NA
MU’AZU SA’ADU MUHAMMAD
Tsakure
Maƙasudin wannan bincike shi ne ƙoƙarin gano wasu abubuwa game da talauci da yadda yakan shafi ko yin tasiri a rayuwa da ɗabi’un mutane. Duk da yake talauci ba ciwo ba ne, amma yakan yi illa ga harkokin yau da kullum, a wani lokaci har halayen masu fama da matsanancin talauci kan saɓa da na lafiyayyen mutum. Binciken kuma ya nazarci irin yadda Bahaushe yake kallon talauci, da sanadojin dake jawoshi tare da duba illolinsa, da kuma matsayinsa a al’ada. Haka kuma za a harari wasu hanyoyi ko dabarun na kawar da talauci a tsakanin mutane a Bahaushiyar al’ada. Za a kawo fashin baƙin wasu muhimman kalmomi kuma a dubi ma’anar talauci da sanadojin dake jawoshi, da ire-iren sunaye da Bahaushe ya kirashi da su, Hanyoyin da aka bi don gudanar da wannan bincike, sun haɗa da nazarin wasu bugaggun littattafai, da mujallu, da muƙalu, da yanar gizo, Dangane da muhallin bincike, shi ne, Ƙasar Hausa. Don cim ma nasarar wannan nazari, an tsara shi kamar haka: goshin aikin yana ɗauke da gabatarwa, sai kuma ƙirjin aikin yana ƙunshe da; ma’anar talauci a idon masana al’ada. Gangar jikin kuma tana ƙunshe; muhimman bayanai, da fito da matsayin talauci da kuma mutanen da talauci ya shafa wato a mahangar al’ada, da jirwayen talauci a adabin bakan Bahaushe, wanda ya zama kamar wani sinadarin harhaɗa wannan bincike. An kawo sakamakon bincike, da shawarwari sai kammalawa da manazarta.
Keɓaɓɓun kalmomi: ƘADAGI, ƘANI,
MUTUWA
ƘADAGI ƘANIN
MUTUWA: NAZARIN TALAUCI A MAHANGAR ADABI DA AL’ADUN HAUSAWA
1. 0 Gabatarwa:
Babu
shakka motsi yafi laɓewa, wannan yasa za a ɗan harari al’amarin tsananin talauci da raɗaɗinsa a Arewacin Nijeriya,
tare da fito da halayen wasu mutane da suke rayuwa a cikin ƙunci. Bayan
haka kuma, za a gudanar da wannnan bincike ne ta hanyar ɗora shi a mizanin al’ada
don gano inda suka yi canjaras da wasu adabin Bahaushe. Da farko dai Bahaushe
na cewa, komai ba ya rasa dalili, haƙiƙa
Bahaushe na da wani tunani da ya danganta wasu dalilai da suke jawo talauci,
tun a farkon al’amari. Misali: lalaci ko ragwanci, da jahilci, da ƙauyanci.
Mu’azu Haɗeja a waƙar Ilmin
Zamani yana cewa:
Da tsiya da talauci duk
suna,
Gun da jahilci yai sansani.
Bayan waɗannan dalilai kuma, sai
wani dalili shi ne, wanda zamani ya zo da shi wato tsarin shugabanci na siyasa
a inda babakere da wasu mutane ƙalilan
suka yi a harkokin rayuwa, musamman shugabanci inda suka zama bakan gizo,
a ƙarshe kuma sai aka samu wasu mutanen masu kala kusa da tari, wato
masu ƙuruciyar ɓera
(sata).
1.1 MA’ANAR TALAUCI:
Abubakar A. Y. (2015: 475) Tsananin rashin wadata,2. Tsananin
tsiya. (2015: 135) Fatara: rashin kuɗi na ɗan
lokaci. BUK (2006: 423) Rashin Wadata,Tsiyata,Fatara, ƙarancin
Ko Rashin Kuɗi na Wani
Lokaci. Newman (2020: 246) tsiya, ko tsananin rashi.
