Ticker

6/recent/ticker-posts

Karan Kirjin Maguzawa

 Wannan nazarin ya fito da al’adar karan ƙirji a fili musammasn ga waɗanda ba su san shi ba. Kamar yadda nazarin ya nuna, al’ada ce ta rufe ƙirjin amaryar da aka ga alamar ta sami shigar ciki. Wannan al’ada kasancewarta matakin farko na al’adun haihuwar Maguzawa, saƙo ne ga amarya da sauran jama’a cewa, aure ya yi albarka, irin da aka shuka ya tsiro. Duk da yake wannan al’ada ba ta sami wata kafa a rayuwar Hausawa (musulmi) ba, fa’idojinta suna da yawan da ke tabbatar da Maguzawa mutane ne masu tsararren rayuwa mai la’akari da kare mutunci da ba kowa hakkinsa a cikin al’uma.

www.amsoshi.com

Karan Ƙirjin Maguzawa

Dr. Ibrahim Abdullahi Sarkin Sudan
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo, Sakkwato.
e-mail: ibrasskg@gmail.com
Tel: 0803 6153 050

 GABATARWA

Daga cikin fa’idojin da ake samu na zaman mutane a wuri ɗaya kuma su kasance al’uma ɗaya shi ne samar wa kansu waɗansu hanyoyi na rayuwa waɗanda suka aminta da shi a matsayin abin alfanu a gare su. Irin wannan tunani ne kan sa ɗaiɗaikun hanyoyin gudanar da rayuwa sukan bambanta tsakanin mutane. Abin da wasu suke ɗauka da muhimmanci, ba zai karɓu ba a wata al’umar, ba don rashin muhimmancisa ba, sai don kawai tunaninsu bai hango can ba. Gane fa’idar al’adar da al’uma ta keɓanta da ita da kuma rashin fa’idar ta ya dogara ne ga yadda aka sami damar baza ta a faifan nazari.

Maƙasudin wannan nazari, shi ne duban yadda Maguzawa suke gudanar da wata al’ada ta bayyana shigar ciki ga amarya. Maguzawa suna ba wannan al’ada muhimmanci ne saboda la’akari da irin kunyar da ke tattare da matakan samun cikin farko ga amarya. Wannan al’ada tamkar wata hanya ce ta yaye yanar kunya da take lulluɓe bayyana wa amarya da sauran jama’a cewa, ta sami shigar ciki. Haka kuma a tasu fahimtar, shigar cikin wani muhimmin mataki ne da ke nuna albarkar aure. Wannan ya sa aka tanadar masa waɗansu al’adu na musamman a matsayin wani mataki a al’adar haihuwa a rayuwar tasu. A wannan nazari, za a kalli yadda Maguzawa suke aiwatar da wannan al’ada ta karan ƙirji da kuma hikimomin da ke tattare da ita. An keɓe wannan nazari ne ga mutanen da ake Maguzawa da tunanin cewa su ne Hausawa asali waɗanda akasarin al’adun Hausawa na gargajiya suka samo asali daga garesu.[i]

2.0 FASHIN BAƘI

Wannan fasali zai yi ƙoƙarin yin sharhi ne a kan abin da ake kira Karan Ƙirji. Ga dukkan alamu dai duk kalmomin biyu Hausawa ne. Wato, ba aro su aka yi daga wasu harsunan ba. A nahawun Hausa, kara ko kare ko karewa kalma ce ta aikatau mai nufin killace ko yin katanga don asirta wani abu (Ƙamusun Hausa 2006:234). Kalmar ƙirji kuwa suna ne na wani sashen jikin abu mai rai (musamman mutum) wanda ya yi iyaka da wuya ta sama da kuma ciki ta ƙasa. Wannan sashe ne muhallin nono, kuma a nan ne ƙasusuwan awazu/haƙarƙari suka haɗu. Haɗa waɗannan kalmomi biyu ya nuna cewa, bisa ma’ana, sirrantawa ko katangewa ake ɗammahar a yi wa sashen da ake kira ƙirji. Idan kuwa haka ne, to tambayoyin da za su tuzgo a nan su ne: A wannan al’ada, ƙirjin wa ake karewa? Me ya sa ake so a kare ƙirjin ba wani sashe na jiki ba? Waɗanne hikimomi ke tattare da wannan al’ada?

