NA
FARFESA MU’AZU SA’ADU MUHAMMAD PhD.
SASHIN NAZARIN HARSUNA
NIJERIYA DA KIMIYYAR HARSUNA
JAMI’AR SULE LAMIƊO, KAFIN HAUSA, JIHAR JIGAWA
07030803404
Email:
muazusaadukudan299@gmail. com
Wanda aka gabatar a taron bikin ranar marubuta harshen Hausa ta duniya, wanda Kungiyar Marubuta ta shirya Manpower Development Institute Dutse a garin Dutse, Jihar Jigawa, a ranar Laraba 31/12/2025 da ƙarfe 9: 00 na hantsi, daidai ban ruwan dawaki.
Tsakure
Manufar wannan
bincike shi ne, nazari a kan asalin Bahaushe kuma
wane ne Bahaushe. Farfajiyar Bahaushe ya gudanar da kusan mafi yawan harkoki
na al’adun gargajiya wanda ya gada tun iyaye da kakanni. Hanyoyin da aka
bi don gudanar da wannan bincike, sun haɗa da nazarin wasu bugaggun littattafai, da mujallu, da muƙalu, da
yanar gizo, Dangane da iyaka ko farfajiyar wannan bincike, shi ne, Ƙasar
Hausa. Maƙalar zata kawo bayanai tare da fito da rawar da Masana suke takawa
a fagen gano salsalar Bahaushe. Da farko za a kawo ma’anar Bahaushe da Harshen
Hausa, sauye-sauye da Bahaushe ya gani a rayuwarsa bias wasu dalilai, da tsawon
lokaci ko zamani da ya ɗauka yana mu’amulla wasu baƙin
al’ummomi. Na ɗora
nazarin bisa Ra’in bincike a kan ra’in Alfanun Sassan Al’ummma (Al’adun) wanda
da Harshen Turanci ake kira Functionalism Theory of Culture, saboda bincike ya
kawo irin yadda al’adar Bahaushe ta bai wa sanin asalin abu muhimmanci kusan
kamar na abinci, kamar a wajen bikin aure, da haihuwa, da sana’a, da magani, da
sauransu. Haka kuma za a kalli irin yadda Hausawa kan yi kasuwancin dare a
tsakaninsu a wasu wuraren. Maƙalar zata
kawo jirwayen dare a adabin Bahaushe na baka da rubutacce wato na
zamani, daga ƙarshe sai sakamakon
bincike, da shawarwari sai kammalawa, da manazarta.
1. 0 Gabatarwa:
Da
sunan Allah mai rahama mai jin ƙai, Allah yai daɗin
tsira ga Shugabanmu Annabi Muhammad (S. A. W) da alayensa da Sahabbansa. Maƙasudin wannan takarda shi
ne, yin tsokaci ko taƙaitancan bayani a kan asalin Bahaushe, sannan
kuma wane ne Bahaushe a yau?. Haka kuma wannan takardar zata yi tsokaci a
kan matsayin harshen Hausa a idon Duniya jiya da
yau, da kuma fatan matsayin da zai kai nan gaba, wato ya ƙara ɗaukaka. A zahiri Harshen Hausa wani babban ginshiƙi ne a rayuwar Duniya, sai
dai kuma kash! ana cin moriyarsa ana kushe shi. Bisa wannan dalili ya sa na yi
wa takardata taken Tushiya masomin dawa. Manufa ita ce, a lalubo tushen Bahaushe wato inda Kakanni da iyaye suka fito zuwa wannan
farfajiyar da ‘ya’ya da jikoki suka samu kansu a yau. Masana magabata daban
daban sun yi rubuce- rubuce masu yawa. A inda suka bayyana inda Bahaushe ya
fito da kuma irin rawar da Bahaushe ya taka, sannan kuma suka nuna babu ƙusurwar da ba a cin moriyar
Harshen Hausa a harkar zamantakewa gaba ɗaya ba. A irin tunanina kuma
Bazazzagin tunani, nake ganin ba a yiwa harshen Hausa adalci ba, tun daga kanmu
mu Hausawa da sauran Al’umma masu cin moriyar Harshen.
