
NA
DAYI RILWANU
TABBATARWA
Mun tabbatar da cewa wannan aiki ya cika sharud’d’an da jami’a ta shimfid’a wanda ake buk’atar duk d’alibin da ya kai shekarar karatu ta k’arshe, da ya rubuta kundin bincike domin ba da gudummuwa ga masu buk’atar nazari a Sashen da ya gudanar da karatu.
____________________ __________________
Sa Hannun Mai Dubawa Kwanan wata
Mal. Sama’ila Umar
____________________ _________________
Sa Hannun Shugaban Sashe Kwanan wata
Prof. Atiku Ahmad Dunfawa
___________________ _____________
Sa Hannun Mai Dubawa Na Waje Kwanan wata
______
SADAUKARWA
Na sadaukar da wannan aiki nawa ga iyayena da kuma ‘Yan’uwana. Da fatar Allah Ubangiji Sarki Ya saka musu da mafificin alherinSa Ya albarkaci rayuwarsu Ya kuma nufe su da cikawa da imani amin.
GODIYA
Dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah mak’agin halitta, kuma fiyayyen masani wanda ya sanar da d’an Adam abin da bai sani ba, ya kuma umurce shi da neman ilimi da yad’a shi. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah Annabi Muhammadu (S.A.W.) fiyayyen halittu wanda ya kwad’aitar da a nemi ilimi komai nisan wurin za a same shi.
Ina mik’a godiyata mai d’imbin yawa ga malamina kuma uba a gare ni, wanda ya jure da yanayin rayuwata, yake ba ni shawarwari kuma yake d’aukar nauyin duba wannan aiki nawa. Wannan malami shi ne malam Sama’ila Umar Allah ya saka masa da mafificin AlherinSa ya kuma gafartawa mahaifansa ya sa aljanna ta zama makomarsu shi da zuriyarsa baki d’aya amin.
Godiya ta musamman ga dukkan malaman Sashen Harsunan Nijeriya da na Sashen Turanci dukkansu na Jami’ar Usmanu ‘DANFODIYO Sakkwato. Ina mik’a godiyata ga malam Nazir Abbas da Dr. Umar Bunza, haka kuma, ina mik’a godiyata ga iyayena, da kuma ‘yan uwana da abokan arzik’i na gida da kuma wad’anda muke tare da su a makaranta baki d’aya. Har ila yau, ina mik’a godiyata ga duk wanda ya ba da taimako ta kowane fanni domin ganin cewa na sami nasarar ci gaba a tsarin rayuwata, don ganin rayuwata ta inganta. Haka kuma wannan aikin ba zai kammala ba sai na mik’a godiyata ga abokaina Tukur Umar, Abdullahi Usman da Is’haka Aliyu da Abubakar Mainasara da Adamu Lemu da Lawal Ahmad Maru da dai sauran abokan karatu gaba d’aya, na gode Allah ya saka da mafificin alherinSa gare su da iyalanSu baki d’aya.
Ba zan yi tuya in manta da albasa ba, tilas ne in mik’a godiyata ga malamina, wato malam Yusuf Ka’oje da ke Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sakkwato (C.O.E.) wanda ke Sashen Koyar da Harshen Fulfulde. Ya taimaka min matuk’a wajen ganin wannan bincike ya kammala, ba abin da zan ce sai godiya mai tarin yawa a gare shi Allah ya saka mishi da alherinSa amin.
Godiya ta girmamawa zuwa ga yayyena da k’annena wad’anda su ne matsayin jagorannina ta kowace hanyar rayuwata, ina mik’a godiya da kuma gaisuwar ban girma zuwa ga Nasare Dayi da Fatima Dayi da Faruku Dayi da Abubakar Dayi da fatar Allah ya taimake su da hanyoyin alherinSa fiye da taimakon da suka yi min. Haka kuma ina mik’a gaisuwata zuwa ga k’annena Hadiza Dayi da Halima Dayi da kuma masoyiyata Hassana D. Muhammad Zagga da fatar Allah ya taimake su da alherin Sa fiye da tamakon da suka yi mini. Allah (S.A.W.) Ya taimaki duk wanda ya ba ni gudummuwa wajen ci gaban rayuwata da tarbiyyata, Ya kuma saka masu da gidan aljanna Amin.
