Being a mandatory Ph. D seminar paper, presented at the Department of Nigerian Languages. Faculty of Arts and Islamic Studies Usmanu Ɗanfodiyo University Sokoto, 2014
RIKIƊA A FALSAFAR BAHAUSHE
NA
SA’ADU MUHAMMAD MU’AZU
Department of Nigerian Languages.
Usmanu ƊanfodiyoUniversity
Sokoto
FITATTUN KALMOMI
MA’ANAR FALSAFA
Falsafa wata kalma ce
da ta samo asali daga harshen Greek (Girkanci) , watau “Philosophy”. Dangane
da ma’anar wannan kalmar kuwa, wasu Masana kuwa, ga abin da suka ce: Falsafa: wani
tunani ne mai ƙunshe da ilmi da nazari a kan wani al’amari (tarihi, da
addini, da kimiyya da sauransu) wanda masana suka tattake wuri, tare da bayyana
ra’ayinsu a kansa. [1]
Ilmi ne da ke tsara ilmummukan magana da ɗabi’u, da siffar kyau da tunani na hankali,
ko wani tsari na addini, ko wani fage na nihsaɗi na mutum, ko kuma aƙida, da fahimta, da
matsayi na wani mutum ko na wsau jama’a. [2]
Hanya ce ta tunani da ƙoƙarin samun bayanin dukkan al’amurra da suka shafi duniya
da ɗan Adam da inda suka
sa gaba. [3]
Wani tsari ilmi ne mai alaƙa da imani, da tunani mai zurfi a kan
al’amarin rayuwa da halita, da duniya, da kuma nazarin halayyar wani. [4]
Bisa fahimtar bayanan da Masana suka yi, muna
iya cewa, kalmar falsafa na nufin wani ilmi ne mai zurfi dake ɗamfare da dogon
tunani. Kuma ya shafi fagagen rayuwa da yawa, wanda ya dogara kan zuzzurfan
bincike wanda gogaggun masana suka gudanar. Bahaushe na irin wannan ilmin, ko
tunanin game dabbobi da tsuntsaye, musamman kan barbara, da haihuwa da kuma
rikiɗa.
MA’ANAR RIKIƊA;
Sauya kamannu, abu ya
juye daga kamannunsa, kirarsa, ko siffarsa, ko launinsa ko a mayar da wani
mutum,ko dabba,ko tsuntsu,[5]
zai iya zama sauya ɗabi’a ko halaye,ko
kamannu ko yanayi ko kuma a sauya wani mutun ko dabba ko wani abu. [6]Sauya
kamannu daga na asali zuwa wani[7]
sauyawa wani mutum ko dabba ko wani abu zuwa wani matsayi ta hanyar tsafi ko
sihiri ko dabo. [8]
sauyawar yanayin ƙirar jiki na ɗabi’a ko halita kamar girman jiki daga jariri
zuwa riƙa (kamar kwaɗo daga gwadari zuwa tsulbu zuwa kwaɗo,ko ƙozo) ,sauyawar
yanayin siffa da launi na dabi’a da wani abu kan yi kamar dutse daga ruwa ruwa
zuwa sandararre ko kuma ruwa zuwa ƙanƙara,ko ƙanƙara ta narke zuwa
ruwa. [9],rikiɗa na nufin jirkita
abu ya koma wata siffa. misali ɗan dabo ya mayar da mutum ya zama dabba. [10]
Sauya siffa ko kamannu daga ta asali zuwa wata sabuwa ta daban,musamman na
dogon lokaci ko taƙaitacce. [11]
Bisa lura da bayanan
masana muna iya cewa rikiɗa na nufin sauya
kamannu na ƙira ko launin jiki, daga siffa ta asali. Wannan na faruwa
ga mutum, ko dabba, ko tsuntsu.
GABATARWA:
A
wannan muƙala za ta ƙunshi wasu bayanai,
game da falsafal Bahaushe. Akan irin yadda Bahaushe ke ɗaukar dabbobi da
tsuntsaye a tunaninsa, ta fuskar abin da ya shafi rikiɗa da kuma ma’anarta,
da ire-iren rikiɗa kamar rikiɗar dake da alaƙa iskoki, da tsafi,
da sihiri, da dabo ko rufa-ido. Haka nan kuma da dalilan da kan sanya a yi ta,
tun daga Mutum, ko iska, ko dabba, ko kuma tsuntsu. Wannan irin matsayi ne har
ya haifar da Bahaushe ke alaƙanta wasu dabbobi da tsuntsaye da
iskoki. Za’a dubi wannan tunanin ne ta mahanga al’ada, a ƙarshe kuma sai naɗewa.
IRE-IREN RIKIƊA. Bisa ga tunanin
Bahaushe game da rikiɗa ana iya cewa ya
karkasa ta zuwa kashi 4, kamar haka: 1-Rikiɗa ta ɗan lokaci. 2-Rikiɗa Mai tsawo. 3-Rikiɗa ta din-din-din. 4-Rikiɗa ta ɓatar da sawu.