A yunƙurin lalubo bayanan da za su amsa waɗannan tambayoyin an fahimci cewa, jinsin mata na Maguzawa ake aiwatar wa wannan al’ada. Haka kuma ba a kan yi shi sai ga matar aure. Ita kuma matar auren, dole ta kasance amarya ce, ko a ce yarinyar da ta yi auren farko kuma ba ta taɓa haihuwa ba. Har ila yau, ba a gudanar da wannan al’ada sai an yi la’akari da alamomin shigar cikin ga amarya.

Kafin matan gida (’yan’uwan ango da iyayensa) su fara zura ido don ganin alamomin samun juna biyu ga amarya, sukan so su san shin an ma fara saduwar aure tsakanin ango da amarya? Abu ne mawuyaci Maguzawa su yarda su bayyana saduwa a tsakanin ma’aurata. Al’adar kunya da hidimomin da ake gudanarwa da rana da tsarin muhallin da ake zaune, ba su ba da damar ango ya keɓanta da amarya da rana tsaka ba. Ma’aurata sukan yi amfani da damar lokacin kwanciya barci ne da dare kawai domin su ɗebe sha’awa a tsakaninsu. Sukan ji kunya matuƙa idan har suka bari wani ya riske su a cikin wannan yanayin. Haka su ma mutanen gida sukan nesanta da muhallin ango da amarya musamman a lokacin da ake ɗammahar su iya amfani da shi don ɗebe Sha’awa.

Akan sami tabbacin lallai ango ya kusanci amarya ne ta hanyar la’akari da sauyawar yanayin tafiyarta idan gari ya waye. Duk yadda amarya ta kai ga juriya, tsofaffi daga cikin matan sukan fahimci alamomin jin rauni a gaban mace musamman idan yarinya shataf aka auro. Wannan kan sa wata tsohuwa ta kusance ta, ta farsa mata gabanta da ruwan ɗumi. Haka dai za a ta yi sannu a hankali har ta saba. Tun daga wannan lokacin ne manyan mata a gidan za su ta ƙoƙarin kula da alamomin da suke sa ran su gani na sakamakon waɗannan saduwar.

3.0 ALAMOMIN SHIGAR CIKI

Yanayin tsarin jikin Maguzawa bai bambanta da na sauran al’umomi na duniya ba. Wannan ya sa ba wasu alamomi na daban Maguzawan suka keɓanta da su a matsayin alamomin shigar ciki ba. To sai dai fasahar kowace irin al’uma dangane da kowane lamari yana iya bambanta. A nasu tunanin, akwai wasu ’yan sauye-sauye da kuma halaye ko ɗabi’u da sukan yi la’akari da su idan amarya ta sami shigar ciki. Waɗannan alamomi sun fi fitowa a fili ga macen da ba ta saba ba. Ita wadda ta saba, suna ganin tana iya ɓoye wasu lamurra ta yadda za a kasa tsinkayarsu kai tsaye.

Akan gane amarya ta sami shigar ciki ne idan aka ga ta faye yawan kukan ciwon ciki da zubar da yawu (miyau) da amai. Ga wadda ba ta saba ba, za ta shiga cikin damuwa da tunanin ko wani rashin lafiya ne. Sauran mata da ke lura da ita musamman tsofaffi, za su shiga murna suna cewa, “lallai Wance ta sami shigar ciki.” Tabbacin haka yakan ƙara bayyana ne idan an lura da tana sauya kamanni, tana yin haske kuma tana ƙara ƙiba. Haka ma za a ga ta fara zaɓen abinci. Wato ta ce ba ta son wannan, ko ta fi son abu kaza, ko ba ta son jin warin abu kaza da dai sauransu. Wata alama kuma da Maguzawa ke la’akari da ita wajen gane mace ta sami shigar ciki ita ce, idan an ga kan nononta ya yi baƙi. Wannan abu ne mai sauƙi kowa ya lura da shi domin a kowane lokaci amarya da ma sauran matan gidan ƙirazansu a buɗe suke. Suna ɗaura zani ne a kwankwaso kawai. Duk wata alama da ake son gani a nonon mace musamman amarya ana iya lura da ita ba tare da an ta ’yan dabaru ba.

