Ticker

6/recent/ticker-posts

Sabalikita Mijin Hajiya (Sunbulallen Uba): Tsokaci A Kan Dabi’un Wasu Mazaje Game Da Harkar Gidajensu

DA AKA GABATAR A KWALEJIN HARSHEN LARABCI DA NA ADDININ MUSULUNCI SHABAB DA KE UNGUWAR DOSA KADUNA, 25 AFRILU, 2014

SAƁALIKITA MIJIN HAJIYA (SUNƁULALLEN UBA): TSOKACI A KAN ƊABI’UN WASU MAZAJE GAME DA HARKAR GIDAJENSU

DAGA:

MU’AZU SA’ADU KUDAN

JAMI’AR JIHAR JIGAWA KAFIN HAUSA

07030803404

SHIMFIƊA

WANE NE SAƁALIKITA?

Saɓalikita, na nufin sunɓulallen mutum, wanda bai iya ƙullawa kansa komai, ko da shawara ce, bai iya yankewa. Watau ba shi da ra’ayin kansa. Rayuwarsa ana kiranta da saɓulanci. Domin haka ne ake ganin duk wanda bai iya ɗaura wando a daidai ba, shi ake kira da saɓalikita. Wannan yasa ake kiran sakin wando ƙasa-ƙasa ko saɓule wando ƙasan ɗuwawu da samari ke yi ake cewa saɓulanci. Haka kuma a kan kira rago, ko matsoraci da sunɓulalle. Macen da ba ta iya ɗaura zani ba, ko iya girki ba, akan ce ma ta sunɓulalliya. Ana jam’in su kuma sunɓulallu.

MIJI:

Miji na nufin mutum cikakke mai aure, watau magidanci. Wannan zai iya yiwuwa mace ɗaya, ko biyu, ko uku, ko huɗu. Mutum bai zama cikakken miji har, sai ya zama jarumi, kuma tsayayye wanda ya tsare dukkan buƙatu da larurorin matarsa da na ‘ya’yansa. Dole ne ya kasance bai da tsoro ko shakka, ba ya karaya ko nuna kasawa a dukkan al’amurran rayuwa.

HAJIYA:

Hajiya, na nufin matar da ta tafi makka aikin hajji, amma akan kira matar mutum wadda yake aure da hakan. Wannan suna, ana amfani da shi ne a matsayin kinaya, don a ɓoye sunanta tare da girmamawa. Domin ko ba ta je makka ba (Hajji) , akan kirata da hakan. A zamanin da a kan ce mijin tace, duk dai ana sakaya sunan matar ne.

MATSAYIN UBA:

Bisa rayuwa ta haƙiƙa, dukkan magidancin da ya haihu, to ya zama uba. Bisa wannan dalili yasa dole ya ɗauki wani nauyi wanda al’ada da shari’a suka ɗora masa. Watau na kula da ‘ya’yansa manya da ƙanana. Matuƙar aka ce uba ya kasa tsare haƙƙoƙin iyalinsa, wanda ya haɗa ne tun daga matarsa, watau uwar ‘ya’yansa da kuma su kansu ‘ya’yan. Matuƙar aka kuskure uba ya gaza sauke wannan nauyi, har ya bar wa wani balle a ce matarsa. Tabbas ya zama sunɓulallen uba.

GABATARWA.

Da Sunan Allah Mai rahama Mai jinƙa, Mai kowa, Mai komai, Mai aikata abin da Ya so, ga wanda Ya so, a yadda Ya so, a sadda Ya so, kuma a inda Ya so, ko ana so, ko ba a so, dole bayi su so. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban halittu Annabi Muhammadu, da Alayensa, da Sahabbansa, da sauran mabiyansa gaba ɗaya.

Wannan muƙala, za ta ɗan taɓo, ko tsakuro wasu daga cikin ɗabi’un wasu mazajen aure. Waɗanda Bahaushe ke ƙyama gaba ɗaya. Idan aka dubesu ta mahanga al’ada, sun saɓawa matsayin da ake so cikakken magidanci ya kai. Haka kuma in aka dubesu ta mahangar addinin Musulunci, a nan ma, sun saɓa wa shari’ar Musulunci. A irin yadda ake so magidanci ya jagoranci al’amuran gida. Bayan haka kuma, ko a hankalce abin ya saɓa wa lafiyayyen hankali. Wannan muƙala, na nufin ta fito da wasu daga cikin waɗannan da kan sanya magidanci ya zama mijin Hajiya. Bayan wannan, za a kawo illoli da suke biyo bayan hakan. Kasancewar wannan ɗabi’a, tsohuwar ɗabi’a ce, ta zama “Gyare tsohon nama, yaro in baka ci ba, tsohonka ya ci”. Wannan ya sanya harkar mjin Hajiya ta yi naso har a adabin Bahaushe na baka da rubutacce. Duk da haka, wannan tasiri da ta yi bai hana Bahaushe ƙyamar mijin Hajiya ba.