1. 2 SUNAYEN TALAUCI:
1. Talauci.
2. Tasku.
3. Tsiya.
4. Tsomomuwa.
5. Fatara.
6. Matsi.
7. Ƙunci.
8. Ƙaƙa-ni-kayi.
2. 0 TALAUCI A MAHANGAR
ADABI
An samu jirwayen talauci a
adabin Bahaushe, ma’ana ya yi naso a dukkan rassan adabi na baka da rubutacce.
Domin an samu karin magana, almara, tatsuniya, barkwanci, waƙar baka.
Haka kuma a rubutacce akwai littattafai da aka yi kamar zube, da wasan
kwaikwayo, da rubutacciyar waƙa, kamar matsalon attajiri,
uwar gulma, ka ƙara karatu da sauransu.
2. 1 Zube:
Annoba: Jabiru
(1970: 22) ciwon annoba a Zango, ciwon agana (‘yan rani) ya faɗa wa al’umma a inda Ɗanduna da
Wakkale suka makance wanda dole yasa suka yi hijira zuwa wani gari.
Idan muka waiwayi wannan
littafi na Nagari Nakowa
2. 2 Waƙa: Waƙar Kassu
zurmi waƙar Nomau Na magarya inda yake cewa:
Torankawan tsiya Uban
mairogo,
Idan fatara tai yawa ta zan
iko,
Nomau ko baka jin batun
masu gari?
2. 3 Azancin Magana : TALAUCI A KARIN MAGANA.
1. Talauci kamar ɓeran Masallaci,
2. Talauci kamar jinjiri,
3. Talauci kamar zai rege
zawo.
4. Talauci mai sa a ci iri
ranar shuka.
5. Idan fatara ta yai yawa
takan zan iko.
2. 4 Talauci A Kirari:
1. Talau-Talau Mugun Tsoho, Da
Kasa Mutum Gaba Gara Ya Sa Ka.
2. Lalata Mutum Da Sauran
Ransa
3. Talauci Ka Fi Ciwo Duka.
4. Fatara Mai Kai Maza Kwance
5. Wahala Mai Sa A Lalace
6. Mutuwar Tuji
7. Talauci Kamar Jinjiri
3. 0 TALAUCI A MAHANGAR
AL’ADA
Bisa hasashe a tunanin
Bahaushe yana ganin cewa lallai akwai abubuwa da sukan yi sanadin faɗawa cikin talauci. Da farko
akwai waɗanda mtum
kan jawowa kansa, sakamakon wasu ayyuka waɗanda yakan aikata da kansa. misalilalaci ko ragwanci, da jahilci
da ƙauyanci, da girman kai, Camfi, ko raina sana’a.
Bahaushe ya yi wannan
tunanin ne bisa la’akari da yadda harkoki na rayuwar yau da kullum da kuma
mu’amullar zamantakewa dake wakana tsakanin sauran jama’a, kaɗan daga cikin waɗannan abubuwa sun haɗa da: lalaci ko ragwanci,
da ƙyuya.
3. 1 Ragwanci:
na nufin gazawa, ko kasawa,
ko lalaci. Ragwanci kishiyar jarumta ne. Ana kiran mai wannan hali da cewa
rago, ko malalaci, shi kuma kishiyar jarumi ne, domin rashin jarumta ke haifar
da ragwanci. Da zarar aka ce da mutum ba ya ƙulla
abin ƙwarai, ko kuma malalaci, ba zai iya ƙullawa
kansa komai ba, dukkan malalaci baya cin nasara a rayuwarsa don haka dole ya faɗa cikin talauci.
Hajiya Uwaliya mai amada
tana cewa:
Wane rago da rigar saƙi,
In bai yo aro ba zai yo sata.
Haka shi ma wanda ya sanya
ragwanci, da ƙyuya a zuciyarsa bai yin komai na bajinta domin ya zama rago, a
game da su Bahaushe na cewa: malalaci ba shi da rana.