Yankan hanzari ko in ce
sarbu, bisa al’amarin da ya shafi Bahaushe da Harshen Hausa da Kasar Hausa wasu
abubuwa ne masu shiga cikin juna wato sun zama tamkar hanta da jini ko tsumma
da kwarkwata. Ba a iya rarrabesu wannan yasa suke yiwa juna shigar gizagizai,
to wannan shi ya faru ga wannan takarda. Don haka a yi hakuri a karɓa haka, saboda idan tuwon
amarya ya yi gudaji ba a Magana.
2. 0
Ma’anar Kalmar Hausa
Ma’anar
kalmar Hausa ba ta tsaya ga sunan harshe kaɗai ba, akwai wasu ma’anoni da Hausawa suke danganta
kalmar da su. Akwai wasu masana dake
ganin ita kanta kalmar Hausa tana nufin harshe ko yare kowane iri. Misali, Ba
na jin Hausarsa. Wato ba na jin harshensa ko yarensa.
Adamu
(2021) babban abin da za a tambaya a nan shi ne, wai shin wane ne Bahaushe ?
wannan tambayar tana da ban mamaki, domin ganin cewa babu wata ƙabila da ake tantanmar salsalarta a Nijeriya
irin Bahaushe. Misali idan aka ce Yarbawa an san waɗanda ake nufi. Amma da zarar kace Hausawa sai a fara musu
domin ana ganin yawan gaurayar al’ummomi, da kuma iya yaren Hausa na mutane da
yawa ya sa ba ma za a iya cewa ga Bahaushe wannan tunani ya ƙarfafa bisa nazarin wani mai nazarin Harshe
da ake kira Joseph Greenberg. A turbar nazarin da ya gina, Ya gina babu wata ƙabila Hausawa domin su kansu Hausawa a
wajensu tana nufin yare.
Bayan
wannan kuma kalmar Hausa a wani lokaci tana nufin harshen da Hausawa suke
magana da shi.
A wurin Sakkwatawa kuwa kalmar Hausa tana nufin Ƙasar Sakkwato.
Ibrahim Narambaɗa Tubali a waƙar Sarkin Gobir yana cewa:
Jagora: Tun daga Kaduna har Gusau ƙarewa Hausa,
Amshi: Baban Shamaki Namalam Toron Giwa,
Baban dodo ba tamma da batun banza.
Haka kuma, Bahaushe da kansa yakan ambaci kalmar Hausa
a matsayin nufin azancin magana.
Wannan ya sa ake danganta azancin Magana wurin mutane
biyar, kowanne daga cikin waɗannan
mutane suna da baiwar azancin Magana a harkoki na yau da kullum ta fuskoki
mabambanta:
1. Bafade. (Iya juya Magana nan take)
2. Gardi. (Ƙirƙirar Magana cikin hanzari)
3. Mahauci. (Mayar da martani ga abokin Magana cikin
sauri)
4. Maroƙi. (Iya ajiye Magana da zaɓar kalmomi)
5. Wanzami. (Iya haddace labarai da yin tilawarsu)
3.
0 Sanin asali yasa Karen cin alli:
Bunza
(2019) Binciken gano diddigin tarihin mutane wata matsala ce mai cin rayuwar
masu bincike da waɗanda
ake yiwa binciken a lokacin da ilmi ya bunƙasa kowace al’umma ƙoƙari take ta taskance tarihin asalinta. Wurin da gizo
ke saƙar,
shi ne, babu mai nunin gidansu da hannu hagu, maimakon a yi canjaras da abu
guda, sai a ga kowane bakin wuta da irin nasa hayaƙin a ƙarshe aka kasa rarrabe tatsuniya da tarihi
da tarihihi, da ƙari faɗi,
da kintaci faɗi, da jita-jita hadisin Bamaguje.
Dangane
da asali kuwa, har yanzu ba a tabbatar da asalin kalmar Hausa ba, saboda saɓanin ra’ayoyi da ake samu dangane da asalin inda
Bahaushe ya fito.