Wannan dalili ne, yasa na kira muƙalar da sunan “Saɓalikita Mijin Hajiya. Kuma Sunɓulallen Uba”. Bayan haka, wannan muƙalar riga ce ba wuya. Duk wanda ya huda yasa, to ya zama mijin Hajiya.

HATTARA DAI MAGIDANTA!

Ina kira ga dukkan magidanci, watau wanda yake da aure. Da cewa, ya yi hattara da al’amarin mace, saboda al’amarin mace, yana da wuya. Haka kuma mace sai Allah, Wanda Shi Ya halicce ta. Bahaushe kan yi ma mace kirari kamar haka: “Mace mai sa ka ci rance, ta cinye ta mance, tun ba ka biya rancen ba”. Bayan wannan kuma, yakan ce: “Mata na inna dangin shaiɗan, in baku ba gida, in kun yi yawa gida ya ɓaci”. Haka kuma Bahaushe ya ce, ba a baiwa abubuwa uku amana, su ne mace, da kogi, da doki. Dalili kuwa shi ne, mace ba ta da tabbas komai daɗewarku da ita, kuma ko me ka yi mata, wata rana sai ta butsare ta ce me ka taɓa yi min? Haka shi ma kogi, kana iya wuce shi lafiya lau, amma kafin ka dawo, sai ka tarar ya cika, baƙon ruwa (Kwazari) ya zo, ka kasa wucewa. Game da doki shi ma, komai ɗadewarku da shi, haka kawai wata rana, sai ya abauce maka ya ƙi sarrafuwa, dole ka ƙyale shi.

Ya kai magidanci, waɗannan bayanai a sarari suke, kuma a bayyane. Don haka, ina kira gare ka da ni kaina da sauran magidanta da cewa, hattara dai dangin warki.

Da farko, a fahimce ni, kar a yi min bahaguwar fahimta. Ba wai nace kar magidanci ya ɗauki shawarar matarsa ba ne, a’a, abin da nake so in ce, shi ne, ko da mace ta ba ka shawara, to ka tsaya ka duba ta sosai. Ka yi ma ta dubi irin na sayen goron tsohuwa, ka juya, ka ƙara juyawa, sannan ka aiwatar. Idan kuwa ka ga matsala a ciki, to ka watsar. Bahaushe ya ce, shawarar mace guda uku ne, ba a ƙin ɗauka: -

In tace tsaya ka ci aninci, to tsaya.

Ko tace zo ka yi wanka.

Kai yaro makaranta, to ka kai shi.

Dalili kuwa, a mafi yawan lokuta daga ɗaukar shawararsu ake faɗawa cikin tarkon zama mijin Hajiya.

Bugu da ƙari, wannan haɗarin bai ƙyale duk wani namiji mai aure ba. Domin kamar yadda Bahaushe ya rarrabasu, kowanne an bashi suna daban-daban kamar haka: -

Mai tsayuwar gauraka, ko mai langa (Mai mace ɗaya).

Mai ƙafar kaza (Mai mata biyu).

Mai murhu (Mai mata uku).

Mai ƙafar doki (Mai mata huɗu).

Dukkan waɗannan, ma’aurata ba wanda ya tsira daga faɗawa, ko zama mijin Hajiya. A wani lokaci mai mace ɗaya kan zama mijin Hajiya, amma mata biyu kan fi zama mijin Hajiya. A dalilin karkata da yayi wuri ɗaya, ko uwar gida, ko kuma ita amarya da tazo daga baya. A kan rinƙa juya shi kamar ƙosai a man gyaɗa. Wani mai mata ukun, shi ma akan same shi a cikin irin hakan. A wani lokaci uwar gida ke jan ragamar gida, ko kwarin tsakiya, ko amarya. Haka shi ma mai mata huɗu, akan samu wani ya faɗa cikin wannan hali. A wani lokaci uwargida, ko kwari, ko kwarin tsakiya ko amarya ita ke mulki.

HAƊARINSA A SHARI’AR MUSULUNCI.

Akwai babban haɗari, magidanci ya zama mijin Hajiya a shari’ar Musulunci. Domin a shari’a, ana ƙyamar magidanci ya saki nauyin ko ya wulaƙantar da haƙƙin da Allah Ya ɗora masa. A Ƙur’ani, Allah Ya ce: “Arrijalu Ƙawwamuna Alan Nisa’i”. Lallai maza na gaba da mata, don haka su ne shugabanni. Kamar yadda wani hadisi ya nuna Manzon Allah (S. A. W) ya ce: “Dukkan al’ummar da suka baiwa mace shugabanci, ba za su taɓa cin nasara ba”. A nan, malamai suka ce al’umma na farawa daga gida ne, saboda lallai ne duk wanda ya zama mijin Hajiya, ba zai ci nasara ba.