Ga matar da ba ta saba haihuwa ba, ɓatan wata, wato rashin ganin jinin al’ada a lokacin da ta saba gani ita ce alamar farko. Sauran jama’a ba za su lura cewa, ba ta ga jinin wata ba, saboda ba wani tanadi na musamman da al’adar ta yi da za a gane ana al’ada kamar yadda mata Musulmi ke barin yin salla. Wasu amaren sukan gaya wa matan da suke kusa da su cewa, ba su ga jini wannan watan ba. Su kuma sukan gargaɗe su da kada su gaya wa kowa saboda abin kunya ne mace ta fito fili, ta bari a gane ba ta ga wata ba.

DABARUN KARAN ƘIRJI

Bayan mutanen gida sun sami tabbacin amarya ta sami juna biyu, sai a fara shiryen-shiryen aiwatar da wannan al’ada ta Karan ƙirji amma cikin sirri, ba tare da amaryar ta sani ba. Bambancin da ake samu a tsakanin muhallin Maguzawa daban-daban ya samar da dabarun da suka saɓa wa juna na yadda ake aiwatar da ainihin wannan al’adar. Ga huɗu daga cikinsu.

4.1 ‘Daura Sabon Zani a Rufe Ƙirji

Idan alamomin da aka yi la’akari da su sun bayyanar da shigar ciki, matan gidan za su zaɓi rana ta musamman da za a yi mata karan ƙirji. Kafin wannan ranar, iyayen ango mata, za su tanadi sabon zani su ajiye. A ranar da za a yi karar ƙirjin, za a shirya da ɗaya daga cikin matan da ke da dangantaka da gidan kamar matar wan miji, ko wata ƙanwar uban miji. Ita za a miƙa wa wannan zanin, ta yi ta kiwon hankalin amarya, tana cikin gudanar da lamurranta na gida, sai ta ɗauko zanin ta zo ta bayanta ta ɗaura mata a ƙiji, ta fufe mata nono. Da amarya ta ga haka, za ta ji kunya ta fahimci an gane ta sami shigar ciki. Za ta rufe fuskarta da tafin hannuwanta, ta gudu zuwa ɗakinta tana kuka.

Bayan wani ɗan lokaci, sai a sami waɗansu matan su shiga ɗakin su rarrashe ta, su ba ta haƙuri. Tun daga wannan lokacin zanin zai kasance ɗaure a ƙirjinta. Ko da ta sake wani zanin, dole ta ɗaura shi ya rufe mata nono har lokacin da ta haihu. Duk wanda ya shigo gidan ya ga ƙirjinta a rufe zai fahimci an yi mata wannan al’adar ta karan ƙirji, wanda ke nuna ta sami shigar ciki. Wannan zai sa a yi ta taya ta murna, ana mata fatar a sauke lafiya. Amarya za ta kasance cikin takunkumin sakin jiki a gidan har na kimanin kwana uku. Daga baya kuma ta fara gudanar da lamurra kamar yadda ta saba.

‘Daɗɗaki

‘Daɗɗaki wani suna ne da kuma dabara da wasu Maguzawan suke amfani da ita a matsayin karan ƙirji.[ii] A tasu al’adar, bayan an tabbatar da shigar ciki ga amarya, za a tanadi wani zani a ajiye. Za a haɗa kai da wata tsohuwa, a ba ta zanin ta shammaci amarya ta ɗaura mata shi a ƙirji. Amarya na ganin an ɗaura mata wannan zanin za ta gudu ta shige ɗaki tana jin kunya. Haka dai za ta ci gaba da rufe ƙirjin har sai ta haihu. Hikimar sa tsohuwa ta aiwatar da wannan al’adar yana da nasaba da tunanin kada kunyar da ke tsakaninta da matan gidan ya kau.