Amma
wasu masana sun yi ƙoƙarin bayyana ra’ayinsu game da asalin kalmar Hausa
kamar haka:
i. Akwai Masana masu ra’ayin cewa Bahaushe ya fito daga
arewacin Afrika suka yiwo yamma, waɗannan
mutane ana zaton su ne kakannin Goburawa. Bunza (2023) ko da Goburawa suka zo
sun iske Zamfarawa.
ii. Akwai masana masu ra’ayin Misira, daga cikinsu akwai
Muhammad Hambali Junju cewa: Mutane ne da suka taso daga Misira wanda ya kafa
hujja da cewa Hausawa sun kama da ƙibɗawa
ta fuskar launin fatar jiki da ginin jumla. Wannan ra’ayi ya yi kusa da ra’ayin
Muhammad U. Adamu (2011) ya ce an samo kalmar ne daga sunan Fir’auna Hausal,
wanda yake ganin daga zuriyarsa ne aka samu Hausawa.
iii. Ban da wannan akwai Masana masu ra’ayin Habasha daga
cikinsu akwai Malam Aminu Kano da Yusufu Maitama Sule Ɗanmasanin Kano, waɗanda suka ce asalin Bahaushe ya samo ne daga Ƙasar HABASHA, domin Hausawa daga Habasha
(Ethiopia) suke.
iɓ. Ra’ayi
na ƙarshe
shi ne wanda ake kallonsa kamar tarihihi wato tarihin zuwan Bayajida. Sarkin
Tarihin Daura da Sarkin Ningi Haruna, wanda yace an samo kalmar ne sakamakon
zuwan Bayajidda Daura.
4.
0 WANE NE BAHAUSHE?
4.
1Allah shi kaɗai yasan uwar kwaɗo in
ji masu maganar azanci.
Wannan
dalilin yasa har yanzu ba a tabbatar da tahaƙiƙin asalin Bahaushe ko harshensa ba, amma akwai hasashe da
dama da ake yi game da asalin Bahaushe ko harshen Hausa. Mafi yawan manazarta
suna ganin harshen Hausa ya malalo ne daga Arewa maso gabas daga gurbin da yake
a yanzu, wato Ƙasar
Hausa. To da yake ance rashin jini rashin tsagawa, bisa wannan hujjar ta sa na
lalubo wasu bayanai daga nazarin Manazarta magabata kamar haka :
4.
2 To da yake idan dambu yai yawa ba ya jin mai:
Duk
da haka zamu dubi ƙoƙarrin da wasu masana magabata suka yi ta fuskar lalubo
mana asalin Bahaushe. Ga kaɗan
daga cikinsu.
Malumfashi
(2024) yace babu wata al’ummar da ta faɗo daga sama, babu al’ummar da zaka ce ba halastacciyar
al umma bace tun daga zamanin annabi Adam saboda haka ana bincikar tarihi ne a
duba yadda alumma na duniya suka samu da yadda suka wanzu suka barbazu a doron ƙasa dukkaninmu muna da yaƙini asalin mu daga Annabi Adamu ne da
Hauwa.
Kamar
yadda Bunza (2024) yace: Abu ne mawuyaci a samu cikakken Bahaushe wanda yake
uwa da uba kakanninsa duka Hausawa ne. Dalili kuwa shi ne Farfesa Mahadi Adamu
yace: idan ana son cikakken Bahaushe dole a samu Ubansa, kakansa uban kakansa
kakankasa Bahaushe. Ana iya haƙuri ta ɓangaren
uwa. Bisa lura da samun haka zai yi wahala, sai Bunza yace: in aka samu uwa da
uba da kakanni Hausawane sai a haƙura. A yanzu sanin ko wane ne Bahaushe na sali sai an
yi ƙoƙarin tantancewa, saboda irin cuɗanyar da Hausawa suka yi da wasu ƙabilu wadda ta yi sanadiyar sauyawarsu.
