Cite this article as: Abdullahi, I. S. S. (2012) “Zawarci da Auren Bazawara A Maguzance” in Champion of Hausa Cikin Hausa, A Festschrift in Honour of Ɗalhatu Muhammad. Department of African Languages and Cultures Ahmadu Bello University, Zaria Pages 473-479 ISSN: 2315-9820.
Zawarci Da Auren Bazawara A Maguzance
Daga
Ibrahim Abdullahi
Sarkin Sudan (Ph. D)
Sashen Koyar da
Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Usmanu ɗanfodiyo, Sakkwato.
e-mail:
kontago2003@yahoo.co.uk
GSM:
08096266581/08036153050
GABATARWA
Kowace al’umma ta duniya tana da hanyoyi na musamman da take
bi wajen gudanar da wasu al’adu nata da suka shafi zamantakewa na rayuwa. Irin
waɗannan al’adu sukan
bambanta da na wasu saboda waɗansu
tanade-tanade da al’umar ta samar wa kanta. Daga cikin irin waɗannan al’adu akwai matsayin
mace da hanyoyin da za a bi wajen mallakar ta ga namiji a matsayin matar aure.
A yawancin al’umomi na duniya, akan ba lamarin auren budurwa muhimmanci fiye da
wadda ta taɓa yin
aure. Yawancin nazarce- nazarcen al’adu dangane da aure, sun fi mayar da
hankali a kan wannan.
Maƙasudin wannan nazari shi ne a ƙoƙarta duban irin tanade-tanaden da al’adar
Maguzawa ta yi wa auren wadda ba budurwa. Wannan ba zai rasa nasaba da cike giɓin da aka bari da yake,
magabata sun fi mayar da hankalinsu ga duban irin kwaramniyar da ake yi a auren
saurayi da budurwa. Sun sha’afa da cewa, kasancewar mace bazawara ba abin ƙyama
ba ce a al’uma tun da har akwai wani tanadi da aka yi mata. Haka kuma an yi
tunanin karkata ga Maguzawa[i] ne saboda tunanin cewa, mutane ne da suke riƙe da
al’adunsu sau da ƙafa, kuma daga garesu ne ake ganin al’adun Hausawa na
gargajiya suka tuzgo.
2.0 FASHIN BAƘI
Bazawara ita ce matar da ta taɓa
zama a ƙarƙashin
namiji a matsayin matar aure. Daga baya wani dalili ya sa ta wayi gari ba a
cikin wannan yanayi na aure ba. Tun daga wannan lokacin da ta rabu da mijin har
zuwa lokacin da ta yi wani auren ko ta koma wa mijinta, ana kiran ta Bazawara
ko Zawara. Jam’i kuma a ce Zawarawa. Yanayin da Bazawara ke shiga na fafutikar
jan hankalin namiji ko jiran namiji ya fito neman aurenta shi Hausawa ke kira
Zawarci. Akan kira namiji mai neman Bazawara musamman wanda ya taɓa yin aure da Bazawari,
(Bazawarin wance). Haka ma akan ce, “Wane shi ke zawarcin Wance,” idan aka ga
yana hidimar neman Bazawara da aure. Akan bayyana daɗewar mutuwar auren mace ba tare da yin wani
auren ba ta kiranta tsohuwar Bazawara.
SHARUƊƊAN ZAMA BAZAWARA A MAGUZANCE
Mutuwar aure ita ke sa a kira matar da abin ya shafa
bazawara. To sai dai hanyar da akan bi auren ya mutu ba ɗaya ba ce. Akwai fuskoki biyar a maguzance da
ke iya sa mace ta tsinci kanta cikin halin zawarci. Waɗannan hanyoyi har wa yau su ke sa Bazawara ta
siffantu da halaye ko ɗabi’u
na musamman da suka bambanta da na budurwa.
3.1 Miji ya saki mace
A lokacin da ake zamantakewa na aure, akan sami saɓani iri-iri tsakanin
ma’aurata. Idan rayuwar aure ta kai ƙarshe, miji ya fahimci ba zai iya ci gaba
da zama da mace a matsayin mata ba, to yakan sallame ta, ta hanyar nuna mata ya
gaji da auren, ta kama gabanta. Galibi akan kai ga wannan mataki ne bayan an bi
hanyoyi da dama na sulhunta ma’auratan abin ya faskara. Tun daga ranar da miji
ya ambaci ba ya bukatar zaman shi da mace a matsayin mata to ta zama bazawara.