Amfani Da ‘Danyen Man Shanu

A maimakon zanin da ake ɗaura wa amarya a ƙirji, Maguzawan Gidan Gwarzo a ƙasar Sayaya ta ƙaramar hukumar Matazu cikin jihar Katsina ɗanyen man shanu suke amfani da shi. Idan iyayen ango (mata) suka gama lura da bayyanar alamomin shigar ciki, za su tanadi ɗanyen man shanu a asirce su ajiye. Za a sa rana, a shirya da wani ƙanin angon ko taubashinsa wanda shi ake son ya aiwatar da wannan al’adar.

Wannan ƙanin angon zai bari sai amarya ta saki jiki, ya lakato man shanun nan da hannunsa ya shafa mata a kan nonnanta. Da yin haka zai yi ta kansa domin za ta bi shi da duka. Duk abin da ta samu tana iya kwaɗa masa cikin hushi. Daga nan sai ta shiga ɗakinta ta ɗauki wasu ‘yan kaya nata ta bar gidan da sunan an yi mata laifi ta yi yaji. A irin wannan yajin, ba ta komawa gidan iyayenta wai don kunya da gudun kada a ji sauƙin gane inda ta tafi a bi ta. Tana iya zuwa wurin wata ’yar’uwarta da ke aure a wani ƙauyen na daban, ko wurin wasu dangin uwarta a wani wuri can da ba a taɓa sa ran za ta tafi. A al’adance, shi wannan ƙanin mijin da ya shafa mata man shanu a nono zai tafi biko. Idan ya gano inda take, zai ce ya biyo Wance. Mutanen gidan za su ce, ai matarku ce. Sai a yi mata magana, a rarrashe ta, ta shirya ta bi shi. Haka za su kamo hanya tare suna hira, ana ba’a irin wadda ke tsakanin ƙanin miji da matar wa. Idan an kusa kawowa gida sai ta ɗaure fuska kamar ba tare da shi suke ba, har su iso gida. Tun daga wannan lokacin ita ma za ta rinƙa ɗaura zani a ƙirjinta har lokacin da ta haihu. Tunanin waɗannan Maguzawan dangane da shafa mata man shanu a nono shi ne a sanar da ita cewa, lokaci ya yi da al’ada ta tanada ta fara rufe su, kuma abokin wasa kaɗai zai iya yi mata wannan isharar a zauna lafiya.

4.4 Lulluɓa Zani A Kai

A al’adar Maguzawan Kaibaki ta ƙasar Fago a Jihar Katsina, idan an ga alamar shigar cikin za a aika wata mata ta faɗo wa iyayen amarya a asirce. Su kuma bayan wani lokaci sai su ɗinko wani farin zani su bayar a kawo. Ba za a bari ta san an kawo wannan zani ba. Sai an ga alamar cikin ya kai wata bakwai, za a sami wata rana a shammace ta tana zaune a ɗauko wannan zanin a rufa mata. Sai ta fara kuka don kunya. Za ta shige ɗakinta ta ƙi fita har kwana uku saboda kunya. Bayan kwana ukun za ta fara fitowa tana ɗaure da wannan zanin a ƙirjinta. Ba za ta yi wa kowa magana ba sai a hankali ta fara sakin jiki kamar dai yadda ta yi a lokacin da take amarya.

5.0 DADDAGE

Karan ƙirji shi ne abu na farko da yake bambanta matakan rayuwar Maguzawa. Idan aka ɗauki aure a matsayin mataki na farko, to da wannan al’ada ake shiga mataki na biyu, wato haihuwa. Amarya tana cikin wani yanayi na amarci a gidan miji za a yi amfani da wannan al’adar a nuna mata ta shiga mataki na biyu na rayuwa (haihuwa). Karan ƙirji tamkar wani mabuɗi ne na shiga al’adun haihuwa. Wannan fasali zai kalli hikimomin da ke ƙunshe a cikin wannan al’ada ta karan ƙirji.

Al’adar ta karan ƙirji wata hanya ce ta sanar da jama’a da ’yan’uwan amarya da na ango cewa, an sami shigar ciki. Ko da ba a gudanar da shi a gaban mutane ba, da zarar an gan ta da zani a ɗaure a ƙirji, to an fahimci cewa lallai ta sami ciki. Wannan saƙo yakan kwantar da hankalin duk wanda yake da dangantaka da auren, domin an sami albarkar da kowane aure yake so. Ta amfani da wannan saƙon ne za a fara duk shirye-shiryen da suka dace masu alaƙa da haihuwa. Duk mai hakki zai fara tunanin hanyoyin sauke abin da ya rataya a wuyansa ta la’akari da wannan ishara da aka nuna masa.