Don haka siffa ko harshe ba ya tabbatar da Bahaushe. Bahaushe ya ɗauki dogo lokaci mai tsawo yana yin mu’amulla da baƙin al’mmu masu yawa daga wasu ɓangarori na Duniya ta fuskar zamantakewa da kasuwanci,
da ƙwadugo/bauta,
da addini, kamar:
Fulani,
zamantakewa Daular Usmaniya Sakkwato, da Barebari kasuwancin kanwa da Buzaye
kasuwancin dabbobi, da dabino, da Nufawa Kasuwanci abinci da Yarabawa cinikin
gwanja (cinikin goro) da Jukunawa da wasu ƙabilu na Afirka masu yawa da wasu daga
Asiya da Nahiyar Turai ciki har da Ƙwarori da Larabawa a lokacin har da Turawa da
Hindiyawa da sauransu.
5.
0 Hausa Mesa uwar haɗiya:
Harshen
Hausa na haɗiye wasu ƙabilu waɗanda
ke maƙwabtaka
da shi, a inda harsunansu na asali sukan sumɓule su ɓace
su koma Hausawa ciki ruwan sanyi sai su koma Hausawa. Ta fuskar Harshe da
al’ada irin su Magana, da abinci, da tufafi a wani lokaci har da muhalli. Gulma
J. (2024 wakilin Blueprint Birnin Kebbi) Yaren Hausa shi ne ya haɗiye kowane harshe musamman ƙananan harsuna dake cakuɗe da Hausawa.
Aujara
da Bunza (2021) sakamakon wannan mu’amulla ta haifar da auratayya da cakuɗuwar al’adu a tsakaninsu da Hausawa, wanda hakan ya yi
sanadiyyar mayar da wasu Hausawa ta fuskar harshe da al’ada duk da cewar hakan
bai hana su iƙirarin
asalinsu ba. Za a iya fahimtar Hausawa ta waɗannan fuskoki:
i. Hausawa ta fuskar muhallin zama. (gari ko yankin da
suke zaune)
ii. Hausawa ta fuskar addini. Yawancinsu musulmi ne ko
maguzawa.
iii. Hausawa ta fuskar halayya da al’ada.
iɓ.
Hausawa ta fuskar asali. Waɗanda suke iƙirarin su Hausawa iyaye da kakanni.
Adamu,
da Bunza da Aujara Don haka a yanzu Bahaushe shi ne mutumin da yake ba shi da
wani harshe sai harshen Hausa, kuma al’adunsa na Hausawa ne, ko da kuwa yana iƙirarin wani asali daban, yana zaune ne a Ƙasar Hausa ko a wajen Ƙasar Hausa. A yanzu kalmar Hausa ta zama
ta harshe ba ta ƙabila ba. Domin kalmar ƙabila, kamar yadda Zarruk da wasunsa
(2009) suka bayyana na nufin:
“... al’umma mai asali ɗaya, da yare ɗaya,
da ƙirar
jiki kusan iri ɗaya,
da al’adu iri ɗaya, da falsafa ko ra’ayin zaman duniya iri ɗaya. Bayan haka cikin al’ummar kowa zai riƙa alfaharin shi ɗan ƙabilar ne. ”
6.
0 Farfajiyar Ƙasar Hausa a jiya:
Adamu
(1970) Ta yi iyaka da Daular Bono daga gabas ta kaɗa tayi arewa har zuwa Filige, ta kaɗa ta yi yamma zuwa yawuri ta dunguri kogin kwara, ta
yi kudu har ƙasar
Gwari zuwa Zazzau, ta yi gabas har ƙasar Bauchi sai da koma ta duguri Borno. Wannan
farfajiya it ace Ƙasar Hausa a da. Aujara () Ƙasar Hausa ta asali tana yankin Afirka ta
Yamma a farfajiyar da ke a Arewacin Nijeriya da kuma Kudancin Jamhuriyar Nijer.
Daga Gabas ta yi iyaka da yankin Mangawa da Badawa a gabas kaɗan da garin Haɗejiya ta Jihar Jigawa, daga Yamma ta yi iyaka da ƙasar Zabarmawa daidai doron Kogin Kwara,
daga Arewa ta yi iyaka da ƙasar Agadas wato yankin Buzaye (Auzinawa) a Kudancin ƙasar Nijer, sannan daga Kudu ta yi iyaka
da ƙasar
Gwari da wasu ƙananan
ƙabilu
da ke Kudancin ƙasar Zazzau (Zariya) a jihar Kaduna.