3. 2 Camfe-Camfe:
Wasu Hausawa sun yi imani
da camfi, kamar sharaɗi mai
kama da addini. Don da zarar an gitta doka, sai a ce wanda ya ƙaryata
zai mutu, ko wani abu mummuna zai same shi. Wannan imani da abin da camfi ya
tsara, wajen harkokin yau da kullum ne ya sanya masana da yawa suka ɗauki camfi wani addini ne
mai zaman kansa. Ko da yake wasu masanan suna da ra’ayin cewar, camfi wani
sashe ne ko ɓangare na
al’ada, don haka basa ware shi daga al’adun garggajiya. Akwai wasu kamar haka:
1. Cin naman gafiya,
2. Ladanci (kiran sallah)
3. Ɗaura ƙonannan
zani ko yagaggen zani,
4. Auren mace mai farar ƙafa,
5. Gamuwa da makaho da
sassafe.
3. 2. 1 Gafiya (Burgu) : Bahaushe
ya camfa gafiya, don haka ko namanta bashi da farin jini. Ko da yake wannan
camfi bai rasa nasaba da wani zargi da ake yiwa gafiya. Wannan zargi kuwa akan
wasu ɗabi’unta
ne, da suka haɗa da
abincinta, da wurin zamanta. Wajen abinci gafiya kan ci komai ta samu. Domin
kuwa gafiya kan shiga kabari ta ci gawa rmutum. Ana ƙyamar
kuma, saboda yanayin wurin zamanta, sau da yawa gafiya kan zauna a wurare kamar
juji, da kabari, da suri da sauransu. Kamar wata waƙa wadda
Alhaji Mamman Shata Katsina ya yi wa Gwamma inda yake cewa:
Gindin
: Gafiyar suri mai wuyar gina,
:
Amma nama da daɗi.
:
Gafiyar juji ba wuyar gina,
:
Ku zubar namanta ɗaci
garai.
Jagora:
Haka nan ne Mamman ƙanin Idi Wan Yalwa.
Muhammad (2015: 152) Camfin
Bahaushe yayi tasiri a kan gafiya, don kuwa an camfa ƙashinta
ko da an kama gafiya an dafa. Idan za’a ci ba ‘a tauna ƙashinta
saboda ana zargin cewa gafiya na da ƙashi iri
biyu. Akwai ƙashin arziki da ƙashin
tsiya duk wanda ya tauna ƙashin to lallai zai yi
tsiya (talauci). Don haka ne Bahaushe ya ƙyamaci
tauna ƙashin, dalili kuwa shi ne ba za’a iya bambance ƙashin
arziki da na tsiyar ba.
3. 3. 2 Girman kai :
Tabbas dukkan mai fama da wannan to lallai yana tattare da ciwon da zai iya
jawo masa talauci. Kamar yadda Bahaushe ke cewa: girman kai rawanin tsiya, don
yakan hanyar arziki. Shi kuwa Alhaji Adamu Ɗanmaraya
Jos a waƙarsa ta girman kai rawanin tsiya sai yace:
Girman kai rawanin tsiya,
Don yakan hana hanyar
arziki,
Tun da Allah Yayi hani a
yi,
Kuma Annabi ya yi hani a
yi,
Don yakan hana hanyar
arziki
4. 0 SANADIN TALAUCI A
MAHANGAR AL’ADA
Bisa hasashe a tunanin
Bahaushe yana ganin cewa lallai akwai abubuwa da sukan yi sanadin faɗawa cikin talauci. Da farko
akwai waɗanda mtum
kan jawowa kansa, sakamakon wasu ayyuka waɗanda yakan aikata da kansa. misalilalaci ko ragwanci, da jahilci
da ƙauyanci, da girman kai, Camfi, ko raina sana’a.
Bahaushe ya yi wannan
tunanin ne bisa la’akari da yadda harkoki na rayuwar yau da kullum da kuma
mu’amullar zamantakewa dake wakana tsakanin sauran jama’a, kaɗan daga cikin waɗannan abubuwa sun haɗa da: lalaci ko ragwanci,
da ƙyuya.