A al’umar da ake ba haihuwa muhimmanci, kwanciyar hankalin kowane ango ne ya san ya auro matar da za ta haifar masa ’ya’ya. Sakamakon farko ga Maguzawa na ɗawainiyar aure shi ne su ga mace ta sami shigar ciki. Wannan saƙon na al’adar karan ƙirji abin farin ciki ne ga miji da kuma hannunka mai sanda na ƙoƙorin yin tanadin abin da ya rataya a wuyansa. Haka su ma iyayen ma’auratan, wannan al’adar ke tabbatar musu da cewa, ’ya’yan da suka haɗa aure, lafiya lau suke ta fuskar yaɗa zuri’a.

Haka kuma wannan al’adar ita ke ba amarya damar dangin miji su ɗauke mata hidimomin gida da al’ada ta rataya mata don renon cikin da tabbatar da nata lafiyar. Idan da za a bar yanayin nata a ɓoye, to za a sa ta cikin ƙuncin fama da laulayin ciki da kuma aikace-aikacen gida da na gona har sai cikin ya bayyana.

Ganin irin kunyar da ke tattare da bayyana abin da ke faruwa tsakanin ma’aurata kafin a ce ciki ya shiga, abu ne mawuyaci a ce mace ta iya shaida wa ’yan’uwanta ga halin da take ciki. Wannan al’adar ta karan ƙirji, ita ta yaye wannan yanar. A ɓangaren ’yan kallon kuma, shi zai ba da damar mutane su yi ta tofa albarka da fatar alheri na abin da suka gani na ƙaruwa. Maguzawa suna sane da fa’idojin da ke tattare da tofa yawun albarka daga mutane a kan abin alheri. Haka kuma sukan guji yin abin da mutane za su ta tofa yawun assha.

Al’adar karan ƙirji ga Maguzawa wata dama ce ga amarya ta saki jiki ta tambayi duk abin da ya dace mai alaƙa da haihuwa. Idan da an bar abin a duƙunƙune, to kunya za ta yi mata takunkumin kasa bayyana wa mutanen da ke kusa da ita halin da take ciki na damuwa, ko rashin lafiya ko kuma sanin makamar wasu sauye-sauye da ba ta saba gani ba. Al’adar karan ƙirjin da aka riga aka gudanar ya bayyana wa jama’a halin da take ciki, ba sauran abin ɓoyewa. Wannan zai ba ta damar samun shawarwari da magunguna da fahimtar ladubban da al’ada ta tanada a kan kulawa da kanta da abin da take ɗauke da shi.

A wannan al’ada ta karan ƙirji, nonon mace shi ne muhimmin abin da ake rufewa daga ganin mutane. A al’adance, cikar nono tana da alaƙa da shigar ciki. Haka kuma nono yana daga cikin abin da ke saurin jan hankali da ban sha’awa da motsa kwaɗayi ga wanda ya gani. Wannan al’ada ta rufe nonon mace a lokacin da aka fahimci ta sami ciki, wata kariya ce daga idanun miyagu. Maguzawa sun aminta da cewa, kwaɗayin maita yana iya matsawa idan an lura da cikar ƙirjin mace. Barin shi a buɗe zai iya jefa ta cikin haɗari. Ko ba kamai an nuna cewa, mayu suna sha’awar mace mai ciki ballantana sun gan ta a tuɓe.

Al’adar karan ƙirji, wata dama ce ta ƙarfafa wasannin barkwanci tsakanin amarya da dangin miji wanda hakan kan ƙara danƙon zumunci. Taubasan ango da ƙanninsa maza da mata za su sami kwarjinin yin ba’a da wasanin raha a tsakaninsu da amarya. Ita kuma a nata ɓangaren, shigar ciki da tabbatar da shi ta hanyar wannan al’adar yakan samar mata da karɓuwa ga dangin miji musamman waɗanda tun farko suke da adawa ga ƙulla auren.