3.2 Mace ta kashe aure
A al’adar Maguzawa, mace tana da ’yancin da za ta rabu da
miji, ta bar gidansa idan ta fahimci ba ta son ci gaba da auren. Ita ma a wasu
lokuta, kafin ta kai ga wannan matakin za ta nemi magabata su ja hankalin miji
a kan wasu ɗabi’u nasa
da take ganin sun saɓa
wa zamantakewa ta aure. Haka kuma yanke wannan shawara zai iya zama sakamako ne
na auren tilas da aka yi mata. Idan ga misali ta fahimci waɗanda suka tilasta mata yin
auren sun kau, kuma har zuwa wannan lokacin ba ta sha’awar ci gaba da zaman
auren, to sai ta bar gidan mijin. Takan koma gidan iyayenta ko kuma gidan wasu
’yan’uwa nata ko ta tare gidan wanda take so, daga baya a tabbatar masa da ita
a matsayin mata bayan an bi wasu ƙa’idoji da al’ada ta shimfiɗa.
3.3 Mutuwar miji
Ba ga Maguzawa kaɗai
ba, a yawancin al’ummomi idan mace ta rasa miji ta hanyar mutuwa, ta zama
bazawara kai tsaye. Sai dai a al’adar Maguzawa, irin wannan mata ba za ta fara
zawarci ba sai bayan wani lokaci na musamman da al’ada ta shata. Haka kuma sai
ta gudanar da wasu al’adu da za su nuna wa jama’a cewa, tana zawarci.
3.4 Iyaye su raba aure
A al’adance, iyaye ko magabata daga ɓangaren miji ko matar aure su ke sasanta
rikici tsakanin ma’aurata. Su ake kai wa koke su bi bahasi don sasantawa. A
lokacin da iyaye suka kasa yin haka saboda sarƙaƙiyar lamarin, sai a ɗauki matakin raba auren.
Haka kuma idan bayan an yi aure, sai miji ko mata suka tsiri wasu halaye da
suka saɓa wa hankali,
to iyaye ko magabata suna iya raba auren. Irin waɗannan
halaye sun haɗa da duk
wani abin kunya da za su sa mutum yin da-na sani kamar sata ko kwartanci ko a
kama matar aure tana lalata da wani da dai sauran su. Idan auren mace ya mutu
ta hanyar yanke shawara daga iyaye na raba aure to ta zama bazawara kuma ta
shiga yanayin zawarci tun daga wannan lokacin.
3.5 ɓacewar
miji
A lokaci da miji ya bar gida na lokaci mai tsawo (shekaru),
matarsa ko matansa za su ci gaba da zama da tunanin yana raye kuma zai bayyana
wata rana. Tsawaitar wannan rashi yakan sa magabata su warware aure musamman ga
matar da ke da sauran ƙuruciya ko sha’awar kasancewa da namiji. Galibi iyayen mace su
kan fara tuntuɓar
iyayen namiji tare da amincewar matar. Tsoron kada ’yar su ta shiga wani hali
na ɓatanci ta ja musu
abin kunya shi kan sa su fara bayar da shawarar raba auren. Daga lokacin da
magabata suka yanke shawarar raba irin wannan aure, to ta zama bazawara, kuma
ta fara zawarci.
BAYYANAR DA ZAWARCI
A wasu lokuta abu ne mawuyaci siffan jikin mace ya iya
bayyanar da kasancewar ta bazawara. Hakan na iya faruwa ne saboda ko da a makon
da budurwa ta tare gida miji suka rabu, ta zama bazawara. A irin wannan
yanayin, halayenta ko ɗabi’unta
da yadda take mu’amala da mutane musamman maza su ke nuna cewa bazawara ce.
Haka kuma al’ada takan haramta mata gudanar da wasu lamurra kamar gaɗa a dandali da sauran
sharholiyar da ’yanmata ko budare ke aiwatarwa. Hatta da yanayin irin mazan da
za a ga bazawara tana mu’amala da su sukan bambanta da na budurwa.
4.1 Hulɗa da Maza
Bazawara takan saki fuska ga maza idan ta kusance su. Irin
wannan sakin fuska ko kaɗan
ba za a same shi ga matar aure ba. Takan riƙa fara’a da ba’a da kuma son tsayawa a yi
zance da maza ba lallai sai da dare ba. Ta haka akan fahimci bazawara ce
musamman ga waɗanda ba
su san ta ba ko ba ƙauye ɗaya
suke ba.