7.
0 Hausawa A yau.
Mahadi
Adamu yace Bahaushe shi ne wanda a tarihinsa daga Ƙasar Hausa ya tsira ko zriarsa tafuskar
iyaye maza haka kuma wadɗanda
suka shaƙu
da aladun Hausawa sosaisuka riƙe harshe da ɗabiunsu
da ddininsu. Duk da haka tilas a ba da kafa ga Fulani da suke zaune a ƙasar Hausa, cikin yunƙurin tantance Bahaushe ya kyautu a waiwayi
ƙirar
zatinsa da ɗabiunsa domin fayyace Bahaushe gado da kazo-nazo da
maziyarta da maƙwabtan da aka hausantar a ilmance. Bahaushen asali za
a sameshi yana da baƙi sosai irin na jama’ar tsakiyar Sudaniyya. Zubin
kansa na da tsawo da ƙurungun kai da ɗan jemo za asameshi. Waɗannan siffofi na zati da launi idan aka ƙura masu idon nazari za a fitar da
Bahaushe kai tsaye a taron jama’a dake zaune a ƙasarsa.
Malumfashi
(2024BBC Hausa) Asali mutane ba irin siffar da ake yanzu suke da ita ba. Ya ci
gaba dacewa Hausawa sun kasance daga cikin mutanen da suka tsira daga ruwan da
aka tafka a lokacin Annabi Nuhu su ne mutanen da ake kira Omo-kibishi. Inda yace
Daga cikin waɗannan al’umma ne Hausawa aka samo asali shekara 1000
da suka gabata.
Bisa
dalilin faruwar mulkin mallaka da Bahaushe ya tsinci kansa, wannan yanayi ya
haifar da karatun boko shi kuma sai samuwar aikin Gwamnati da na kamfanoni da
masana’antu, da samar kasuwanci iri daban daban. Wannan ya sa Hausawa suka riƙa yiwa juna shigar gizai-gizai da wasu baƙin al’ummomi, wanda ya haifar da wani
sabon zubi na Bahaushe.
Manyan
garuruwan ƙasar
Hausa a yanzu sun haɗa
da Kano da Katsina da Daura da Sakkwato da Kebbi da Zazzau (Zariya) da Gusau da
Haɗejiya da Bauci da Azare (ƙasar Guddiri) a arewacin Nijeriya, da kuma
Damagaran da Maraɗi
da Filinge da Dogon Dutse da Ƙonni a jamhuriyar Nijer.
A
taƙaice
ƙasar
Hausa ta asali, daula ce da ta wanzu a tsakanin daular Barno daga gabas da kuma
daular Songhai daga yamma, ko da yake tarihi ya fi ganin yankin a matsayin
daular birane, inda kowane sarki yake da ikon cin gashin kansa, wato babu wani
shugabanci da ya haɗe
yankin a matsayin dunƙulalliyar daula.