GAB ATARWA
Babu shakka masana da manazarta sun yi bayanai masu muhimmanci da gamsarwa a kan harshen Hausa. Hausa harshe ne wanda duk d’an asalin harshen yake tunk’aho da shi. Harshen Hausa yana d’aya daga cikin harsunan da ake samu a nahiyar Afirika ta Yamma. A nazari irin na masana ilimin kimiyar harshe, harshen Hausa yan a cikin wani gundari babban rukuni na sauran harsunan duniya. Wannan aiki ya gudanar da bincike ne a kan yadda ake samun kamanci ko bambanci tsakanin jimloli biyu na Hausa da na Fulatanci (Fulfulde) wato jimlar korewa da ta tambaya, domin fayyace irin dangantakar da ake samu tsakaninsu.
An karkasa aikin zuwa babi-babi inda aka fitar da babuka hud’u don samun nasarar kammaluwar aikin. Babi na farko yana d’auke ne da Shimfid’a da kuma Waiwayen ayyukan da aka gabatar da suka shafi nahawun harshen Hausa da na Fulatanci (Fulfulde). Bayan an waiwayi ayyukan masana sai aka sami dalilin gudanar da binciken da kuma manufar da bincike yake d’auke da shi. An bayyana farfajiyar da za a gudanar da binciken, da hanyoyin gudanar binciken da kuma muhimmancin da binciken yake da shi. Daga k’arshe kuma sai aka nad’e babin da tak’aita abin da ya k’unsa.
A babi na biyu kuma an fito da ma’anar jimlar Hausa da ta Fulatanci (Fulfulde)) da ire-iren jimla, kamar jimlar tambaya, jimlar korewa, jimlar umurni da kuma sassauk’ar jimla. Daga k’arshe kuma an nad’e babin da bayanin kammalawa.
A babi na uku kuma an nuna kamanci na jimlar tambaya ta Hausa da ta Fulatanci (Fulfulde) da kuma Bambanci na jimlar tambaya ta Hausa da ta Fulatanci (Fulfulde). Haka kuma, an fito da kamanci da Bambanci na jimlar korewa ta Hausa da ta Fulatanci (Fulfulde). A k’arshe an nad’e babin ta hanyar tak’aita jawabin kammalawa.
Babi na hud’u kuwa babi ne da yake k’unshe da tak’aitawar aikin gaba d’ayansa, tare da jawabin kammalawa. Manazarta ta biyo baya domin inganta aiki gaba d’aya.
ABUBUWAN DA KE CIKI
Tabbatarwa ii
Sadaukarwa iii
Godiya i’b
Gabatarwa ‘bii
Abubuwan da ke ciki id’
BABI NA D’AYA: BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA
1.0 Shimfid’a 1
1.1 Bitar Ayyukan Da Suka Gabata 1
1.1.1 Bitar Kundaye 2
1.1.2 Bitar Muk’alu 4
1.1.3 Bitar Littattafai 6
1.2 Dalilin Bincike 8
1.3 Manufar Bincike 8
1.4 Farfajiyar Bincike 9
1.5 Hanyoyin Gudanar Bincike 10
1.6 Muhimmancin Bincike 11
1.7 Nad’ewa 11
BABI NA BIYU: MA’ANAR JIMLAR HAUSA DA RABE-RABEN TA
2.0 Shmfid’a 12
2.1 Ma’anar Jimla 12
2.2 Ire-Iren Jimlolin Hausa 13
2.3 Jimlar Tambaya 15
2.4 Jimlar Korewa 17
2.5 Sassauk’ar Jimla 21
2.6 Jimlar Umurni 22
2.7 Nad’ewa 24
BABI NA UKU: KAMANCI DA BAMBANCI NA JIMLAR TAMBAYA DA TA KOREWA TA HAUSA DA TA FULATANCI (FULFULDE)
3.0 Shimfid’a 25
3.1 Kamanci na Jimlar Tambaya Ta Hausa Da Ta Fulatanci
(Fulfulde) 25
3.2 Bambanci na Jimlar Tambaya Ta Hausa Da Ta Fulatanci
(Fulfulde) 28
3.3 Kamanci Na Jimlar Korewa Ta Hausa Da Ta Fulatanci
(Fulfulde) 30
3.4 Bambanci Na Jimlar Korewa Ta Hausa Da Ta Fulatanci
(Fulfulde) 32
3.5 Nad’ewa 34
BABI NA HUD’U: TAK’AITAWA DA KAMMALAWA
4.0 Tak’aitawa 35
4.1 Kammalawa 36
4.2 Shawarwari 38
Manazarta 40
https://www.amsoshi.com/tuntubi-masu-gudanarwa/
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.