Bayan haka, a harkokin addini gaba ɗaya, namiji shi aka sani da jagoranci. Domin haka, duk wanda ya sanya tsarin ta hanyar bai wa mace jagoranci, to ya saɓa. Haƙƙin ciyarwa da shayarwa, da tufatarwa, da mahallin zama, duk yana kan maigida ne, ko da mace na da dukiya, ba a ɗora ciyarwa a kanta ba, sai dai shi miji ya ciyar da ita. Banda wannan, saki da sadaki, da izinin fita, duk suna hannun miji, wajibi ne ya tsare su. Wanda duk ya kasa, to ya zama mijin Hajiya.

Akwai inda darajar ta ƙara bayyana a sarari, kamar wajen bashi kaso biyu in aka zo rabon gado. Haka kuma inda aka ce aljannar mace tana ƙarƙashin dugadugin mijinta. Sannan ko azumin nafila za ta yi, sai ta sanar da shi, ko ta nemi izini. Haka kuma ga limanci da bayar da aure, zuwa jana’iza da sauransu, dukkansu namiji ne ake so ya jagoranci harkar.

To don Allah, ya kai bawan Allah, wace irin wauta ce za ta saka ka yi watsi da irin waɗannan darajoji da Allah Ya baka ka bar wa mace? Haƙiƙa mijin hajiya ya yi watsi da darajojin nan, saboda ya baiwa mace jagorancin gidansa. Wannan, ba ƙaramin haɗari ba ne, saboda ba zai tsaya a kansa ba shi kaɗai, sai ya shafi sauran al’umma kamar wata waƙa da Alhaji Aƙilu Aliyu ya yi wa Ɗandaudu, inda yake cewa: -

“Da falle biyu ce daraja tasa,

Ya watsar ya riƙe falle ɗai.

Ga wani ya bar gaba domin baya,

Ya ɓatawa mazaje suna.”

Duk da yake da Ɗandaudu ake yin magana a waɗannan baitotci. To kuma ya yi daidai da mijin hajiya.

YA WUCE WAI, BAI ZAN WAIWAI BA.

Tabbas, harkar mijin ta ce, ko mijin hajiya, wani al’amari ne daɗaɗɗe, wanda ba yanzu aka fara ba. Ana iya cewa wannan al’amari an gaje shi ne tun iyaye da kakanni. Bisa wani nazarin adabin Bahaushe nabaka, da rubutacce da aka yi, yana iya zama hujja ko madogara akan haka.

Idan muka dubi adabin bakan Bahaushe, akwai wasu daga cikin rassansa da aka samu jirwayen mijin tace. Misali, wasu almarori guda uku sanannu a Ƙasar Hausa, waɗanda suka tabbatar da samuwar ko faruwar wannan al’amari. Kamar almarar mai ɗebo tsamiya.

“Wani manomi ne zai tafi zuwa gona, sai matarsa tace in zaka dawo ka ɗebo mana tsamiya, shi kuma sai ya ce ba zai ɗebo ba. Ita kuma sai ta ce to ka dawo, zuwa can sai ya ce to in na ɗebo ba zan ɓare ba. ”

Almara ta biyu kuwa, ita ce, almarar malami.

“Wani malami ne yana bayar da karatu a azure ga almajirai da yawa. Zuwa can sai matarsa ta aiko a ce ana kira a cikin gida. Ko da aka faɗa masa, sai ya ce, ku je ku ce ba zan zo ba. Bayan yaran sun tafi, jimawa kaɗan, sai malam ya ce bari mu gani in bi yaran nan cikin gida, ko sun faɗa cewa ban zuwa?

Almara ta uku kuwa:

“Wani sarki ne yana zaune a fada ana fadanci, sai ga jakadiya ta zo kusa da kunnensa ta ce uwar gida na kira. Maimakon sarki ya yi Magana, sai kawai ya girgiza kai da nufin cewa ba za a je ba. Jakadiya ta koma cikin gida ta faɗa, ba a daɗe ba, sai jakadiya ta ƙara dawowa. Ai sarki na ganinta, sai ya yi wuf ya tashi, kamar zai buge ta, ita kuma da ta ga haka, sai ta ruga da gudu. Sarki ya bi ta kamar ya yi fushi, ashe ya tafi wurin kiran nan na farko ne da matar ta aiko, amma sai ya yi barazanar zai bugi jakadiya. ”

Dangane da karin magana, da kirari, da maganar azanci, ana iya cewa dukkansu an samu jirwayen mijin tace a cikinsu. Misali kamar haka: -

Mijin tace.

Mijin Hajiya Mijin banza/in ba kuɗi ba aiki.

Bita zaizai.

Sauyar sala.

Santilaɓi.

Soloɓiyo.

Je ka ka dawo.

Gaso rogo a baka ɓawo.

Za ta unguwa.

Ta more miji.

Gwamma talla da biko.

Bautar mata kowa da irin tasa.

Ana tsoronka kana tsoron hajiya.