8. 0 Sakamakon Bicike:
Babu shakka gane tsintsar
Bahaushe a yanzu ba ƙaramin aiki ba ne. Haƙiƙa kowa ya
yarda cewa tun daga zamanin maguzanci har zuwa lokacin da addinin Musulunci ya
iso Ƙasar Hausa ya tarar Hausawa suna gudanar da wasu harkokin rayuwar
yau da kullum wasu baƙin al’ummu a Ƙasar Hausa. Don haka wannan
daɗewar da
aka yi ana gudanar da harkokin rayuwa, sai hakan haifar da cakuɗuwar al’ada, haka kuma da
Turawa suka shigo Ƙasar Hausa sai aka ƙara samun
wasu sauye-sauye. Ga ɗan abin
da bincike ya hararo akwai:
Bahaushe na kwarai, wajibi
ne ya yi kishin Harshe da al’adarsa, amma ina a yau ba haka abin yake ba. A bisa gaskiya wasu daga cikin Hausawanmu mu muka fara
wulaƙanta
harshen Hausa, a inda muka ƙyamaci al’adunmu, mu ka yi jifan matacciyar mage da
Bahaushen tunani. A inda muka zaɓi baƙon harshe muka fifita baƙin al’adu, muka rungumi baƙon tunani (abinci, da
magani, da tufafi). Irin wannan wauta da muka yi shi ya ba da dama ga wasu
jama’a ko ƙabilu
har suke tsangwamar Hausawa da Harshen Hausa da Al’adunsu. Ashe ke nan, Hausawa
mu ne masu awaki, muka fara zagin Kura, don haka sauran jama’a ko ƙabilu suka samu damar zagin
harshen Hausa. Alhali kura bata da laifin komai. Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun a waƙarsa ta mubi Al’adunmu na
gargajiya yana cewa:
“sai
ka ga ɗan
Musulmi da wandon yadi guda,
Ga
‘yar shet yasa ga wuya nai,
Ba
hulla ga kai nai,
Aljihu
nai ba tasbaha, sai kwalin sigari.
Kar mu
sake mu mance,
mubi
al’adunmu na gargajiya.
Ɗiya mata waɗanda aɗ ɗiyan musulmi,
su ɗora sayen siket da ‘yar kanti,
suna
ta yawo rariya-rariya,
abin
ga ya bamu kunya.
Shi
kuma Alhaji Adamu Ɗan maraya Jos a waƙarshi ta mu so al’ada yake cewa:
“Kamar
mutum da halayanshi,
sun
kama da al’adunshi,
Kamar
mutum da al’adunshi,
sun
kama da halayenshi.
‘yan
Uwa mu so al’ada,
kowa
ya bar gida kai Malam,
Na
tabbata gida ya barshi.
Na
tuna akwai wasu ‘ya’ya,
idan
kace sannunku,
Sai ka
ji sun ce,
ai
no da hiya Hausa,
Na
tuna akwai wasu ‘ya’ya,
idan
kace kwale se dadani,
Sai ka
ji sun ce,
ai
no da hiya Yaroba.
Na
tuna akwai wasu ‘ya’ya,
idan
ka ce kedun adunma.
Sai ka
ji sun ce,
ai
no da hiya Ibo.
Abin
da su suka ɗauka,
Harshen
Nasara shi yafi na su.
Ba ni
jin Turanci,
Mai
ingilish sam teki wan we.
Kayan
aro abin banza ne,
in
mai abin ya karɓi
abinsa,
to
dole zaka komo naka. ”
9. 0 Shawarwari:
Bahaushe
na cewa: “ba a dafa gawa a tashi ba hawaye” a ƙarshe
sai na fahimci. Tabbas wannan takarda na da fatan alheri da samun kyakkyawar
rayuwa ga al’ummar Hausawa da kuma shi kanshi Harshen Hausa nan gaba. Domin
idan ruwa bai koro gafiya ba, to kuwa hayaƙi
zai korota.
Ban
da wannan kuma, na hararo irin tasku da halin ƙaƙa-ni-ka-yi
da Bahaushe da kuma Harshensa suka tsinci kansu a ciki. Haka kuma, wasu Masana
sun karkasa Bahaushe zuwa gida hudu, kamar haka:
1. Bahaushe na tsatso babu sofane (uwa da uba Hausawa).
2. Bahaushe Barbaran yanyawa (uwa Bahaushiya, uba daban,
ko uba Bahaushe uwa daban).
3. Bahaushe Feƙe kafi ƙaya tsini (uwa da uba ba Hausawa ba).
4. Bahaushe na ara ka yafa ( Waɗanda suke wata Nahiya amma sun rungumi harshen Hausa)
Bahaushe yace: zamani ba
kan ji magani, to yanzu zamani ya zo da wani sauyi na nau’in Bahaushe, shi ne
kamar haka:
Duk wanda ke jin Hausa kuma
yake yin Magana da Harshen Hausa, yana yin al’adun Hausawa yana bugun kirji shi
Bahaushe ne, to wannan Bahaushe ne a yau.