6.0 NADEWA

Wannan nazarin ya fito da al’adar karan ƙirji a fili musammasn ga waɗanda ba su san shi ba. Kamar yadda nazarin ya nuna, al’ada ce ta rufe ƙirjin amaryar da aka ga alamar ta sami shigar ciki. Wannan al’ada kasancewarta matakin farko na al’adun haihuwar Maguzawa, saƙo ne ga amarya da sauran jama’a cewa, aure ya yi albarka, irin da aka shuka ya tsiro. Duk da yake wannan al’ada ba ta sami wata kafa a rayuwar Hausawa (musulmi) ba, fa’idojinta suna da yawan da ke tabbatar da Maguzawa mutane ne masu tsararren rayuwa mai la’akari da kare mutunci da ba kowa hakkinsa a cikin al’uma.

7.0 MANAZARTA

Adamu, M. (1976), “The Spread of Hausa Culture in West Africa 1700 – 1900” Savanna No 5 Vol. 1, A Journal of the Environmental and Social Sciences. Published at Ahmadu Bello University, Zaria.

Akodu, A. (2001), Arts and Crafts of the Maguzawa and some Educational Implications. Gaskiya Corporation Limited. Zaria – Nigeria.

Alhassan, H. da Sauransu (1982), Zaman Hausawa

Charanchi, R. (1999), Katsina Dakin Kara: Tarihin Katsina Da Garuruwanta, Northern Nigerian Publishing Company Limited, Zariya.

Fletcher, D. C. (1929) “The Kai-na-Fara.” Extract from Re-assessment Report on ’Yanɗaka District, Katsina Emirate, Zaria Province. M. P. No K. 8833 National Archives and Monuments, Kaduna.

Greenberg, J. (1946) The Influence of Islam on a Sudanese Religion: Monographs of the American Ethnological Society. J. J. Augustin Publisher, New York.

Ibrahim, M. S. (1982), “Dangantakar Al’adu da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa”, Kundin Digiri na Biyu (M.A. Hausa), Jami’ar Bayero, Kano.

Kado, A.A. (1987), “Kainafara Arnan Birchi”, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Sakkwato.

Krusius, P. (1915), “Maguzawa” Archiu, Anthropologies, NF Vol. XIV.

Lawal, A.T. (1986), “Al’adun Hausawa Jiya da Yau”, Kundin Digirin farko Jami’ar Sakkwato.

Madauci I. da wasu (1968) Hausa Customs Northern Nigerian Publishing Company, Zaria.

Mairukubta, H. (1999) “Jego da Reno a Ƙasar Hausa: Tsokaci Kan Hausawan Kabi” Kundin digiri na biyu, Jami’ar Usmanu ‘Danfodiyo, Sakkwato.

Safana, Y.B. (2001), “Maguzawan Lezumawa (Babban Kada) Gundumar Safana”, Kundin Digiri na farko, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato.

Sufi, A. H. (2001) “Hanyar Kiran Maguzawa Zuwa Ga Addinin Musulunci.” Maƙalar da aka gabatar a taron Kwamitin Yaɗa Addinin Musulunci na Jihar Kano.

Travitt, L. (1973) “Attitudes And Customs In Childbirth Amongst Hausa Women In Zaria City,” Savanna No 2 Vol. 2, A Journal of the Environmental and Social Sciences Published at Ahmadu Bello University, Zaria.

Tremearne, A. J. N. (1913) Hausa Superstitions And Customs. John Bale, Sons and Danielsson, LTD Oxford.

Umar, M. B. (1980), Al’adun Haihuwa A Ƙasar Hausa. Hausa Publications Centre Zaria.

Yusuf, A. B. (1986), “Wasannin Maguzawan Ƙasar Katsina”, Kundin Digirin farko, Jami’ar Sakkwato.

[i] Maguzawa su ne Hausawan da ba Musulmi ba, masu gudanar da rayuwarsu ta hanyar bin tanadin da aka yi a al’adunsu da addininsu na gargajiya.

[ii] Maguzawan ƙauyen Gidan Bakwai a }asar Faskari cikin jihar Katsina su ke kiran wannan al’ada da ɗaɗɗaki

Post a Comment

0 Comments