Ticker

6/recent/ticker-posts

Matsalolin Koyar Da Maguzantattun Wakokin Hausa

Maƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa da ƙasa a kan Ƙalubalen Koyar da Harsunan Afrika wanda Association des Auters Nigeriens en Langues Nationales (ASAUNIL) ta shirya tare da haɗin guiwar Nagerian Indigenous Languages Writers Association (NILWA) a Emir Sultan Venue, Niamey Janhoriyar Nijar daga ranar 19 zuwa 21 ga watan Fabrairu 2014

www.amsoshi.com

Ibrahim Abdullahi Sarkin Sudan
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
E-main: ibrasskg@gmail.com
Lambar Waya: +2348036153050

GABATARWA

Sauyawar da aka samu na al’amurran Hausawa a sakamakon karɓar addinin musulunci ya daidaita yanayin rayuwarsu ta fuskokin da dama. Suturar da suka saba sawa ta sauya. Irin abincin da suke ci ya inganta musamman ta fuskar fayyace haram. Mu’amalarsu ta kasuwanci da zamantakewa da fayyace haƙƙoƙin juna duk sun shiga zukatan mutane kuma sun yi tasiri ainun. Baya ga waɗannan kuma hatta da lafuzzan da aka yarda mutum ya furta shi ma addinin na musulunci da al’adar kunya sun ƙarfafa shi ta yadda ya zama baƙon abu mutum ya buɗe baki ya yi ashar ko ya furta batsa. Duk wanda ya ɗabi’antu da furta ire-iren waɗannan lafuzza sai a ɗauke shi mutumin banza ko la’ananne.

A irin wannan rayuwa da ake ciki, sai ga shi an wayi gari wasu makaɗan Hausa musamman waɗanda suke da birbishin Maguzanci a rayuwarsu sun bijire. Ba su damu su rinƙa furta irin waɗannan kalmomi ba duk da kasancewar shi tsohon yayi. Maƙasudin wannan nazari shi ne fito da wannan matsala a fili musamman na irin ƙalubalen da ake fuskanta wajen koyar da ɗiyan waɗannan waƙoƙi ga ɗaliban adabi.

2.0 WAIWAYE

Kafin bayyanar addinin musulunci da tasirinsa a rayuwar Hausawa, rayuwa ce da ba ta dogara ga wani tsari mai armashi ba dangane da abin da mutum zai furta. A rayuwa maguzanci, mutum na iya buɗe baki ya faɗi duk abin da ya ga dama muddin dai bai ci fuskar wani ko ya haddasa husuma a tsakanin mutane ba. Babu wani takunkumi wajen yin ashar ko faɗar kalmomin batsa. Babu wani ƙasƙanci ga babba don ya yi batsa ko ashar a gaban yara ko waɗanda ya kamata ya ji kunya. Haka shi ma yaro, kasancewar babba ko wani surukinsa a wuri ba dalili ba ne da zai kasa ƙunduma zagi ko ashar ko kalaman batsa ba. Wannan wani babban reshe ne daga abin da aka kira maguzanci wanda kuma ake ganin ya munana rayuwa musamman ta Hausawan da ba musulmi ba (Maguzawa).[iɗ

Abu ne mai sauƙi a kasa bambance Bamaguje da Bahaushe (Musulmi) a wajen mu’amalar yau da kullum in ba lokacin salla ya yi ba. To amma da zarar aka ce kowanensu ya buɗe baki ya yi magana musamman wajen hira ko zance na raha, nan za a fahimci lafuzzan Bamaguje sun bambanta. Za a ji Bamaguje na luguden kalmomin batsa ko ashar ba tare da ya damu ba. Al’adar Maguzawa ta ba su dama ko ma ta ƙarfafa ire-iren waɗannan lafuzza musamman idan mun ɗauki abin da ke faruwa a wajen ɗaurin aurensu a matsayin misali. Maguzawa suna amfani da ire-iren waɗannan lafuzzan wajen ɗaura aure.

Ni Wane na ɗaura auren Wane da Wance.

In ga ɗan jar ƙaniyar da zai raba.

Ni Wane na ɗaura auren Wane da Wance

In ga ɗan babban bura-uban da zai raba.

Ni Wane na ɗaura auren Wane da Wance.