Bari in tambayota.

Bayan wannan kuma, in muka kalli rubutaccen adabi, ko muce adabin zamani. Akwai littattafan zube, da na wasan kwaikwayo, da aka samu jirwayen tace a cikinsu. Kamar a magana jari ce, littafi na uku a labarin sususu da shashasha. Inda matansu suka sanya suka zama abin dariya a gari. Matar ɗaya daga cikinsu watau sususu, ta ce yace ba shi da lafiya, ya kuma yarda, ta ce ai ya mutu, ya kuma yarda, da ya mutun. Shi kuma ɗayan, watau shashasha matarsa tasa shi ya yi yawo tsirara, wai ta saƙa masa riga da wani zare da ba kowa ke iya ganinsa ba, shi kuma ya yarda. Haka kuma a littafin Ruwan Bagaja, an samu jirwayen mijin tace. A inda matar Malam Zurƙe ta dinga zuga shi har sai da ya tashi suka tafi daji don yin faɗa da wami mutum (Alhaji Imam). “Ita kuwa, ta yi ta turara mai gidanta da ƙarairayi har sai da ya tashi biɗi kulki ya nufi daji tare da ita”….

Haka kuma, a wani littafin wasan kwaikwayo mai suna Uwar Gulma, shi ma akwai nason mijin hajiya. Kamar inda uwar gulma dillaliya take cewa: “Ai ku kuke ƙyale maza suke rena ku, ni namiji in ya yi min, ai ma haɗu a gado”….

DALILAN DA KAN SANYA HAKA.

Bisa lura da kuma nazarin rayuwa, tare da sauye-sauye da akan samu. Tabbas akwai wasu dalilan da kan sanya wasu mazaje suke zama mijin tace, ko mijin hajiya, kamar haka: -

Karayar zuci.

Son abin duniya

Matsanancin son mace.

Baƙuwar Al’ada.

Sihiri ko tsafi.

Kissa da kisisina.

Karayar arziƙi.

Auren Gadara.

KARAYAR ZUCI:

Karayar zuci, na nufin mutum ya yanke ƙauna ga cin nasara, ko cire rai ga cimma burin rayuwa. A wata fuskar kuma, ana iya cewa gazawa, ko kasawa a gudanar da wasu al’amura. Sannan kuma ana iya cewa tsoro, ko razana. Ba shakka, karayar zuci tafi karayar ƙafa, kamar yadda Bahaushe ke cewa. Domin idan ka karye a ƙafa, ana iya ɗora ka ka warke. Shi kuma karayar zuci in aka karye ba ta ɗoruwa. Kusan ana iya cewa duk wanda ya samu karayar zuci, to ya zama “Talasuru” mai matacciyar zuciya, ko kuma raƙumi da akala, sai inda aka juya shi. Ma’ana ba shi da wani ra’ayin kansa. Duk wanda ya faɗa wannan hatsari, to babu makwa zai zama mijin hajiya.

SON ABIN DUNIYA:

Son abin duniya na nufin kwaɗayi na dukiya, ko wasu kayayyaki, ko kadara da sauransu. Kwaɗayi kan sanya wasu mazaje su faɗa haɗarin zama mijin hajiya. Domin akwai wasu mazajen da sukan aure mace saboda dukiyarta, ko dukiyar iyayenta. Akan kira wannan aure da cewa auren jari, ko auren hange-hange. A wani lokacin akan samu wasu mazajen da sukan zama tuwon tushe, watau ba su da kataɓus akan harkar gidansu. Wannan na faruwa ne a dalilin gudun kar ya saɓawa matar nan ko don dukiyarta, ko kuma abin da take yi masa na hidimar gida ta daina. Haka kuma idan iyayenta ke da dukiyar, kar su daina taimaka masa.

Bugu da ƙari, irin wannan hali ne ke sanya mai gida ya zama kamar baran gida. Domin a wani lokaci, matar kan aike shi kasuwa, ko wasu wurare, ko talla. A wasu gidajen ba ɗan aike mijin hajiya ke zama ba, abin ya kan kai har tana daka masa tsawa. Bayan wannan, hatta ‘ya’yan cikinsa kan raina shi, sannan kuma ba shi da iko a kansu. Ko da aure ‘ya’yansa mata za su yi, dole sai wanda uwarsu take so za su aura. In ba haka ba, ba za a yi auren ba. Wani mijin hajiyan hatta cefanen gida ita ke yi, ko kuma ka iske tana yi masa ɗinkin sallah.