4. 1 Ragwanci: na nufin
gazawa, ko kasawa, ko lalaci. Ragwanci kishiyar jarumta ne. Ana kiran mai
wannan hali da cewa rago, ko malalaci, shi kuma kishiyar jarumi ne, domin
rashin jarumta ke haifar da ragwanci. Da zarar aka ce da mutum ba ya ƙulla
abin ƙwarai, ko kuma malalaci, ba zai iya ƙullawa
kansa komai ba, dukkan malalaci baya cin nasara a rayuwarsa don haka dole ya faɗa cikin talauci.
Hajiya Uwaliya mai amada
tana cewa:
Wane rago da rigar saƙi,
In bai yo aro ba zai yo
sata.
Haka shi ma wanda ya sanya
ragwanci, da ƙyuya a zuciyarsa bai yin komai na bajinta domin ya zama rago, a
game da su Bahaushe na cewa: malalaci ba shi da rana. Alhaji
Adamu Ɗanmaraya Jos a waƙarsa ta mu kori malalaci,
sai yace:
Mu kori malalaci,
Mu zagi malalaci,
Wofi mutumin banza,
Wanda bai sana’ar komai
4. 2 Jahilci: Idan
muka koma ta fuskar jahilci shi ma yana jefa mutum cikin talauci saboda matuƙar aka ce
mutum bai san komai ba to lallai yana cikin duhu, to kuwa dole ne ya rayu
cikin ƙunci kamar yadda Mu’azu Haɗeja a waƙar Ilmin Zamani yana cewa:
Da tsiya da talauci duk
suna,
Gun da jahilci yai sansani.
Duk wanda yake ba ya shiga
jama’a don yin ma’amalla to babu mamaki ya faɗa cikin talauci da ƙuncin
rayuwa.
4. 3 Aikin Gwamnati: Bayan waɗannan kuma an samu baƙin
dalilai da suka yi sanadin faɗawa
talauci shi ne, karatu ko ilmin zamani, wani bahagon tunani da wasu ke da shi,
shi ne, duk wanda yayi ilmin boko to dole sai ya samu aikin Gwamnati.
Ɗangambo
(1984: 3) Wannan tunani ya kashe zukatan matasanmu da yawa, sun ƙi sana’a,
saboda sun raina ta kuma aikin bai samu ba, dole sai zaman kashe wando, wanda
yake ɗakinsu ɗaya da talauci.
Abdullahi (1993) cewa ya
yi: Ma’aikaci ɗan
albashi ko na Gwamnati, ko kamfani ko masana’anta, da shi da bashi ɗan wa ne da ɗan ƙani.
Domin duk yadda zaka yi baka raba su da bashi. Ga wani kirarin Ɗan
albashi:
Ɗan albashi mai taƙama da
bashi,
Ka yi aiki a bashi,
A baka albashi ka biya bashi,
Ka ƙara cin bashi kafin wani
albashin. [1]
4. 4 Siyasa: Shigowar
siyasa shi ma ya ƙara ingiza mutanenmu a talauci, dalili kuwa shi ne ya kashe wa
wasu zuciya da son a ci bulus ko cin banza, da yawon maula ko garam. Da yawa
wasu sun watsar da sana’o’i, sun kama gaibu wai su kan su ya waye.
4. 5 Babba da jaka: Usman
(2023) wato babakere da wasu ƙalilan
suka yi a harkokin rayuwa,idan Gwamnati ta ƙirƙiro wani
shiri na tallafawa talakawa masu ƙaramin ƙarfi, ko
don a rage masu raɗaɗin talauci sai su handame,
anan sai suka zama kamar bakan gizo, a ƙarshe
kuma sai aka samu wasu masu yin kala kusa da tari, wato masu wawure dukiyar
Hukuma. [2]
5. 0 ILLOLIN TALAUCI
Bahaushe kan yiwa talauci
kirari da cewa: “Talau-talau mugun tsoho, ƙadagi ƙanin
mutuwa, lalata mutum da sauran ransa”. Wannan
kirari na talauci gaskiya ne, saboda talauci kan yi tasiri ga rayuwar Ɗan adam,
ta kowacce fuska. Rayuwar ma gaba ɗaya takan samu dabaibayi ko tarnaƙi a kasa
sukuni da walwala a cikin al’umma. Talauci kan yi tasiri matuƙar aka ce
ya shafi mutum, to sai kuwa an ga alama. A kan wannan hujja ce ya sanya duk
mutumin da ya tsinci kansa a cikin talauci ko kuma ya faɗa masa, yake shiga wani
hali na gaba damusa baya siyaki. Mafi yawa mutane matalauta ke galabaita fiye
da tsararrakinsu da suke da wadata. Wannan kuwa na bayyana ne tun daga ɗabi’unsu, da tunaninsu, da
kamannunsu, kai hatta yanayin fatar jikinsu kan bambanta da sauran jama’a.