4.2 Cin Kasuwa
Bazawara a muhallin Maguzawa takan yawauta cin kasuwa ko da
ba ta zo sayar da komai ko sayen komai ba. Dalili a nan shi ne, a ranakun
kasuwa ne maza ke taruwa don saye ko sayar da abin da suka kawo kasuwan. Ga
wanda ya sayar da wani abu, yana da ’yan kuɗin
da zai yi toshi ga bazawarar da ya gani ya nuna yana so. Ga bazawarar, wata
dama ce da za ta haɗu
da maza iri-iri da suka taru don cin kasuwa. A irin wannan wuri, ta la’akari da
irin damar da aka ba ta na mu’amala ko sayar da wani abu, akan gane cewa
bazawara ce.
4.3 Samun abin sayarwa
Zawarawa sukan tsiri yin ’yan sana’o’i musamman na ƙwalama.
Wannan kan sa maza su riƙa matsowa kusa da ita har su fahimci bazawara ce ta hanyar
kalamanta ko ɗabi’unta
na ba’a da sakin fuska. Takan fahimci ra’ayin namiji gareta ne idan ya yawaita
sayen abin da take sayarwa.
5.0 MATAKAN AUREN BAZAWARA
Haɗuwa
tsakani wanda ke son aure da wadda ake so shi ne mataki na farko na ƙulla
irin wannan auren. A wurin gudanar da sha’anonin rayuwa a ko’ina bazawara tana
iya haɗuwa da masoyi.
Daga cikin muhimman wuraren da aka fi wannan haɗuwar
akwai kasuwa da wurin buki ko wani sha’ani na taruwar jama’a
Idan bazawara mai farin jini ce tana iya samun manema fiye
da goma. Kowane daga cikinsu zai rinƙa ƙoƙarin samun abin da ya ba ta don jawo
hankali. Wasu daga kasuwar nan za su yi mata cefane iri-iri ta komo gida. Idan
bazawara na son mutum daga kasuwar nan tana iya bin shi zuwa gidansa. Tana ma
iya yin kwana biyu ko uku tare da shi. Daga baya ta kawo shi wajen
iyayenta.[ii]
Bazawara takan ba da dama a zo zance a gidansu. Idan manemi
ya zo zance zai gai da iyayenta, ta shimfiɗa
masa tabarma su yi zance. Haka kuma, yana iya zuwa da rana. Sai dai galibi suna
zuwa da ’yan rakiya saboda gudun rikici. A al’adar neman bazawara a maguzance,
ba lalle ne sai iyayen manemin sun zo ba. Idan an ba shi baki, nan take
iyayenta kan ce, “Ka gaya wa magabata su zo rana kaza a ɗaura aure.” Kafin a kai ga ɗaura aure, iyayenta za su
tambaye ta inda ta samo bazawarin. Idan hankalinsu ya kwanta da shi, sai a ce
mata ta gaya masa ya fito. Idan kuma ba su amince ba, za su ba ta shawara. Sai
dai ba a tilasta mata. In ta ƙi jin shawarar, ruwanta.
Idan ya kasance bazawara tana da manema da yawa, kuma ta karɓi kuɗi ko kayan da yawa daga cikinsu, to ranar da
ta tsayar da ɗaya,
ranar shi wanda aka tsayar zai biya sauran. Haka kuma ranar zai ba ta kuɗin sayayya. Wato ta tanadi
’yan kayan da za ta tare da su. Idan daga cikin manemanta akwai wanda ya ba ta
wani abu ba a biya shi ba, to ba zai ce komai ba sai ranar ɗaurin aure. Sai an fara
shirye-shiryen ɗaura
aure abokansa za su ce, “Kada a ɗaura,
akwai kuɗin Wane.” Za
a tsayar da hidimar ɗaurin
auren a bincika. Idan an tabbatar da haka, to nan take angon ko danginsa za su
biya ko a fasa ɗaura
auren sai ranar da aka biya shi.
A auren bazawara ba a yi wasu hidimomi kamar yadda ake yi a
auren budurwa. Illa dangin amarya da na ango kawai za su halarta, sai kuma waɗansu maƙwabta
da waɗanda ke kusa.
Dangane da kayan ɗaurin
aure, akan zo da toshin uwa da uba da kuɗin
ajiya da dukiyar aure. Haka ma bayan ɗaurin
auren, bazawara tana iya tarewa kai tsaye. Wasu akan sami mata su yi mata
rakiya zuwa gidan miji ta ci gaba da zaman aure.