Kishin Harshe wajibi ne:
Da fatan za a fahimce ni,
kar a yi min bahaguwar fahimta. Ba wai nace kar Bahaushe ya ɗauki wani
Harshe ya yi magana da shi ba ne, a’a, abin da nake so in ce, shi ne, ko da
kana amfani da wani Harshe to kar kuskura ka mance da naka harshen, don haka
ina ba ka shawara. Idan har kana da tunani, to ka tsaya ka duba ta sosai.
Ka yi wa shawarar dubi irin na sayen goron tsohuwa, ka juya, ka ƙara
juyawa, sannan zaka fahimce ni.
Bisa
lura da bayanai da suka gabata, ana iya cewa an gani kuma an gamsu. akwai buƙatar a ɗauki matakin fito tare da bayyana asalin Bahaushe da
Harshensa da kuma al’ada. shawarwari waɗanda
ya kamata mu ɗauka su ne:
Ya dace masana masu koyarwa
da wannan Harshe na Hausa mu bai wa juna shawarar neman mafita.
Akwai wasu abubuwa da yawa
da suke buƙatar a fito da su don al’umma su ƙaru.
Akwai buƙatar yaƙar
zuciya, da kuma cire ƙyuya mu zurfafa nazari a
kan abubuwan da suka shafi al’adar Bahaushe.
9. 2 Rashin sani yafi dare
duhu:
Turawan yamma da
‘yankoransu sun shigo da wata guba suna dasa ta a tsakaninmu na kiyayyar juna,
wai da sunan kishin Hausawa. To ka sani za a yi amfani da kai ne a cimma buri,
don a tartsa al’ummarka. Da zarar an cimma buri shi ke nan, saboda haka suka yiwa
wasu Kasashe da wasu al’ummomi, misali, Ruwanda, da Burundi, da Afrika ta
Tsakiya, sannan ga Somaliya, da Libiya, da Sudan da sauransu. Domin haka,
Kungiyar Hausawa zalla guba ce mu gujeta mu kiyayeta domin ba zata haifar mana
da da mai ido ba.
10. 0 Kammalawa:
Ƙarshen tika-tika tik, komai
yai farko, dole ne yai ƙarshe, don haka wannan
tsokaci dangane da bayanai da suka gabata bisa ga asalin Bahaushe tare da gano
muhimmancin Harshen Hausa a rayuwar bil’adama. Duk wasu bayanai game da abin da
ya shafi asalin Bahaushe da Harshen Hausa ya wuce wasa, haƙiƙa wannan
fage ne kandami, ba zai yiwu a taɓo shi duka ba. Amma dai mun
yi abin da zamu iya ta hanyar binciko da nazartar bayanan Masana manazarta da
suka gabata rubutattu da nab aka. Bisa wannan dalili ne, yasa muka Ɗan
tsakuro wani abu daga cikin fage, saboda ko ba a shafa ba maruru ya ɗara
kaluluwa. Dukkan bayanan da muka yi, to ya zo ne a matsayin fitila abin haskawa
da kuma jagora. Bahaushe dai yace; lomar hasafi tafi kaɓakin
tsiya, ƙaramin goro yafi babban dutse, sai a yi haƙuri da
abin da samu. Alhamdu lillahi.
Manazarta
Abubakar A. T. (2015) Ƙamusun
Hausa. Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Adamu U. A (2021) Wai shin Wane ne Bahaushe?
BUK (2006) Ƙamusun
Hausa. Bayero Uniɓersity
Press Kano.
Bargery, G. F. (1993) A Hausa-English Dictionary and
English-Hausa Ɓocabulary. Zaria: Ahmadu Bello Uniɓersity
Press.
Bunza, A. M. (2006) Gadon feɗe al’ada. Tiwel Nigeria
Limited Surulere,
Lagos.
Bunza A. M (2019) Jaridar Aminiya Asalin
Hausawa 1
Bunza (2023) Hira da shi Haske online
T. Ɓ.
Malumfashi (2024) BBC Lodon Sashin Hausa.
Malumfashi (2024) Digital Journalist
Isyaku Muhammad.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.