RIKIƊA TA ƊAN LOKACI: Akan samu rikiɗa ta wucin-gadi ne,
saboda ƙwatar kai (rai). A mafi yawan dabbobi ko tsuntsaye kan
rikiɗa ne cikin ƙanƙanin lokaci, domin su
ƙwaci
kansu daga halakarwa ko cutarwa daga abokan gaba. Ko da yake a irin wannan rikiɗa ba a cika daɗewa ba. Da zarar an
wuce haɗari sai ya koma siffa
ta asali. Misali hawainiya takan sauya launin jikinta, don ta saje da muhallin
da ta samu kanta a ciki. Takan yi haka ne don ta kuɓuta daga mahara. Idan
ta iske ganye kore sai ta rikiɗa kore, in kuma ƙasa-ƙasa ta ga ni sai rikiɗa ko kuma baƙi-baƙi. Bisa wannan dalili
ne ya sa ake haɗa maganin rikiɗa da mushen hawainiya.
Ita kuwa makwarwa takan ɓace a kasa ganinta,
sabo da ta saje da launin ƙasa da launin gashinta. A nan ita ma
Bahaushe na haɗa maganin layar zana
watan layar ɓata da ita.
RIKIƊA MAI TSAWO: Dabbobi, kan rikiɗa zuwa mutane har su
shiga kasuwa su yi harka tare da ‘yan Adam, a inda suke yin cinikayya. Misali
barewa, da beguwa sukan rikiɗa zuwa Bafulatana. Tunku da kada sukan rikiɗa zuwa kuturu su
shiga cikin mutane suna yin bara.
RIKIƊA TA DIN-DIN-DIN: Ita kuma wata irin
rikiɗa ta har abada. An fi
samun wannan ne a wurin dabbobi irin su maciji musamman irin wanda iska ya rikiɗa zuwa shi. Haka kuma
akan samu irin wannan ga irin mutanen da mayu sukan kama su mayar da su dabbobi.
A mafi yawan lokutta sukan zauna a daji har abada.
RIKIDAR ƁATAR DA SAWU: Wannan irin rikiɗa akan yi ta ne, don
a kawar da hankalin wasu, ko kuma a yaudaresu. Dabbobi da mutane na yinta, ta
fuskar dabbobi akan samu irin su tunku, da barewa, da beguwa. Ɓangaren mutane kuwa,
akan samu a wurin mayu, ko kuma ɓarayi. A lokutta, kuma a wurare da yawa, ɓarayi kan rikiɗa wata halitta, idan
suka ga asiri zai tonu. Kamar yadda ya faru a garin Ilori.
Rikiɗar sauya launin jiki: Akwai
rikiɗa wadda
dabbobi, da kuma wasu mutane kan yi. Waɗannan
dabbobi masu sauya launin jikinsu, babu kamar hawainiya. Ko da yake a wani
lokaci maciji kan yi mele, saboda yawan shekaru watau tsufa, ko ya yi saɓar fatar jikinsa. Haka kuma
akwai wasu dabbobin irin su ƙadangare,
da danginsa sukan sauya fatar jikin su ta hanyar yin saɓa.
Rikiɗar sauya ƙirar
jiki:
Akwai wata rikiɗa wadda
wasu dabbobi, da kuma wasu mutane kan yi. Dabbobi masu yin haka, suna da yawa,
kamar barewa, da tunku, da beguwa. Ko da yake a wani lokaci maciji kan rikiɗa zuwa mutum, saboda tsufa, ko
iskoki su shige shi. Haka kuma akwai wasu dabbobin irin su ƙadangare,
da danginsa. Misali irin su kada, da tsari sukan sauya ƙirar
jikin su ta hanyar komawa mutum.
DALILAN DA KAN SANYA
RIKIƊA
Bahaushe yakan ce komai baya rasa dalili, ko
kuma zai faru ba tare da dalili ba. Don haka dalilan rikiɗa na iya kasancewa na
sarari ko ɓoye tun daga dabba,
ko tsuntsu har mutum ko aljani. Duk wanda ya rikiɗa zuwa wata baƙuwar siffa ta daban,
saɓanin wadda aka sanshi
da ita, to akwai wasu dalilai na sarari ko na ɓoye. Al’adar Bahaushe ta kalli waɗannan dalilai kamar
haka: Ƙwatar rai, ko nuna buwaya, ko biyan wata bukata.
Ƙwatar rai : Akan samu rikiɗa a dalilin ƙwatar rai. Wannan
kuwa na faruwa ga dabba, ko tsuntsu, ko mutum. A mafi yawan lokuta wasu
dabbobin kan rikiɗa ne, don kaucewa
halaka. Ma’ana saboda su da su tsira.
Nuna buwaya (Gagara)
: Akan samu rikiɗa a dalilin nuna
buwaya, ko gagara. Wannan kuwa na faruwa ne ga dabba, ko tsuntsu, ko mutum. Ta
fuskar mutane an fi samun maharba, ko ɓarayi, ko da yake akan ɗan samu bambancin
yanayin hakan.