Bazawara ita ma takan yi auren kissa musamman idan ta ci kuɗin mutane da yawa a lokacin
da take zawarci. Sukan shirya da wannda take so idan ba zai iya biyan kuɗin ba. Sai ya ce ta yi
auren bayan kwana biyu ta tabbatar da ya more ta dawo masa.
6.0 HUKUNCE- HUKUNCEN AUREN BAZAWARA A MAGUZANCE
Maguzawa suna da hukunce-hukuncen da suka tanadar dangane da
abubuwan da kan biyo mutuwar auren mace da sake yin wani auren. Waɗannan ƙa’idoji
sun danganta ne da yanayin rabuwar auren. Haka kuma akwai tanade-tanaden da aka
yi dangane da tsohon miji ko dukiyar aurensa a lokacin da tsohuwar matarsa ta
kashe auren kuma ta tashi yin wani auren.
6.1 Ƙayyade lokacin sake aure
A maguzance babu Idda.[iii] Hausawa sun sami wannan tsari ne
bayan da suka karɓi
addinin musulunci. A al’adar Maguzawa, idan auren mace ya mutu, tana iya ƙulla
wani auren a kowane lokaci ta ga dama. Wato babu wani ƙayyadadjen lokaci da za
ta ɗauka ko dai tana
jiran ta fara zawarci, ko tana zawarci kafin ta yi wani auren. Ba a la’akari da
cewa auren mace na iya mutuwa da shigar cikin tsohon miji. idan bazawara ta yi
aure da cikin tsohon miji, abin da aka Haifa na sabon mijin ne.
6.2 Sauya Miji
Bamagujiya tana da ikon in ta ji ba ta son mijinta, ta bar
gidansa ta koma gidan wanda take so. Illa daga baya a zo a sasanta da tsohon
miji dangane da abin da za a mayar masa na dukiyar aure. Idan sabon mijin ya
kasa biyan dukiyar auren da tsohon miji ya yanke to dole ta haƙura ta
koma gidansa. Idan ya kasance mace tana da cikin tsohon miji, ta koma gidan
sabon miji ta haihu, to abin da aka haifa ya zama mallakar sabon miji.
6.3 Kome
Kome yana nufin mace ta koma gidan tsohon mijinta bayan
aurenta ya mutu. Irin wannan lamari yana faruwa ne bayan mace ta rabu da mijin
farko, ta yi wani auren, sai ta fahimci ba ta gamsu da mijin na biyu ba. A irin
haka ta ga damar ta koma ga mijinta na farko kai tsaye ba tare da wani sharaɗi ba. Sai dai sabon mijin
ya haƙura.
Haka kuma idan ya kasance mace ta yi wani auren ne bisa dalilin ɓacewar mijinta na farko,
sai aka wayi gari ya dawo, to tana iya koma wa mijin na farko ba da wani sharaɗi ba. An nuna wasu matan
sukan koma gidan tsohon mijinsu ne saboda halin da ’ya’yan da ta bari kan
kasance.
6.4 Auren Matar Mamaci
Matan da Bamaguje ya mutu ya bari sukan shiga takaba ne a
ranar da aka share makoki, wato kwanaki bakwai da mutuwarsa. Ita dai takaba ga
maguzawa, zama ne na kaɗaici
da haramcin yin aikace-aikace ko mu’amala da mutane kamar yadda aka saba na
wani ƙayyadadjen
lokaci da mace kan yi bayan miji ya nutu. Adadin watannin da matar mamaci takan
kasance cikin takaba sukan bambanta daga wuri zuwa wuri. Ga misali, Maguzawan
Lezumawa wata biyar sukan yi, kamar yadda su ma na Ƙwanƙi suke
yi. Maguzawan Ƙwanƙi sukan yi wa takabar laƙabi da shiga biyar, (idan za a shiga), ko
wanke biyar (idan lokacin fita ya yi). Maguzawan Gidan Bakwai wata shida suke
yi.