Ba ɗan kutumar babakeren babban buran-uban

da zai raba wannan auren sai wanda ya kwana

da uwarsa. A nan duniya ba ta da wani miji in ba

Wane ba.”

Na ɗaura auren nan ɗamar.

In ga ɗan durin uwar da zai kwance shi.

Na ɗaura auren Wane da Wance

 Ba ɗan jar durin uwar da zai kwance shi.

3.0 TANKAƊE DA RAIRAYA

Haƙiƙa waɗannan lafuzza in har an iya ambaton su a muhallin ɗaurin aure cikin bainar jama’a, ba za su zama abin zargi ba idan sun fito a zantuttukan yau da kullum. Ga wanda yake musulmin Bahaushe, kuma ya tarbiyantu da ilimi da ladubba na addinin musulunci, haramun ne ya ambaci haka. Tun yara suna ƙanana ake hani gare su da yin zagi ko furta kalmomin batsa. A duk lokacin da bakin wani ya kubce ya furta batsa ko ashar to kan masu sauraro yakan yi nauyi. Wani ya ji kamar ya nutse don kunya ko takaici. Idan mai faɗar maganar da gangan ya yi, to tun daga wannan lokacin ya shiga cikin kundin marasa kunya na wannan al’umar. Za a rinƙa kallonsa mutumin banza. Za a fara tsoron gardama da shi, ko ma mu’amala da shi don tsoron kada ya ƙunduma wa mutum ashar. Ta fuskar jin kunyar furucin irin waɗannan lafuzza kuma (ga masu kyakkyawar tarbiyya) hatta da lafuzzan Kur’ani da ya yi kama da su ana jin kunya ambata. A wannan nazari an ɗauki duk wani abu da za a furta dangin ashar ko batsa a matsayin maguzanci .

4.0 MAGUZANTATTUN ƊIYAN WAƘOƘIN HAUSA

Duk da kasancewar Hausawa (Musulmi) suna rayuwa a cikin al’umar da ta katange kanta daga munanan lafuzza, sai ga shi wasu makaɗan Hausa ba su mayar da wannan abin kunya ba. Kai tsaye sukan buɗe baki amma a cikin waƙa su yi batsa ko ashar ba tare da an zarge su da yin abin assha ba. A wannan fasalin, za a kawo misalan ashar da batsa kamar yadda suke zuwa daga bakunan makaɗan don kawai a tabbatar da dugadugan nazarin.

Ashar

Ashar na nufin muguwar magana ko zagi wadda ta saɓa wa tarbiyar al’uma. Duk wata kalma da za a buɗe baki a furta da niyyar zagi, to ana kiran shi ashar. Waɗannan kalmomi keɓaɓɓu ne duk da yake suna iya bambanta daga wuri zuwa wuri. Ga misalin waɗannan kalmomi ko lafuzza a bakin wasu makaɗan Hausa.

Mamman Shata a Waƙar Gagarabaɗau:

Ɗan ƙundun durin uwa

Shadidi mazinaci

Gambu Dogo Mai Kalangu

Sai ya yi kwatakyas yah hwaɗi zaune

Jab babban bura-ubanga

Sarki ya ji tsoro

Mi arranar yaƙin Talakka.

Gambu Dogo Mai Kalangu

Mai shanun noma kaico kanka

Jab babban bura-ubanga

Ka ji kiɗin yawo da zwari

Ana cigiyar banza da yohi

Umaru Sanƙiran Gambu Dogo Mai Kalangu

Dogo ga kyau, ga kyauta, ga ’yab babbab bura’uban sata

- Kassu Zurmi – Waƙar Nomau Namagarya

Yac ce “Ina hita Maikassuwa,

  Amma hwa ba da alheri ba,

 Bari ko an hana ni yanzu da rana,

Sai iskan sha biyun dare ya taso,

Sannan za ni kunna yab bura uba

Magarya sannan wada ko ɗiyansu wasu ba su hita

Waɗannan ’ya’yan waƙa kaɗan kennan daga cikin ɗimbin ire-irensu da suke ɗauke da zagin da a al’adance ba a so a yi su ko a ji su ko ma a kusanta da mai yin su. Duk iyaye ko malamin da suka ɗabi’antu da furta su, to ko shakka babu za a wayi gari yaran da ke kusa su fi shi iya ƙunduma su. Idan kuwa a waje yaro ya koyo su, to iyaye sai sun yi da gaske kafin su fita ƙwaƙwalwar yaro.