Shi kuwa Baba mai gyaɗa Agege marubucin waƙoƙin Hausa
a waƙar ‘Yan Duniya cewa yayi: -
“Idan baka da dukiya, a yau an raina ka,
Sa’o’in ‘ya’yanka, Su sukan riƙa taka
ka.
Idan kai Magana, Su ce wane fa yana hauka.
Da ka yi shiru sai suce fa Wane bai cika fara’a ba. ”
Tabbas talauci kan haifar
da illoli masu yawa waɗanda suka
shafi mutum wato shi kansa matalaucin da kuma al’umma kai hatta da muhallinsa.
Bisa lura da bayanai da suka gabata, ana iya cewa talauci na cutar da ko jawo
illa ga rayuwar matalauci ko ya sani ko bai sani ba. Da farko talauci na haifar
masa da wasu abubuwa takwas.
1. Baƙin jini
ko rashin kwarjini,
2. Ƙyama,
3. Kyara,
4. Tsangwama.
5. Tauye tunani da hazaƙa na
harkokin duniya da na mu’alla da jama’a.
6. Talauci na yanke
zumunta,
7. Yana hana samun walwala,
don yana tauye matalauci ya tsangwami kansa a inda zai riƙa ɗari-ɗari da jama’a.
8. Sanya zargi.
Bayan ga illolin da suka
shafi matalauci shi kaɗai, to
haka kuma akwai illolin da suka shafi al’ummar da yake cikinsu. Da farko dai
talauci na haifar da ƙiyayya ko gaba a tsakanin
mawadata musamman marowata da talakawa mabuƙata.
Wannan na haifar da mummunar alaƙar
zamantakewa,
6. 0 HANYOYIN MAGANCE TALAUCI A BAHAUSHIYAR AL’ADA
Akwai wasu hanyoyi ko dabaru waɗanda Bahaushe ya ƙirƙirar wa
kansa waɗanda suke
magance talauci. Dabara ta farko ita ce sana’a, haƙiƙa
Bahaushe ya gaji sana’o’i masu yawa tun iyaye da kakanni. Baya waɗannan sana’o’i kuma akwai
wasu hanyoyin taimakekeniya, kamar su gudumowa da tafiye-tafiye.
6. 1 SANA’A
6. 2 MUHIMMANCI SANA’A A BAKIN MAWAƘA.
Muhimmancin sana’a ya bayyana a bakin mawaƙan baka
na Hausa da yawa, wasu sun yi waƙoƙin kai
tsaye wasu kuma sun yi a kaikaice.
Alhaji Sani Aliyu Ɗandawo a
waƙarsa ta
Mutane a kama sana’o’i yace:
Mutane a kama sana’o’i,
A mai da hankali wajen noma.
Abdu Minjibir a waƙarsa ta Mu kama sana’a ‘yan
Najeriya,Yace:
Mu kama sana’a ‘yan
Najeriya,
zaman banza ba namu ne ba.
Sai kaga kanti na yawo a
titi
ba asali ba tattali ba.
Mu kama sana’a ya fi kyau
tunda ya fi zama na lido da
karta.
Zamanin nan wanda muke ciki
babu banza sai mara yin
sana’a.