Bayan matan mamaci sun fita takaba, idan akwai masu sauran ƙarfi
ko sha’awar yin aure daga cikinsu, nan take sukan fara zawarci. To sai dai irin
wannan zawarci yana da ƙa’idoji da yawa. Daga cikin waɗannan
ƙa’idoji,
’yan’uwan mijinta da ya mutu su ke da alhakin ɗaura
wa mace aure. Don haka sai wanda suka ga ya dace. Ko da masoya suna da yawa,
sai wanda suka yi shawara suka ga ya cancanta ya auri matar ubansu ko ɗan’uwansu. Haka ma ko da ta
aminta tana son bazawari, in su ba su amince ta aure shi ba, ba yadda za a yi
wannan auren, dole ta haƙura. Iyayen mace na ainihi ba su da damar su sa baki. Idan
dangin mamaci suka bayar da auren matar da ya bari, sai aka wayi gari ta fito
daga gidan wannan mijin, to duk wani lamari nata ya koma ga iyayenta ko
danginta na jini. A wannan lokacin ba ruwan dangin mijinta da ya mutu wajen
tsoma hannu ko sa baki a auren da za ta ƙara yi.
Dangane da mijin da matar mamaci za ta aura bayan ta ƙare
takaba, ba a yarda mutumin da ya haɗa
jini da shi (mamacin), ko maƙwabci ko wani amininsa ya aure ta ba.
Hakan na faruwa ne wai saboda kunya da girmamawa ga mamacin. To sai dai an
yarda dangin mamacin su nemo wani can wanda suka aminta da shi, su ce ya aure
ta musamman don ya kula musu da ƙananan ’ya’yanta idan akwai su. Haka kuma
suna iya haɗa wannan
aure don su sami wanda zai kare mutuncinta ba wanda zai wulaƙantar
da ita ba a matsayinta na matar uba, ko matar ɗan’uwansu.
Idan aka dace da mijin, to za a ɗaura
auren ne a ƙofar
gidan mijinta da ya mutu. A nan za a yi duk al’adun da auren bazawara ya
tanada. Haka ma daga nan za a ɗauke
ta zuwa gidan sabon mijin.
7.0 KAMMALAWA
Wannan nazari ya tabbatar muna da wasu al’adu da
hukunce-hukunce na musamman da suka shafi zawarci da auren Bazawara a tunanin
Maguzawa. Muhimmin abin lura da waɗannan
al’adu shi ne damar da suka ba matan da suka faɗo
a wannan rukuni na darjewa su zaɓi
abin da suka ga ya dace da su musamman da yake ana ganin sun ɗanɗana rayuwar aure, sun san daɗinsa da ɗacinsa. Haka kuma wasu daga
cikin waɗannan al’adu
na auren bazawara, tamkar wata hanya ce na samar wa mace gata da kyakkyawar
rayuwa saɓanin inda ta
fito, ko ɗorewar
ingantacciyar rayuwa ga matar mamaci da abin da ya bari. Haƙiƙa
wannan nazari wani haske ne manazarta na ganin irin saɓanin da ake samu na tunanin ɗan Adam a kan sha’anin
zamantakewa musamman idan an kwatanta da abin da aka wayi gari ana gudanarwa a
alumar Hausawa a yanzu.
8.0 MANAZARTA
Abdullahi, M. (1997), “Yanayi da Tsarin Al’adun Aure a
Birnin Kebbi”, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Usmanu Danfodiyo
Sakkwato.
Abu, M. (1985) “Al’adun Aure da Canje-canjensu a Katsina,”
Kundin Digirin farko (B.A. Hausa), Jami’ar Sakkwato.
Adamu, M. (1976), “The Spread of Hausa Culture in West
Africa 1700 – 1900” Savanna No 5 Vol. 1, A Journal of the Environmental and
Social Sciences. Published at Ahmadu Bello University, Zaria.
Adamu, M. (1977) “The Economics of Culture Among The Hausa
during the Present Millenium A. D.” Culture Seminar Ahmadu Bello University,
Zaria.
Akodu, A. (2001), Arts and Crafts of the Maguzawa and some
Educational Implications. Gaskiya Corporation Limited. Zariya – Nigeria.
Alhassan, H. da Sauransu (1982), Zaman Hausawa (Babu Maɗaba’a).
Anchau, M. D. (1986), “Tasirin Zamani Da Illolinsu Kan
Al’adun Auren Hausawa A Lardin Zazzau, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa),
Jami’ar Sakkwato.
Fletcher, D. C. (1929) “The Kai-na-Fara.” Extract from
Re-assessment Report on ’Yanɗaka
District, Katsina Emirate, Zaria Province. M. P. No K. 8833 National Archives
and Monuments, Kaduna.
Furniss, G. (1999), Poetry, Prose and Popular Culture in
Hausa, Edinburgh University Press, London.
Gennep, A. V. (1960) The Rites of Passage The University of
Chicago Press, USA.