MATSANANCIN SON MACE:

Wasu mazajen, tsabar soyayye da suke nunawa mace ke sawa su zama mijin hajiya. Kamar yadda Bahaushe kan ce: “So hana ganin laifi”. Bisa matsancin so da miji ke da shi a kan matarsa. A wani lokaci, bai iya cewa komai. Irin wannan, shi ke haifar da kishin saraku, watau kishi a tsakanin uwar miji da matar ɗa, ko ya haifar da kishin sauri, watau kishi a tsakanin matar ƙani da matar wa (yaya). Haka kuma, shi ke haifar da mummunan kishi a tsakanin matan mutum ɗaya (Kishiyoyi). Domin ya kan sakar wa mowa, watau matar so ragamar gudanar da harkar gida, wanda zai sa sauran matan su zama ‘yan bora (waɗanda ba a damu da su ba). Duk matsannacin son mace ke sanya haka. Bugu da ƙari, ko an nuna masa haka, sai ya rufe idonsa ya ƙi karɓar gyaran.

BAƘUWAR AL’ADA:

Haƙiƙa, hulɗa da baƙin al’ummu daga wasu sassan duniya. Baƙaƙe da farare, da Bahaushe ya yi, to ya haifar da tasiri mai yawa. Waɗannan al’ummu, sun bar al’adunsu Bahaushe ya ɗauki wasu, haka su ma sun ɗauki wasu al’adun Bahaushe. A al’adar al’ummar ba sa saɓawa matarsu, sai abin da take so, za ta yi. Misali, Turawa sun kawo ilmin boko, wanda Bahaushe ya rungume shi. Don haka ya yi tasiri matuƙa a kan wasu mazaje.

Da farko, wasu mazaje ‘yan boko ba sa wuce mace ɗaya, sannan kuma sun sakar ma ta ragamar gudanar da komai na gida, ba duka ɗan boko ke faɗa a ji a gidansa ba, musamman idan matar ta yi ilmin boko mai yawa, ko a ce ta fi shi yawan karatu. Ko kuma tana kan wani babban matsayi, ko muƙami a wurin aikin ta (ofis). Bayan wannan kuma, wani ɗan bokon, matarsa ko izinin zuwa unguwa ba ta tambayarsa, wannan kuma bai sa ya damu ba, kuma bai iya yi ma ta magana. A tunani irin na Bature, shi ne, ai tana da ‘yanci, saboda haka kar ya takura ta. Wannan kuwa, ai baƙuwar al’ada ce don ba al’adar mu ba ce. Daga irin haka, ana iya faɗawa ramin mijin hajiya.

SIHIRI KO TSAFI:

Kalmar sihiri, baƙuwar kalma ce daga harshen Larabci “Sihir”. Kalmar asali ta Bahaushe ita ce tsafi. Dukkan wasu kalmomi ko sunaye da akan yi amfani da su, kamar makaru, ko sammu, ko jifa, ko magani, ko tambaya, ko asiri da sauransu, ana yi ne don sakaya sunan tsafi. Haƙiƙa wasu mata kan yi amfani da tsafe-tsafe da dama, ta fuskoki masu yawa, saboda su mallaki mazajensu. Akwai matan da kan tafi wurin bokaye, da malaman tsibbu, da ‘yan bori don a haɗa masu abin da zai sanya su mallaki mazajensu. To daman an ce: “Tsafi gaskiyar mai shi”. Waɗannan ƙulumboto da mata kan yi, ko suke sawa a haɗa masu don mallake mazajensu, suna da yawa. Kaɗan daga ciki sun haɗa da: Miɗis, da Bi-ta-zaizai, da Bi-ni kamar kare, da Kar-ka- tsallaka, da bar shi kurum da sauransu.

Mazaje da yawa kan zama mijin hajiya a sakamakon tsafin da matansu suka yi masu. A inda sukan zama raƙumi da akala, ana juya su kamar maburgin miya a hannun mata a irin wannan ne akan ce, ai wane matarsa ta shanye shi, ko a ce ta wanke masa hannu a ka, ko ta kafe shi da sauransu.

KISSA DA KISISINA:

Wannan, na nufin halaye ne, ko dabaru waɗanda wasu mata kan yi, saboda su mallake mazajensu. Wasu mata sun iya nuna soyayya da kyautatawa ta ƙarya ko na yaudara. Suna iya zama na magana ko wajen biyayya, ko nuna ƙaunar danginsa, ko ‘ya’yansa, amma na ganin ido. Idan aka ce mace tana da kissa, ko kisisina, ko hila, to ta kan mallake mijinta gaba ɗaya. Bisa wannan dalili, sai magidanci ya zama bai son kowa, kuma ba ya ɗaukar maganar kowa sai na matar. Wasu matan su kan shiga tsakanin miji da iyayensa (Surukai) , ko tsakaninsa da danginsa, ko abokai, ko maƙwabta. Daga nan ya zama mijin hajiya.

KARAYAR ARZIƘI:

Rashi, ko ƙarancin abin hannu, kan haifar da magidanci ya zama mijin hajiya a mafi yawan lokuta. Ko da yake an fi samun attajirai, ko masu dukiya waɗanda suka karye, watau arziƙin su ya karye. Sau da yawa, wasu harkokin da sukan gudanar a da, sais u gagare shu a daloilin rashi. Sakamakon irin wannan halin da suka tsinci kansu a ciki sai al’amura su koma hannun matar. Haƙiƙa irin haka, kan sa mai gida ya zama mijin hajiya. A wani lokaci matar kan koma miji, shi kuma ya koma matar.

AUREN GADARA:

Auren dadara na nufin mutum ya yi alwashi sai ya auri wata mace mai mnatsayi iri kaza, alhali kuwa yasan cewa tafi ƙarfinsa, ko kuma ya auri ‘yar gidan su wane mai babban matsayi bayan kuma Bahaushe ya ce: “Ko yaro ya san matar aurensa”. Ko “Linzami ya fi ƙarfin bakin kaza”. Tabbas wasu mazan sukan yi irin wannan auren ne, don kawai su rinƙa yin gadara da cewar ai mata iri kaza yake aure, ko ‘yar gidan wane kaza yake aure. Wasu kuma don abokinsu ya auri wata mata daga wata zuriyya, to shi ma sai ya dage sai ya aura, don ya rinƙa yin alfahari da hakan.

Bugu da ƙari, a irin wannan halin, wasu mazan sukan daure da duk irin wulaƙanci, tare da wahalar da su da matar ke yi, ba sa nunawa, balle su yi magana. Domin Bahaushe ya ce: “Sa-kai ya fi bauta ciwo”. Mafi yawan mazajen da suka shiga irin wannan yanayi, suka faɗa ramin zama mijin hajiya cikin sauƙi.

BAUTAR MATA KOWA DA IRIN TASA:

Babu shakka, ana iya cewa kowane namiji da irin hidima, ko ɗawainiyar da yake yi wa matarsa to, amma shi mijin hajiya, nashi matsayin ya zarce hankali, idan muka dubi al’amarin zaman aure, ana iya karkasa shi gidaje, ko mazaje, ko magidanta zuwa kashi huɗu, kamar haka: -

Gidan Ilmi (Malamai na Addini da na zamani).

Gidan Sarauta (Sarki, ko Shugaba, ko Jagora).

Gidan Wadata (Mai kuɗi, ko Ɗan Kasuwa).

Gidan Talauci (Talaka, ko Matalauci)

Gidan Ilmi:

Gidan ilmi, na nufin gidan malamai, inda ake samun wasu malamai a gidajensu, sun faɗa cikin matsalar tace. Ko da yake dalilan da kan sanya wasu malamai su zama mazan tace, kan bambanta. Wasu malaman a dalilin bin shari’a da dokokinta ke sawa su zama haka.

Sharia’r Musulunci, ta sharɗanta a tausaya wa mace, kuma a kyautata ma ta. A sanadiyyar haka, sai matansu su fi ƙarfinsu, su riƙa juya su. Wasu malaman kuma, a saboda rashin lokaci na gudanar da wasu harkokin gida, sai su sakar wa matansu. To daga haka, sai mazan su zama mazan tace, wasu kuma a dalilin ganin mutuncin iyayen matar, watau surukai.

Da farko, ba za yi ma ta magana ba, ita kuma sai ta yi amfani da wannan damar, ta rinƙa juya mijin. Don haka, waɗannan na daga kaɗan daga cikin dalilan da kan sanya a samu mijin tace a cikin malamai, duk da yake ga ilmi.

Gidan Sarauta:

Gidan sarauta, na nufin gidan sarki, ko wani shugaba a kowane matsayi. Tabbas, ana samun mijin tace a cikin wasu daga sarakuna, da shugabanni na da, da na zamani. A mafi yawan lokuta, akan sami wani sarki, ko shugaba matarsa na juya shi kamar ƙaramin yaro. Komai mulkinsa, ko ɗamararsa, bai hana mace ta juya shi kamar sitiyarin mota. Misali:

“Wani babban soja ya dawo gida, har an buɗe masu get (ƙofa) , sai ya ce madam na ciki?” Mai gadi ya ce: “Tana ciki”. Sai ya ce wa direba: “Yi ribas mu koma”. Za a iya samun wani sarki ko shugaba ana matuƙar tsoronsa a waje, ko a fada da kuma ofis. Idan kuma ya koma gida, shi kuma yana tsoron hajiya shi ne ake cewa: “Ana tsoronka kana tsoron Hajiya”.

Gidan Wadata:

Gidan wadata, na nufin gidan wasu masu kuɗi, masu hannu da shuni. Akwai mawadata masu yawa, da suka zama mazajen hajiya. Ko da yake akwai dalilai da suke jawo hakan. Wasu masu kuɗin sukan sakar wa matansu ragamar gudanar da harkokin gida. Abin kamar wasa, sai ya zama ya wuce ƙa’ida, wanda daga nan, sai mai gida ya zama mijin hajiya. Wasu suna ganin isa ce, ko ƙauna, ko wayewa ke sa masu kuɗi na barin harkokin gidansu zuwa ga matansu. Akwai masu ganin harkokin neman dukiya ko tafiye-tafiye, ba zai bar su har su lura da wasu abubuwa ba. A ƙarshe, sai su bar wa matansu, su kuma su yi ta damawa, da mai tanka masu, ko a dangi, ko a abokai, balle kishiyoyi idan ma har akwai su.

Gidan Talauci:

Gidan talauci, na nufin talakawa. Akwai talakawa da yawa da suke zaman mazan hajiya. Su ma talakawan da akwai dalilai da suke jawo hakan. Matuƙar magidanci ya tsare nauyin da ke kansa, abu ne mawuyaci ya zama mijin Hajiya. Idan kuma ya zama talasuru ya gaza sauke nauyin da ke kansa, haƙiƙa zai iya zama mijin hajiya. Ko da yake akwai waɗanda kan shiga wannan hali bisa dole. Domin babu, babu abin da ba ta sawa. Wasu bisa dole ‘ya’yansu kan yi talla, saboda ko na cefane ba su da halin bayarwa, ita matar ce ke ƙuƙƙulawa ta san yadda za ta yi. Domin haka, sai ragamar gudanar da harakokin gidan ya koma hannun matar. Daga nan sai ‘ya’yansu su fara gagararsa, ba sa saurarornsa balle su yi shawara da shi.

GWANO BA YA JIN WARIN JIKINSA:

Wani abin mamaki, da ban haushi, da takaici, game da al’amarin mijin tace, shi ne, ko da iyaye, ko dangi, ko abokai sun gane irin halin da yake ciki. Ko da sun yi ƙoƙari su nuna masa, ko su ƙwato masa haƙƙi, sai ya bijire ya ƙi sauraronsu. Kai in har aka matsa masa, sai ya ce: “Kar ku dame ni” “Ai bautar mata kowa da irin tasa”, ko ya ce: “Gwamma talla da biko”, da dai sauran maganganu masu nuna cewa ba ruwan ko da da shi.

Wani mijin hajiya ma ko ya ɗauki shawarar da aka bashi. Da zarar ya koma gida ya faɗa ma ta, sai ya fasa ya ƙi ɗaukar shawarar.

ILLOLIN DA KAN BIYO BAYA:

Sakamakon faruwar waɗancan dalilai, da suka sanya wasu mazajen suka zama mazan hajiya. Babu shaka, akan samu wasu illoli da sukan biyo baya. Waɗannan illoli kuwa, sukan cutar da al’umma gaba ɗaya. Kaɗan daga cikinsu sun haɗa da:

Zubewar mutunci.

Gurɓacewar tarbiyya.

Ɓata zumunta.

Taɓarɓarewar al’umma.

Zubewar Mutunci:

Babu shakka, matuƙar aka ce mutum ya zama mijin tace, mutuncinsa kan zube gaba ɗaya. Dalili kuwa, duk mijin tace ba ya yin magana ɗaya. Domin in ya yi magana ko alƙawari, sai hajiya ta yarda, in ba ta yarda ba, sai ya fasa. Bisa wannan dalili, sai ya zamanto ba ya magana ta tabbata. A ƙarshe, al’umma za su ɗauke shi ba shi da dattaku, to a nan mutunci ya zube. Kamar yadda Alhaji Aƙilu Aliyu yake cewa:

“Malam nemi ɗiyar Dattawa,

Sanda kake riya neman aure.

Ba mai gemu ko saje ba,

Ba mai mota ko babur ba.

Ba mai faffaɗar riga ba,

Ba mai gogaggen wando ba,

mai magana ka ji tamkar ƙyaure.

In ya ce i, ba ya a’a,

Wanda yake da kula da shari’a’,

Wanda a zuci yana da ƙana’a,

Ba nauyi ba kawai ga jama’a.

Ba kanari ba kurum ɗan kare. ”

Haƙiƙa waɗannan baitoci, sun nuna mana hoton dattijo, kamannunsa da ɗabi’unsa. Don haka, duk wanda ya saɓawa waɗannan abubuwa, ko ya rasa su, to shi ba dattijo ba ne, kuma mutuncinsa ya zube. Bisa wannan dalili, mijin hajiya ba shi da mutunci, sai dai na riga ko muƙami.

Gurɓacewar Tarbiyya:

Sakamakon rashin iko na faɗa a ji, ko tsawatarwa kan haifar da hukunci ya koma hannun mace, ko da ya ga ɓarna, baida ikon hanawa. ‘Ya’yansa maza da mata kan zama sangartattu, kuma su zama ‘ya’yan mace. A zahiri, Bahaushe kan ce wa zai auri ‘yar mace? Ko ya ce: “Wane ai ɗan mace ne”, ma’ana ubansa bai da iko akansa. Don haka, ya samu rauni a tarbiyyarsa. A bisa rayuwa ta haƙiƙa, ana son duk yaro ya tashi tsakanin uwa da uba, kuma kowanne cikinsu yana da irin gudummuwar da zai bayar ta fuskar tarbiyya. Kamar yadda aka sani ne bisa al’ada, yara sun fi tsoron iyaye maza fiye da iyaye mata. Wannan, bai rasa alaƙa da kasancewarsu tare da iyaye mata a ko da yaushe.