Alhaji Mamman Shata Katsina
a waƙarsata Kai ‘yan yara gumina nake ci,
Yace:
Kai ‘yan yara gumina nake
ci,
masu zuwa tebur su yi tebur
lebura kan hanya ku yi aiki
a yau kowane guminai yake
ci.
Masu tireda nata tireda
su leƙa nangun
su leƙa can gun
wannan gumunsu suke ci.
Alhaji Adamu Ɗanmaraya
a waƙarsa wofi mutumin banza ya ce:
wofi mutumin banza,
Wanda bai sana’ar komai,
Ga sana’ar fawa ita ma
sana’a ce ai,
Ga turin kura,
ga yankan farce ita ma
sana’a ce ai.
Alhaji Musa Ɗanƙwairo
Maradun a waƙarsa ta Noma babbar sana’a
Ya ce:
Noma babbar sana’a
koway yita ya bar rasawa
taimaki bayinka Allah,
Allah kai an mai iyawa.
Alhaji Musa Ɗanƙwairo
Maradun a waƙarsa ta Sarkin Muri
Ya ce:
Mai sana’a in dai akwai
riba
sai ka riƙeta ba
illa ne ba,
mai sana’a in baya cin
riba,
shi ma riƙeta ba
ririyal ne ba.
Hajiya Barmani Choge a waƙarta ta
sakarai bata da wayo. ta ce:
Mata ku kama sana’a,
sakarai bata da wayo.
Duk wanda ba ta sana’a,
ta bani ta lalace.
Hajiya Barmani Choge a waƙarta
ta Mai soso ke wanka. ta ce:
Mai soso ke wanka,
Duk wadda ba ta da shi sai
ta ara,
Duk matar da bata sana’a
aura ce.
7. 0 Sakamakon Bincike:
Babu shakka talauci a arewa
ya zama ƙarda baƙon dole ana ba wuri yana kafa ɗaki ko kuma ana murna baƙo ya tafi
ashe baƙo na bayan gari. Bisa zahiri kowa ya yarda cewa an ɗauki dogon zamani ana
gudanar da rayuwa cikin baƙin talauci a Ƙasar
Hausa. Tarihi ya nuna cewa tun ana amfani da wuri a matsayin kuɗi gabanin bunƙasar
samun tsabar kuɗi da
takardun kuɗi da
zamani ya kawo Ƙasar Hausa. Haka kuma, a wancan lokaci ba a Ƙasar
Hausa kaɗai aka yi
fama da talauci ba, har da wasu sassan Afrika. Shigowar ilmin zamani, tare da
kwaɗayin
samun aikin Gwamnati sun bayar da gaggarumar gudummowa ga mutuwar zuci da raina
sana’a tare da zaman kashe wando a Ƙasar
Hausa. Ga ɗan abin
da bincike ya hararo akwai:
1. Tabbacin
cewa, binciken ya fito da wasu tunane-tunanen Bahaushe, game da talauci a
fagage masu yawa.
2. Haka kuma
binciken ya nuna talauci a matsayin wata tsohuwar Magana ce wadda take ta yi
tasiri matuƙa a al’adar Bahaushe.
3. Binciken
ya bayyana cewa talauci gyare tsohon nama ne don kuwa babu wanda ya san lokaci
da aka fara talauci ko kuma mutumin da ya fara faɗawa talauci.
4. Bahaushe
ya ba talauci mahimmanci shi yasa yake jefa shi a maganganun hikimarsa, a inda
ya yi tasiri kuma har yanzu ake samun jirwaye ko nasonsa a dukkan rassan adabin
baka.
5. Bahaushe
na cewa ko ba a shafa ba maruru ya ɗara kaluluwa, ma’ana irin dabaru ko hanyoyin magance talauci, da
suna samun tallafi daga Hukuma lallai da sun taimaka wa Ƙasar
Hausa wajen rage talauci.