Greenberg, J. (1946) The Influence of Islam on a Sudanese
Religion: Monographs of the American Ethnological Society. J. J. Augustin
Publisher, New York.
Gwarjo, Y. T. da wasu (2005) Aure a Jihar Katsina Hukumar
BincikenTarihi Da Kyautata Al’adu ta Jihar Katsina, Hausa Vocabulary, Oxford
University press, London
Ibrahim, M. S. (1982), “Dangantakar Al’adu da Addini:
Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa”, Kundin Digiri na Biyu (M.A. Hausa),
Jami’ar Bayero, Kano.
Ibrahim, M. S. (1985), Auren Hausawa: Gargajiya Da
Musulunci, Cyclostyled Edition – Hausa Publications Centre – Zaria.
Kado, A. A. (1987), “Kainafara Arnan Birchi”, Kundin Digiri
na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Sakkwato.
Krusius, P. (1915), “Maguzawa” in: Archiu, Anthropologies,
NF Vol. XIV.
Lawal, A. T. (1986), “Al’adun Hausawa Jiya da Yau”, Kundin
Digirin farko (B. A. Hausa) Jami’ar Sakkwato.
Madauci I. da wasu (1968) Hausa customs Northern Nigerian
Publishing Company, Zaria.
Magaji, A. (2002) “Wasu Al’adun Hausawa: Yanaye- yanayensu a
Ƙasar
Katsina.” Kundin digiri na uku (Ph.D Hausa) Ja’mi’ar Bayero, Kano.
Maikano, M. M. (2002), Maguzawan Yari Bori: Tarihinsu Da
Al’adunsu”, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Usmanu Danfodiyo,
Sakkwato.
Malumfashi, A. A. (1987) “Hausa Language Speech Usage Norms:
A Case Study of Maguzawa Society in Malumfashi Area” (B. A. Hausa Project),
Bayero University, Kano.
Mashi, B. U. (2001), “Maguzanci Da Zamananci: Nazari A Kan
Al’adun Maguzawan ɓula
A Gundumar Mashi”, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Usmanu
Danfodiyo, Sakkwato.
Morel, E. D. (1968), Nigeria Its Peoples and Problems, Frank
Cass and Company Limited London.
Nyamwaya, D. and Parkin, D. (1987) Transformation of African
Marriage. Manchester
University Press, United Kingdom.
Ottenberg, P. and Simon (Ed.) (1960), Cultures and Ethics of
Africa, H. Wolff Book Mfg.Co., Inc. U.S.A.
Robinson, D. (2004) Muslim Society in African History Cambridge
Safana, Y. B. (2001), “Maguzawan Lezumawa (Babban Kada)
Gundumar Safana”, Kundin Digiri na farko (B.A. Hausa), Jami’ar Usmanu
Danfodiyo, Sakkwato.
Saulawa, I. A. (1986), “Yanayi da Tsarin Al’adun Aure A Ƙasar
Katsina”. Kundin Digirin farko (B.A. Hausa), Jami’ar Sakkwato.
Sufi, A. H. (2001) “Hanyar Kiran Maguzawa Zuwa Ga Addinin
Musulunci.” Maƙalar da aka gabatar a taron Kwamitin Yaɗa Addinin Musulunci na Jihar Kano.
Temple, C. L. (ed.) (1965), Notes on the Tribes, Provinces,
Emirates and States of the of the Northern Nigeria, Frank Cass and Company
Limited London.
Tremearne, A. J. N. (1913) Hausa Superstitions And Customs. John
Bale, Sons and Danielsson, LTD Oxford.University Press United Kingdom.
Yusuf, A. B. (1986), “Wasannin Maguzawan Ƙasar
Katsina”, Kundin Digirin farko, Jami’ar Sakkwato.
[i] Maguzawa su ne Hausawan da ba Musulmi ba kuma addininsu
da al’adunsu na gargajiya sun yi tasiri a kansu.
[ii] I rin wannan ba a tsammanin saduwa a tsakanin su. Takan
yi haka ne kawai don ta tabbatar masa tana son shi.
[iii] Idda na nufin mace ta yi tsarki na wani lokaci bayan
mutuwar aurenta, kafin ta yi wani auren. Wannan umurni ne na addinin Musulunci
3 Comments
[…] Zawarci Da Auren Bazawara A Maguzance […]
ReplyDelete[…] Zawarci Da Auren Bazawara A Maguzance […]
ReplyDelete[…] Zawarci Da Auren Bazawara A Maguzance […]
ReplyDeleteENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.