. "Ga kuɗina can ga wane,

       Gobe haja za ta zowa."


20. To ina nutsuwar ibada,

       Gun Tabaraka mai iyawa?


21. Ƙoƙarin tsare dukiya na,

      Sa ralala ai biyewa.


22. Sai ka ga an kai ga tsafi,

      Sihiri an rungumewa.


23. Har a kai shirka da Allah,

      Dukiya don ai tsarewa.


24. Son da kowa ke gare ka,

       Ka sani ƙarya sukewa.


25. Don a samu abin riƙa ne,

      In fa babu suna bajewa.


26. In ka so ka farar dabara,

       Hidimar dini ka yowa.


27. In halal ce dukiyarka,

      Rabbi zai karɓa yabawa.


28. Ba a ba Allah haramun,

      "Ɗayyibun" yake bai riƙawa. 


29. Don haka mu biɗi halali,

      Don haram ba ta daɗewa.


30. Dukiya ta halali za ai

      Wa hisabi ran tsayawa.


 31. In haram ce sai uƙuba,

       Ga Jahannama ke direwa.


 32. Ɗan uwa gode wa Allah,

       Lafiya da yake ta baiwa.


 33. Sana’arka riƙe da kyawu,

       Ƙwadagonka zamo kulawa.


 34. Kar ka raina abin riƙawa,

       Na halal shi ke daɗewa.


35. Zam ƙana'a kar ka damu,

       In asiri yai rufewa.


36. Nemi albarkar Ilahu,

      Godiya ka yi zai daɗawa.


37. Ko da yaushe mu roƙi Allah,

       Mu yi kyan ƙarshe gamawa.


38. ‘Yan uwa da ka jarrabe su,

      Dukiyarsu ta yi yalwa.


39. Rabbi sa su bisa tafarki,

      Mustaƙim ba kangarewa.


40. Ba su ikon taimakawa,

      Da halal mai tsarkakewa.


41. Mu talakkawa ka ba mu,

      Hakuri da kaɗan mu yowa.


42. Zan tsaya haka ‘yan uwana,

      Baitukan nai kammalawa.


43. Nasiru G. Ahmadu ne,

      Ya yi waƙar don tunarwa.


 Alhamdu lillahi.

      28 / 4 / 2014

Post a Comment

0 Comments