Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Cin Kudin Haram

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum. Malam, mene ne hukuncin cin kuɗin haram alhali mutum ya san cewa wanda ya ba shi kuɗin ya same su ne ta hanyar haram? Ina yi wa malam fatan alheri.

HUKUNCIN CIN KUƊIN HARAM

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuh.

Idan mutum ya san tabbatacce cewa kuɗin da aka bashi an samo su ne ta hanyar haram, to hukuncin karɓarsu ya danganta da dalilin da aka bashi. Idan an bashi kuɗin ne a matsayin lada, kyauta ko taimako daga dukiyar haram da aka sani, malamai da yawa sun ce ya kamata ya guje musu saboda hakan yana taimakawa wajen cin haram.

Amma idan kuɗin an bashi ne a matsayin biyan haƙƙinsa, kamar albashi, bashin da ake binsa ko kuɗin kayan da ya sayar, to ya halatta ya karɓi haƙƙinsa, domin zunubin haramcin yana kan wanda ya samo kuɗin ta haramtacciyar hanya. Haka kuma idan ba a san tabbas kuɗin haram ba ne, sai dai zato kawai, to ba a haramta karɓarsu saboda zato.

Saboda haka, abinda yafj dacewa ga Mutun shi ne ya nisanci abinda yake da shakku, yaci abinda yake halal kuma mai tsarki, domin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: "Ka bar abin da yake sa ka shiga shakka zuwa abinda baya saka shiga shakka. Allah yasa mudace

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Duk wani jikin da aka ciyar da abincin haram ko ya ginu daga haram, ba zai shiga aljanna ba. wuta ce tafi cancanta (ko mafi dacewa) da shi."

An rawaito makamancin wannan fadi daga sahabai kamar Ka'ab bin Ujrah, Abu Bakr As-Siddik, da Jabir bin Abdullahi (Allah ya yarda da su), kuma Imam Tirmidhi da sauran malaman hadisi sun rawaito shi, inda Albani ya inganta shi. Kalmar "Suhut" (السحت) a cikin hadisin tana nufin dukiya ko abinci na haram (kamar riba, sata, cin hanci, ko zalunci).

An ruwaito Hadisi daga Sahabi Ka'ab bin Ujrah (RA). Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce wa Ka'ab: "Ya Ka'ab bin Ujrah! Sallah garkuwa ce, kuma sadaka tana shafa zunubi, azumi kuma garkuwa ce. Jikin da bai tashi da halal ba, wuta ce ta fi dacewa da shi."

A wani hadisin kuma da ya zo daga Jabir bin Abdillah (RA), Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Ba zai shiga Aljanna ba wani jiki da aka ciyar da haram; wuta ce ta fi dacewa da shi." (Imam Ahmad da Abu Ya'la da Al-Albani sun inganta shi a Sahihul Jami').

Ma'anar Hadisin Ciyar da Haram: Yana nufin cin abinci ko amfani da kuɗin da aka samu ta hanyar da ba ta dace ba a muslunci. Misalai sun haɗa da cin kudin riba, kuɗin sata, da cin hanci, da kudin da aka samu ta hanyar damfara. Wannan gargadi ne mai tsauri ga musulmi kan muhimmancin neman na halak da kuma nisantar haram ko da kaɗan ne.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments