WANDA AKA GABATAR A KWALEJIN KOYON LARABCI DA ADDININ MUSULUNCI TA SHABAB DAKE UNGUWAR DOSA KADUNA. RANAR JUMA’A 14 GA MAYU 2012.
BAƘIN BATURE (BAƘIN MUTUM DA KAN BANASARE): TSOKACI A KAN ƊABI’UN
WASU ‘YAN BOKO MASU RA’AYIN GABA-DAI GABA-DAI
DAGA
MU’AZU
SA’ADU KUDAN
SHIMFIƊA:
WANE NE
BATURE? Bature na nufin mutumin da ya fito daga nahiyar Turai. Wannan nahiya
ta ƙunshi ƙasashe irin su Ingila ko
Birtaniya, Faransa, Jamus, Italiya, Holan, Esfaniya da sauransu. Waɗannan Ƙasashe sune a Turai ta yamma (western Europe). Idan muka koma
Turai ta Gabas (Eastern Europe) sun haɗa da Ƙasar Rasha,Jamus,Hongiri da
sauransu. Bature na nufin namiji, mace kuwa Baturiya,jam’i kuma Turawa. Ita
kuwa Kalmar Nasara daga Harshen Larabci,mai asali daga kalmar nazaret da aka
samo ta,daga sunan wata Ƙabila da kuma sunan wani
gari a Ƙasar Isra’ila.
Baya ga
waɗannan
Turawa na asali, sai kuma waɗanda aka turantar da su. Waɗannan kuwa sune kamar Amurka, Kanada, a da waɗanan mutane asalinsu ba
Turawa ba ne. Bisa dalilin mallakarsu da Turawa suka yi,ta hanyar mulkin
mallaka. Wannan yasa aka turantar da su a inda suka rikiɗa suka zama Turawan dole. A
inda har ma suka zama ‘’feƙe kafi ƙaya tsini’’. Turawan Birtaniya suka tafi Amurka suka iske
indiyawan daji da kaboyi masu kiwon shanu. Waɗannan mutane suna da harsunansu na asali,amma aka cusa masu
harshen Turancin Ingilishi.
Hoton
Bature; shi mutum ne fari,
mafi farar fata kamar zabiya mai gashin kai ƙarangiya
launi ƙasa-ƙasa mai ido launi toka-toka kamar na mage. Mai baki ƙarami da matsattsen hanci mai tsini. Baturiya ita kuma tana da
gashin kai har ya sauka kafaɗa, wasu kuma har gadon bayansu.
Hoton Baƙin mutum shi kuma, a nahiyar Afrika Allah ya ajiye
shi. Bahaushe kuma yana cikin nahiyar Afrika sashin yammacin Afrika a Ƙasashen Nijeriya,Nijer,Gana,da wasu Ƙasashe na Afrika. Baya ga nan, duk sauran wurare da ake samun Baƙaƙen fata kuwa ban da Afrika to kai su aka yi.
GABATARWA.
Da sunan
Allah Mai rahama Mai jinƙai, Mai kowa, Mai komai,
Mai aikata abin da Ya so, ga wanda Ya so, a sadda Ya so a yadda Ya so, ko ana
so ba a so dole bayi su so. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban
halittu Annabi Muhammadu, da Alayensa da Sahabbansa.
Wannan muƙala zata ɗan taɓo, wani abu da ya shafi wata irin rayuwa da Bahaushe ya tsinci
kansa a ciki. Wannan rayuwa ta kasa Bahaushe zuwa gida uku ko huɗu. Kowane daga cikinsu
akwai irin nasa rayuwa,tare da dalilai da suka jefashi cikinta. Wannan yasa na
kira muƙalar da suna ‘’Baƙin Bature’’ (Baƙin mutum da kan Banasare). Ma’ana gashi baƙI ne to amma tunaninsa na Bature ne. Za mu tsakuro wasu dalilan mu
kallesu,don muga irin tasirin da suka yi. An ce komai bai rasa sanadi,saboda
haka zuwan Turawa Afrika shi ne sila. Dogon lokaci da aka ɗauka ana tare ya taimaka a
kan haka ƙwarai.
Zuwan
Turawa Nahiyar Afrika,Turawan da suka fara tako
Afrika ta yamma sune Turawan bincike (explorers) ku mu ce ‘yan leƙen asiri (spices). Kamar yadda aka sani ne, cewa wani Baturen
Potugal mai suna Mango Park da wasu ayarin mutane huɗu, sune suka fara zuwa
Afrika, wasu kuma suka ce a’a wani Baturen Ingila ne Henry the navigator shi ne
ya fara zuwa.
Bayan waɗannan kuma, sai ƙungiya ta biyu, ita ce ƙungiyar ‘yan kasuwa
(traders) masu cinikin bayi (slave traders). Waɗanda suka taka muhimmiyar rawa wajen rusa nahiyar Afrika.
Daga su
sai kuma ƙungiyar masu kare ‘yancin Ɗan adam
da hana cinkin bayi, watau (Humanitanians) Waɗannan sun taho ne tare da ƙungiyar
Turawa mishan watau (Missionaries) masu yada addinin kirista.
Ban da waɗannan kuma, sai wasu ƙungiyar watau Turawan kamfani (trader for ligetimate trade) waɗanda suka rinƙa sayan kayan amfanin gona (gyaɗa, auduga, fatu da ƙiraga, kwakwar manja,
koko, ƙaro da sauransu. )
MULKIN
MALLAKA (COLONIAL RULE) 1900-1960; Turawan kamfani su ne suka share wa Turawan
mulkin mallaka hanya, (colonialist). Tabbas Turawan kamfani sun e suka fara
rusa ko karya Daulolin mu (kingdoms and empires) kamar Daular Oyo,
Benin,Etsekiri a kudu. A nan arewa kuma Daular Sokoto (Sokoto caliphate).
Bayan
Turawan kamfani sun gama yin irin nasu zagon ƙasa, musamman kamfanin Royal Niger Company. Su kuma Turawan mulkin
mallaka suka zo suka ƙarasa ruguza mu. Bayan sun
rusa Daulolin kudu, sai suka dawo Arewa kan Daular Sokoto. A inda suka rinƙa yi masu ɗauki- ɗai-ɗai, daga shekarar 1900 suka dirarwa Bidda, Kwantagora, Keffi, sai
Zariya 1902, Kano 1903 a ƙarshe Sakkwato 1903.
Bugu
da ƙari, da suka ci galabar mu, sai suka kafa wani mulki mai kama da
baba –na ɗaka- gemu- na- waje ko kuma cinka –nan –kashin-can. Ma’ana
Sarauniyar Ingila ita ce take mulki daga can Turai, amma kuma wakilinta ke
aiwatar da umarnin ta.
A
shekarar 1914, sai aka ƙulla wani auren zobe
(amalgamation) , inda aka haɗe sashin kudu (southern protectrate) da sashin arewa (northern
protectrate) a ƙarƙashin jagorancin Pedrict Lord Lurgard. Bayan ya haɗesu (kudu da arewa) sai
matarsa Florence lurgard ta raɗawa Ƙasar sunan Nijeriya wanda
ya samo asali daga kogin Kwara (River Niger).
Turawan
Birtaniya sun gudanar da mulkin Nijeriya, ta hanyar tsarin mulkin mai shamaki
(indirect rule). A inda yake a sama Turawa ne, a tsakiya zuwa ƙasa sarakunan gargajya. Kamar haka: gwamna janar, mai binsa Resdan
daga shi sai D. O (District Officer). Dukkan waɗannan Turawa ne, daga baya aka ƙara D. D.
O (Deputy Director Officer) wanda ake kira baƙin
Bature. Bayan su sai kuma sarakunan mu kamar haka:
Sarkin
yanka (Emir) , Hakimi (District Head) , sai Dagaci (Village Head) a ƙarshe Mai Unguwa (Ward Head). Haka wannan tsari ya gudana na
tsawon shekara 60 ko fiye da haka.
ZAMA DA
MAƊAUKIN KANWA; Wannan irin dogon zama da aka yi, na shekaru masu
yawa. Shi ne ya haifar da abubuwa da yawa da suka yi tasiri a kan rayuwar
Bahaushe gaba ɗaya. Shi wannan irin tasirin kuwa, zamu iya karkasa shi zuwa kashi
huɗu ko kuma
su mutanen kamar haka:
1. Akwai
mutanen da tasiri ya yi masu jirwaye suka yi dabbare- dabbar.
2. Akwai
mutane da suka yi rabi da rabi kamar ragon uda ko akuya mai gefe rabi fari rabi
baƙi.
3. Akwai
mutane da suka yi baƙi-baƙi.
4. Akwai
mutanen da suka rikiɗe gaba ɗaya sun yi baƙiƙƙirin. Sun ƙuna ba su gudun ƙauri.
Kowane
daga cikinsu baya rasa dalili da ya sanya shi zama hakan;
i. Rukunin
mutane na farko su basu yi boko ba, amma sun fi ‘yan bokon zaƙewa.
ii. Rukunin
mutane na biyu, ana iya samun ‘yan boko zalla watau waɗanda suka yi karatun zamani
kuma suka ɗauki ra’ayin boko, amma kuma suna gaurayawa da al’adunsu.
iii. Rukunin
na uku,sune boko sana’a, suna cin moriyar ta amma ba su dulmiya ba.
iv. Rukunin
mutane na huɗu su ake
kira boko aƙida, kuma tunanin su yafi na Bature, tun da su rayuwarsu ta yi ban
–tafin- makafi da rayuwar Bahaushe da kuma musulmi.
A inda
suturarsu da harshensu ba su ɗauke su da muhimmanci ba. Kai har da addini, al’ada da tunani,
babu wani abu muhimmi, sai wanda Bature ya yi, ko ya faɗa. Ga masu irin wannan
tunani na Nasara, maganarsu, rayuwarsu da tunaninsu duk na Bature ne. Farko
dai, matarsu 1, ‘ya’ya 2-3,ga baƙar rowa kamar yaro ɗan yaye, ƙin zumunci kamar ɗan tsako, kare yafi ɗan uwa, farkarsa tafi matar aure. Ya san tarihin turai, bai san
danginsa ba ko na Ƙasarsa. Ƙyale dala’ ilu ka ɗauki jarida. Jikinka na Kano zuciyarka a London, shi da
makwabcinsa kuwa ba ruwan wani da wani (mahaukaci ya yi baƙo) , jikinka baƙi zuciya ta Nasara.
To wannan
shi ne baƙin Bature, ɗan boko ne ko ba ɗan boko ba.
MASO
KAYANKA YA FI KA DABARA; Dangane da hanyoyi ko dabarun da Turawa suka bi wajen
cin nasarar wannan aiki shi ne, yaudara da yaƙi
da ƙwaƙwalwa (tunani) da Larabci ( gazawatul fakir) da turanci kuma
(psychological warefare). A inda suka yaƙi tunani mutane ta hanyar
yin amfani da ‘yan korarsu farare da baƙaƙe da barbarar yanyawa.
Haka kuma
sun yi amfani da wayon rainin hankali, watau riƙe
min ɗa na,ka
ba ni naka in buga. A nan sukan kushe al’adunka, amma su fifita nasu don ka karɓI nasu. Su munana maka naka
amma su ƙawata nasu.
Dandaƙa ko hana haihuwa; wata
dabara da suka yi amfani da ita,don su rage yawan mu ta hanyar hana yin aure da
wuri mazanmu da matanmu. Misali yin karatun boko a daɗe ana yi, har sai shekaru
sun yi nisa. Kamar saurayi sai a iske ya kai shekaru 35-40 bai yi aure ba, mace
kuma sai ta wuce budurwa ta kai uwar mata, ta kai shekara 25-30, wasu ma fiye
da haka. Idan aka kwatantasu da tsararrakinsu da suka yi aure kafin su. Misali
shekaru 18- 25 sai a iske sun hayayyafa kuma sun kafu. Waɗanda suka makara kuwa,
al’amurra sukan kasance a murɗe. Da farko yara kan kasance kaɗan, kuma iyayen su tsufa yara basu taso ba. Haka kum ga ƙyamar haihuwar ‘ya’ya da aka cusa masu. Ɗa ɗaya kamar goɗiya. Ga ƙayyade iyali ko tazarar
haihuwa da sauransu.
Gudun
zumunci da ƙyamar dangi;Duk wanda ya faɗa irin wannan rayuwa, yakan koma Baƙin
Bature. Haka kuma yakan koma yana ƙyamar wani ya kusance shi,
daga shi sai matarsa da ‘ya’yansa ko karensa idan ma har akwai ‘ya’yan ke nan.
Wannan ne ya haifar da ƙin riƙon ‘ya’yan ‘yan uwa ko ziyartar dangi watau zumunta.
Raina
tunani ko fifita kansa akan waninsa; Duk wani
wanda bai da tunani irin nasu, komai ya taso matuƙar dai ya
saɓa da
ra’yainsu, sai su ce hauka ne ko da iyayensu ne.
Sakin na
hannu kamun na guje; Abin da ke faruwa a
nan shi ne, irin waɗannan mutane sukan yi watsi da al’adunsu, harshensu, tufafinsu,
abinci, magani da sauransu. Wanda a ƙarshen al’amari sai su
tashi a tutar babu, su zama jemagu ba su a tsuntsu ba su a dabba. Da farko, su
dai ba Turawa ba, kuma ga su sun guji baƙaƙe sun yi rasasa- rasasa.
Kishi a
rashin kishi ( kishin kare) ; waɗannan mutane sukan yi kishi
a inda bai dace ba, kuma su ƙi yin kishi a inda ya
kamata. Miji bai kishin matar sa, bai damu da maza komai yawansu su yi hulɗa da ita ba a wani lokaci
su ake aikawa su kira ta.
Ɓangaren mata; su kuma sai aka cusa masu
kishin banza (kishin mai dadaro). A inda suke ƙyamar mijinsu ya ƙara aure, amma kuma yana da
farka a waje. Sun ƙi zama da kishiya,
amma ƙawar Alhaji ko Amimiyarsa ko abokiyar aiki za ta zo gidan su,kuma
su karɓe ta
hannu bibiyu. Duk ɓarnar da miji zai yi indai ba maganar kishiya to daidai ne.
Wata
yaudarar da aka yi wa mata; Da farko bayyana tsiraci,
(tun daga Budurwa har Matar aure) canza halitta (shafe-shafe don a yi fari)
, ƙyamar haihuwa da son abinda duniya (dogon buri) ,sun sacewa mata
kunya,sun kawar da ƙauna,tausayi da ke tsakanin
Uwa da ɗanta.
Suka mayar da shi tsakanin Nani (mai raino) da yaro da sauransu. Wannan kuma
ita ce Baƙar Baturiya.
TO JAMA’A
INA MAFITA? Matuƙar aka rutsa mage a cikin ɗaki, to dole ta nemi mafita inda zata gudu, don ta tsira da ranta
ta samu ta kuɓuta. Bisa wannan dalili, ina mai yin kira ga dukkan Bahaushe da
Bahaushiya, da cewa mu farka daga baccin da muke yi, mu san kanmu, mu kula da
kanmu, da mu tsare kanmu.
Dukkan
mai hankali a jikinsa ya kamata ya dawo cikin hayyancinsa ya tsaya ya yi wa
rayuwarsa kallon natsuwa. Watau kallo irin na sayen goron tsohuwa. Wajibi ne mu
sanya kishin harshen mu, al’adunum da addininmu, saboda su ne rayuwar mutum
gaba ɗaya. Matuƙar aka ce mutum ya rasa su to zai yi ballagazar rayuwa mara manufa
da amfani. Domin ya yi ɗigirgire ko kan-tafi da rayuwarsa,an kuwa ce kan-tafi masomin
asara.
Ga wata
tambaya ga masu ra’ayin nasara, shin wai sun san cewa, sauran Ƙasashe da suka ci gaba, ba irin wannan hanyar suka biyo ba?. To
idan masu irin wannan tunanin ba su sani ba,to ga wani bayani: Ƙasashe da yawa da suka riƙi harshensu a matsayin
harshen ma’amulla,watau Harshen Ƙasa. Suka tsare al’adarsu
suka tsare addininsu, sun ci gaba nesa ba kusa ba. Misali: Sin (china) Indiya,
Japan, Iran,Kyuba, Birazil da sauran su.
Matashiya
ga masu irin wannan ra’ayi. Tabbas
wannan magana gaskiya ce, kuma a zahiri duk mai hankali zai yarda da ita.
Al’ada dai kamar riga ta ke, don haka al’adarka ita ce rigarka wadda ta ke
daidai da kai. Idan kuwa har ka ɗauki rigar wani, in har ba a yi sa a ba, za ta yi maka yawa ko a
tsawo ko a kauri ko faɗI. A ƙarshen al’amari ko ka sanya
ba za ta yi maka kyau ba. Shi ya sa aka ce naka shi ne naka kayan aro abin
shirme ne,in mai abin ya karɓi abinsa to dole zaka komo naka.
Ina kira
ga masu hankali a jikinsu da su san cewa kaza ba ta zama agwagwa, haka ita ma
agwagwa ba ta zama kaza. Don haka mu tsaya a inda Allah ya ajiye mu, kar mu
wuce gona da iri. Domin in ba haka ba zamu yi saki na dafe, zamu zama ba Turawa
ba, kuma ba baƙaƙe ba. Da farko mun watsar da al’adunmu, harshen mu waɗansu ma har da addininsu.
Ina yi wa
Bahaushe albishir, idan bai sani ba ya sani cewa, Allah ya yi wa harshensa da
ala’dunsa ɗaukaka a duniya. Domin a yanzu harshen Hausa ya karɓu ƙwarai, tufafin Bahaushe na da kwarjini a ko ina a duniya, sannan
addinisa na musulunci ya gagagara a duniya. Duk da irin tsangwama da Turawan
yamma da Yahudawa suke yi masa, shi ne a sama cikin ikon Allah. To dama
Bahaushe ya ce “an so kare da gwaiwa Allah ya bai wa rago” don haka mu taru mu
yi kishin kan mu, saboda wasu Hausawa sun ɓata biyu ɗaya ba ta gyaru ba. Su dai ba harshen Turancin, kuma sun saki
Hausar a ƙarshe sun saki reshe sun kama ganye. Haka ita ma al’adar sun bar
ala’adar Bahaushe sun ɗauki ta Bature, sai dai kuma ba a Turai suke ba. Gashi kuma
Turawan ba za su karɓe su ba, sai su ƙare a rasasa-rasasa. Alhali
kuwa masu hikima sun kasa ribar rayuwa mataki uku zuwa huɗu kamar haka:
1. san samu
(mutum ya samu alherin duniya da na lahira)
2. samu rasa
(mutum ya samu alheirn duniya ya rasa na lahira)
3. rasa ka
samu (mutum ya rasa alheri duniya ya samu na lahira)
4. rasasa-rasasa
(mutum ya rasa alherin duniya da na lahira)
Allah ya
tsare mu amin.
KAMMALAWA;
A ƙarshe wannan takarda, ta tsakuro wasu halaye ne na wasu mutanen mu
waɗanda
Turwa suka yaudaresu suka kuma sake su a igiyar ruwa. Irin waɗannan mutane ana samunsu a
maza da mata. Don haka akwai baƙin Batutre, akwai baƙar Baturiya, ko baƙin mutum da kan Banasare da
kuma baƙar mace da kan Banasariya. Kamar yadda bayani ya gabata cewa,
an ɗan taɓo ne. Domin abubuwan suna
da yawa. Ina fatan al’umma su fahimci inda wannan muƙala ta sanya gaba. Manufar ita ce mutum ya san shi wane ne, kuma
mene ne matsayinsa?Don ya yi kishin kansa, saboda an ce’’ da uba aksse ado, in
don riga ko a kasuwa sai a saya’’.
Mun riga
munji irin illolin da Turawan nan suka yi mana, ta fuskoki marasa iyaka kuma ta
kusurwoyi daban daban. Domin wasu har halitarsu suke sauyawa, daga baƙi zuwa fari ta hanyar shafe-shafe (bleaching) ko dasa gahin kai,
nuna tsiraici da sauransu. Allah Ya tsare mu Ya bamu ikon gyarawa amin.
Assalamu alaikum
KIRARIN
BATURE
1. Bature
manta sallah mai fitsarI a tsaye.
2. Huntu
ubangijin mai riga.
3. Goga ka
fi kyau tsira- tsira.
4. Ka ci
gari ka kwana a daji.
5. Bature
mai ture mutum a hanya ta ƙwarai.
6. Nasara
asarar duniya.
7. . Nasara
jar akuya mai kaI ga yara ɓarna.
8. Na Ingila
ba ku daɗin gaba.
9. Na
Jamus ɓata Ƙasa.
10. Na
Faransa a bi ku a huta.
11. Shirinya
raɓi ki
kashe.
12. Mishau
bad da musulmi.
13. Kowa ya
daka taku zai yi nadama.
14. Kori
tsohonka ka girmama kare.
15. Kori
matarka ka kwana da farka.
16. Gaida
kwartonka ka ba shi abinci.
17. Ƙadda baƙon dole, ana ba wuri kana kafa ɗaki.
18. A ci tuwo
da kai, ai tsadar kai kwano.
19. Nasara ba
ku yi don Allah, kun fi son ku yi suna.
20. Nasara ba
ka cin hatsi sai rayis.
21. Nasara ba
ka aikin banza.
22. Faransa
romon jaɓa.
23. Na
faransa mai kisa ba shiri’a
MANAZARTA
OniS.
(1980) West African History 100 Questions And Answers. University Press Ibadan
Brian C.
(1968) A Map History of the Modern World second edition Heimann Educational
Books Ltd. Lodon
Lempert.
L. O. (1968) A History of Africa 1918-1967 Printed in the U. S. S. R.
Sarki H.
A. (2000) Zuwan Musulunci a Afirka da shigowarsu
Ƙasar Hausa. G. A. Computer Centre. Ikere – Ekiti, Ekiti State.
Adam M.
Tahir (1997) Asalin Hausawa da Harshen su. Kano Nigeria.
Madauci
I. (1963) Al’adun Hausawa. Northern Nigerian Publication Company Zaria.
Shagari
S. A. (1975) Waƙar Najeriya. Northern Nigerian Publication Company, Zaria.
Bunza
A. M. (2006) Gadon feɗe al’ada. Tiwel Nigeria Limited Surulere, Lagos.
Ladan
Y. (1980) Zaman Duniya Iyawa ne. Northern Nigerian Publication Company,
Zaria.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.