8. 0
Kammalawa
A ƙarshe,
wannan Bincike ya nazarci tare da kawo bayani game da talauci da irin yadda
Bahaushe yake kallon rayuwa da talauci, da sanadoji ko dalilai da suke jawoshi
tare da fayyace illolinsa, da kuma matsayinsa a al’ada. Haka kuma an nuna wasu
hanyoyi ko dabarun na kawar da talauci a tsakanin mutane. Sannan kuma an kawo
fashin baƙin wasu muhimman kalmomi kuma da ma’anar talauci da sanadojin dake
jawoshi, da ire-iren sunaye da Bahaushe ya kirashi da su. A ƙarshe
kuma, an samar da wani abin nazari. Wanda zai kasance kamar wata taska ce,
wadda za ta zama wuri da aka adana bayanai da suka shafi talauci. Sannan kuma
wannan ajiya ta zama wani abu da zai amfani manazarta zuwa nan gaba.
9. 0 Shawarwari.
Dangane da shawarwari waɗanda ya kamata mu ɗauka su ne:
Bisa lura da bayanai da
suka gabata, ana iya cewa an gani kuma an gamsu. talauci wani aiki ne ko ɗabi’a mai matuƙar tasiri
ga rayuwar Hausawa, saboda haka akwai buƙatar
masana su ɗauki
matakin fito tare da bayyana matsayinsa a al’ada.
Ya dace masana masu
koyar da wannan Harshe na Hausa mu bai wa juna shawarar neman mafita. Musamman
a kan irin waɗannan
abubuwa da ake da ƙarancin bayanai ko rubuce-rubuce game da su.
Akwai wasu abubuwa da yawa
da suke buƙatar a fito da su don al’umma su ƙaru, kuma
al’umma masu zuwa zasu yi alfari.
Akwai buƙatar yaƙar
zuciya, da kuma cire ƙyuya mu zurfafa nazari a
kan abubuwan da suka shafi al’adar Bahaushe. Mu daina raina ƙanƙantar
abin da za a riƙa yin bincike akansa, ɗan abin da Allah Ya sa ka fito da shi, sai wani ya faɗaɗa tare da zurfafawa.
10. 0 MANAZARTA.
Abraham, R. C.
(1947) Dictionary of the Hausa Language London Hodder &
Stoughton.
Bargery, G. F.
(1993) A Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary Ahmadu
Bello University Zaria.
Bunza, A. M. (2006) “Gadon Feɗe Al’ada”, Lagos
Tiwel Nigeria Limited.
Bunza, A. M. (2009) “Narambaɗa” Lagos
Ibrash Islamic Publication Centre Limited.
Bunza, A. M. (2014) “Wauta A Tunanin Bahaushe” Maƙala da
aka gabatar a Jami’ar Umaru ‘Yar’adua, Katsina.
Ɗan Gambo
A. (1983) Kitsen Rogo. Triumph Publication Kano.
Ɗangambo
A. (1984) Rabe-Raben adabin Hausa da Muhimmancinsa garayuwar Hausawa. Triunph
Publication Kano.
Daura S A (1970) Tauraruwar
Hamada. Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Garba, M. (1998) Azancin
Magana a Waƙoƙin Makaɗan Baka.
M. A. Hausa.
Bayero University
Kano.
Gusau, S. M. (1996) Makaɗan da Mawaƙan Hausa
Fisbas Media Service Kaduna.
Imam A. (1973) Ruwan Bagaja
Northern Nigerian Publication Company, Zaria.
Imam A. (1973) Magana Jari
ce Littafi Na 2, Northern Nigerian Publication Company, Zaria.
Jabiru A
(1970) Nagari Na kowa Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Ƙamusun
Hausa (2006) C. N. H. N. Jami’ar Bayaro Kano.
Katsina M. S (1960) Uwar
Gulma. Northern Nigerian Publication Company, Zaria.
Wushishi, B. J. (1998)
Adabin Baka sigoginsa a Hikimominsa. M. A. Hausa
Bayero University
Kano.
[1] Abdullahi Mustapha (1993) hira da shi a
gidansa layin Bashama tudun wada Kaduna.
[2] Usman Babangida Haɗejia (2023) A shirin
Fitilar Rayuwa Rediyon Sawaba F.M Haɗejia.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.