Ɓata Zumunta:

Idan aka yi rashin sa’a, mace ba ta son zumunci da dangin miji, sannan kuma mijinta ta shanye shi, ma’ana mijin hajiya. Tabbas zumunci zai ɓaci, saboda ba za ta bar shi ya yi hulɗa da danginsa ba, balle har ya kyautata masu. Idan ba a yi sa’a ba, sai dai ya yi da danginta. A irin wannan ne, mata kan ce: “Dangin miji ba ku san abin arziƙI ba” ko “Dangin Miji ba ‘yan goyo ba ne”. Bayan wannan kuma, hatta zumunci na cikin gida ɗaya a tsakanin mai gida da ‘ya’yansa, ko mai gida da sauran matansa, watau kishiyoyi ke nan. A bisa dalilin zama mijin tace da mai gida ya yi, shi yasa ake samun ‘yan ubanci, inda mai gida kan ware wasu daga cikin ‘ya’yansa a matsayin ‘ya’yan so (waɗanda ake kyautatawa) , wasu kuma a ƙyamace su, ba a son su, irin wannan wariya, shi ke haifar da ‘yan ubanci a cikin ‘ya’yan mutum ɗaya, amma uwarsu kowa da tashi, watau ‘ya’yan turaka (‘ya’yan kishiyoyi). Ta fuskar kishiyoyi kuwa, mai gida mijin tace ya kan fifita matar so, wannan zai iya kasancewa uwar gida ko na ‘yar mowa da ‘yar bora ba za a samu zaman lafiya ba ballantana har a yi zumunci.

Taɓarɓarewar Al’umma:

Taɓarɓarewar al’umma, na nufin lalacewa, ko susucewar al’umma. Wannan na iya samun al’umma, ko ƙasa, ko gari, a dalilin yawaitar mazajen hajiya. Idan aka rasa kakkyawar tarbiyya a gida, dole ne ya shafi sauran gidajen, watau maƙwabta, da zaran aka ce marasa tarbiyya sun yawaita, to dole al’umma ta lalace, al’amurransu su taɓarɓare.

KAMMALAWA

A ƙarshe, wannan muƙala ta ɗan taɓo wasu daga cikin ɗabi’un wasu mazaje ko magidanta. A inda aka fito da dalilai da illoli, tare da nuna matsayin mijin hajiya ko mijin tace. Idan muka kalli bayanan da suka gabata, sai mu ce dalilan da sukan sanya magidanci ya zama haka, sun bambanta daga wannan magidanci zuwa wancan, ko daga wannan gida zuwa wancan. Haka kuma, mun ga irin hanyoyi ko dabaru waɗanda wasu matan kan bi su jefa mazajensu wannan rami

Bayan haka, wannan muƙala ta kawo shawarwari ga mazaje a inda aka yi hannunka mai sanda ga mai hankali, saboda a gudu tare, a tsira tare.

Ina fatan wannan muƙalar ta zama matashiya gare mu mazaje, a nan ma ya haɗa har da ni.

Alhamdu Lillahi. Allah Yasa mu dace, amin.

 MANAZARTA

Aƙilu A (1985) Fasaha Aƙliya Northern Nigerian Publication Company Zaria.

Imam A (1939) Magana Jari ce na uku. Northern Nigeria Publication Company

 Zaria.

Imam A. (1937) Ruwan Bagaja. Northern Nigeria Publication Company Zaria.

John T. U. (1989) Jiki Magayi. Northern Nigeria Publication Company Zaria.

Maƙarfi S. (1970) Jatau na Ƙyallu. Northern Nigeria Publication Company Zaria.

Sada M. (1969) Uwar Gulma. Northern Nigeria Publication Company Zaria.

Hauwa A. (2010) Don Iyalai. Jaridar Nasara

Sadiyya I. B. (2008) A Gani na. Jaridar Gaskiya Tafi Kwabo.

Imam S. (2014) Hira da shi a gidansa. Bakin Kasuwar Sati Unguwar Dosa Kaduna.

Sarki A. (2014) Hira da shi Kasuwar Sati, Unguwar Dosa Kaduna 23/2/2014

Jiƙamshi S. (2014) Hira da shi Kasuwar Sati, Unguwar Dosa Kaduna 27/2/2014.

Is’haƙa A. (2014) Hira da shi a gidansa Layi Mai Anguwa Unguwar Dosa Kaduna

23/2/2014.

Lawal M. (2014) Hira da shi a gidansa Layi Mai Anguwa Unguwar Dosa Kaduna

 23/2/2014

 Hausa Post

Post a Comment

0 Comments