Batsa

Batsa na iya kasaancewa duk wata magana ta ɓatanci wadda ke da alaƙa da furucin sunayen al’aura na zahiri ko kuma kalaman da suke nuni ga jima’i tsakanin mace da namiji. Akwai da yawa daga cikin makaɗan Hausa da sukan yi wa ɗiyan waƙoƙin nasu kwalliya da waɗannan kalmomi na batsa. Zai iya kasancewa sun yi haka ne don burge masu sauraro, amma ba don lalurar waƙa ba. To ko dai wane dalili ke gare su na wannan ɓatanci, birbishin maguzanci ne a ji irin waɗannan kalmomi daga mutum mai hankali. Misali:

Ɗan’anace a waƙar Shago

Na yarda don Gato aka aure,

In don daka ku bar ni in yi abuna

Mamman Shata – Waƙar Gagarabadau

Taho nan kwanta ki bubbuɗe ƙafafu,

Ki bubbuɗe ƙafafu,

Ki lullumshe idanu

Sa’adu Bori (ɗaya daga waƙoƙinsa)

Ashe mata wayau suke mana,

Abin daɗi na can ƙasan zani,

Mai hana duri Bura ubanta

Mamman Shata

In kin je kul ki ba da bado,

Yarinya in kin je kar ki ba da bado

-----------------------------------------

In ka ji kwaramniya ɗaki,

Yarinya ta ƙi ba da bado.

5.0 MATSALOLIN KOYAR DA MAGUZANTATTUN ƊIYAN WAƘOƘI

Waɗannan ’yan misalai da suka gabata, sun tabbatar da samuwar tsarmin maguzantattun lafuzza a cikin waƙoƙin makaɗan Hausa. Waƙoƙi makaɗa kuwa suna daga cikin ginshiƙan darussan koyarwa a adabin bakan Bahaushe. Idan har za a koyar da adabin musamman na waƙa ba da su ba, to lallai an bar giɓi. Sannan kuma akwai bukatar a cikin irin wannan darussa a nuna illolinsu da kuma illolin koyar da su musamman don gudun yi wa tarbiyya zagon ƙasa. A wannan fasali za a tunkari ƙalubalen waɗannan waƙoƙi a azuzuwan adabi.

Ruguza Tarbiyya

Duk da yake ana cewa, zamani riga ne, sauraro ko kuma nazarin ɗiyan waƙoƙin da ke ƙumshe da ashar ko batsa tamkar ruguza tarbiyar da aka yi wa yara ne a gida. A wasu gidajen an tarbiyantu da rashin sauraron irin waɗannan waƙoƙin. Zai iya zama abin sha’awa ga yara musamman waɗanda suka fara tashen balaga, su rinƙa jin su. Rera su a cikin waƙa zai fi sauƙin shiga rai fiye da nauyin da za su iya ɗauka a cikin zance. idan haka ya samu to an yaye tarbiyar da aka gina na lokaci mai tsawo. Kuma wannan ya zama wata kafa na gurɓata lafuzzan da za a ji yana fitowa a bakunansu musamman idan suna cikin sa’o’insu.

Zubewar Mutuncin Malami

Daga cikin abin da ya kamata a ce malami ya siffantu da shi musamman wanda ake ɗammahar yara su koya shi ne kyakkyawar lafazi. Ƙoƙarin koyar da ko kuma bayanin ƙumshiyar waɗannan ɗiyan waƙoƙin ba ƙaramar illa take jawowa ba na kimar malami a idon ɗalibi. Ko da ya kasance kayarwa ake yi, a duk lokacin da malami zai saki jiki wajen kawo misalan waɗannan waƙoƙi, za a fara yi masa kallon mara kunya, ko mara mutunci. Ba wani tsawatawa da malam zai yi na furucin ire-iren waɗannan kalmomi idan ɗalibi ya zo da su ko da a cikin zance ne.

5.3 Zurfafa Bincike

A duk lokacin da aka yi wa ɗalibi darasin da yake sha’awa, to kamar an ba shi kafa ne na ƙara zurfafa bincike wajen sanin wannan abu ko da kuwa a lulluɓe aka zo da shi. Kada a ji mamakin idan malami ya bayar da misali ɗaya na waɗannan ɗiyan waƙoƙi, a mayar masa da goma idan ya yi tambaya. Duk abin da yake da muni ko al’ada ta yi hani da shi ya fi saurin shiga zuciya da haddacewa. Samun tarin waɗannan lafuzza a zukatan matasa zai iya gurbata tunani na tabbatar da faɗar mawaƙi.

 NAƊEWA

Kalmomin ashar ko batsa in ba Bamaguje ba, ba Bahaushen da al’ada ta yaye wa lulluɓin yinsa kai tsaye a bainar jama’a. Duk da yake tun fil azal ana samun tsarmin waɗannan ɗiyan waƙoƙi a gargajiyance kamar a cikin waƙoƙin gaɗa da na daɓe, amma fitowarsu a irin wannan muhalli, ba ƙanƙanin abin tashin hankali ba ne. A can da a inda aka yi su a nan ake barinsu (a dandali ko wajen aikin daɓe). Shigowar irin waɗannan waƙoƙi a muhallin da kowa zai iya cin karo da su, wata matsala ce da wannan maƙalar ta gano, kuma ta fahimci illarta ta ruguza wani sashe na tarbiyya a al’uma. Waƙoƙin da ke ƙumshe da ashar da Batsa haƙiƙa an riga an yi su kuma sun shiga jama’a. To sai dai har yanzu akwai wata ’yar dama na sanin yadda za a yi nazarin su da bayanin su ga ɗaliban adabi. Idan har malamai da ɗalibai za su riƙa sara suna duban bakin gatari, to talalaɓiyar da ta ja makaɗan suka rera su (waƙoƙin) ba za ta kayar da su ba. Haƙiƙa wannan nazarin tamkar hannunka-mai-sanda ne ga tunanin keɓo ɗalibai da malamai daga komawa ga rayuwa ta maguzanci.

MANAZARTA

Abdullahi, I. S. S. 2008, ”Jiya Ba Yau Ba: Waiwaye a Kan Al’adun Matakan Rayuwar Maguzawana Aure da Haihuwa da Mutuwa.” Kundin Digiri na Uku (Ph.D Hausa Culture) Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Abdullahi, I. S. S. 2008. “Fitattun Ɗabi’un Maguzawa” Maiduguri Journal of Linguistics

and Literary Studies (MAJOLLS) Vol. X Department of Languages and Linguistics, University of Maiduguri.

Abdulkadir, M. F. 1988: “Culture and Linguistic Behaviour: A Sementic Study of Hausa

Insult words. Unpublished” M. A Dissertation, Dept. of English A. B. U. Zaria

Douglas, M. 1966: Purity and Danger: An Analysis of concepts of Pollution and Taboo.

London – Routledge and Kegan Paul.

Ɗangambo, A. 1984, Rabe-raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar

Hausawa. Kano: Triumph Publishing Company LTD

Garba, A. 1982, “Mammam Shata Da Waƙoƙinsa.” Kundin Digiri na ɗaya (B. A. Hausa)

Jami’ar Bayero, Kano

Gusau, S. M. 2008, Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu

Kano: Benchmark Publishing Limited

Gusau, S. M. 2009, Diwanin Waƙoƙin Baka Zaɓaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka na

Hausa Kano: Century Reseach and Punlishing Limited

Usman, B. B. 1990, “A Sociolinguistic Study of Tabboos in Hausa” M. A. Hausa Thesis,

Bayero University, Kano

[iɗ Maguzanci na nufin halaye da ɗabi’un Maguzawa waɗanda suke da ala}a da rayuwarsu ta gargajiya

kuma ba su da wani birbishi na addinin Musulunci. Don }arin bayani, dubi Abdullahi, I. S. S. (2008)”Jiya

Ba Yau Ba: Waiwaye a Kan Al’adun Matakan Rayuwar Maguzawana Aure da Haihuwa da Mutuwa.”

Kundin Digiri na Uku (Ph.D Hausa Culture) Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Post a Comment

1 Comments

ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.