Biyan bukata: Akan samu rikiɗa wadda kan faru a
dalilin biyan wata bukata. Wannan na faruwa ne ga dabba, ko tsuntsu, ko mutum. A
mafi yawan lokuta hawainiya kan rikiɗa ne, don neman abinci. Takan saje da ciyawa,
ko ta haye rama ta rikiɗa launin ramar, ta
rinƙa
kama ƙwari tana ci. Dangane da ɓarayi kuwa, saboda su ɓatar sawu su yi sata.
ƘARAMAR RIKIƊA
Wannan rikiɗa ita ce wadda ba
cikakkiyar rikiɗa ba (ƙarama ko gajerar rikiɗa). Su uku ne kamar
haka: Saɓar fatar jiki, da
zubar gashi, da sajewa.
Saɓa: ba cikakkiyar rikiɗa ba ce, (ƙarama ko gajerar rikiɗa). Akwai wasu
dabbobi da sukan sauya kama, ta hanyar yin saɓa, a inda fatar jikin su kan saɓule, a saboda wasu
dalilai. Kamar maciji kan yi saɓa ko ƙadangare, ko damo, ko tsari, da sauran
danginsu.
Zubar gashi: tsuntsaye sukan
sauya kamannu ta hanyar zubar gashin jikinsu. Irin wannan ya fi faruwa ne,
musamman idan suna kwanci akan ƙwai kafin su yi ƙyanƙyasa. Ko da yake wasu
sai in ba su lafiya ne suke zubar da gashi.
Sajewa: Ita ma kamar rikiɗa ce, sai dai ba
cikakkiya ba ce, kamar inda dabba kan saje da muhalli. Misali ƙadangare in yana wuri
yakan rune ya saje da launi katangar, ko ɗakin girki, haka shi ma ɓera da kuma gafiya,
da wasu macizai, da kada, da tsari, da jauji.
RIKIƊA A TUNANIN BAHAUSHE
TA MAHANGA AL’ADA.
A al’adance akwai
wani tunani da Bahaushe ke da shi, na cewa wasu dabbobi na iya rikiɗa su koma wani nau’i
na dabbobin da ba irinsu ba. Ko kuma su koma siffar mutum, misali kamar tunku
Bahaushe na zargin sa da cewa yakan rikiɗa ya koma siffar kuturu kuma har ya zo kasuwa.
Baya ga wannan kuma akwai iskoki da kan rikiɗa su koma siffar wasu dabbobin kamar, kare,
da maciji, da ƙadangare, ko mage da sauransu. Bahaushe bai cika yarda ko
amincewa da baƙin kare ba, musamman da dare. Haka wasu ƙadangaru ba, a amince
masu domin ana zargin iskokin kan rikiɗa su zama ƙadangaru.
Akwai wasu mutane
daga cikin masu wasu sana’u da suke rikiɗa wata dabba. Domin su nuna gagara, da ƙuƙuwa akan sana’arsu,
kamar maharba, da masunta, da masu ba da magungunan gargajiya da wasu masu
aikin sarki, kamar yari, da dogarai, ‘yandoka, da hauni, da wasu riƙaƙƙun ɓarayi.
Wannan tunani ya yi
kaka-gida a rayuwar Bahaushe, ana samun jirwayensa a adabin baka da rubutacce. Kamar
a waƙoƙI, da tatsuniya, da al’amara, da tarihi. Tunanin ya ƙara samun goyon baya
daga addinin musulunci. Wannan kuwa ba ya rasa nasaba da wasu bayanai daga
hadisai da suka yi magana akan al’amarin rikiɗa.
DABBOBIN DA KE RIKIƊA.
Bahaushe na zargin
wasu dabbobi da cewa sukan rikiɗa a wasu lokuta, kuma iskoki kan shige su. Su ne kamar
haka: - baƙin kare, da Ƙadangare, da Kada, da
barewa, da baƙar mage, maciji, da damo, da bguwa bushiya, da tsari, da
tunku. Waɗannan dabbobi kan
sauya kama ko kuma su rinƙa nuna wasu halaye na gagara ka buwaya.
BAƘIN KARE: Bahaushe ya camfa,
kuma bai cika yarda da baƙin kare, sabo da alaƙarsa da aljannu. A
wasu lokuta iska kan rikiɗa zuwa baƙin kare, ko kuma su
shiga jikin baƙin kare na haƙiƙa. Don haka ne ko
duka ko jifansa ba a yi. Wannan ya wuce hasashe ko zargi, saboda waɗansu hujjoji da suka
tabbata a wurare, da lokutta da kuma mutane daban-daban. misalai.
Karona da wani baƙin kare
Na dawo yawo da dare na shiga wani lungu sai
naga baƙin kare sai na ɗauki dutse na jefeshi, sai ya gudu ba,a ɗauki wani lokaci ba,
sai naga wani mutum ya bayyanar min. Nan take sai yace kai yaro kar ka ƙara jifan kare ka ji.
[12]
Baƙar mage: Bahaushe bai amince
mata ba sabo da iskoki kan rikiɗa, ko shigeta. Haka kuma a dalilin, Mayu, da ɓarayi, da matsafa kan
rikiɗa zuwa ita. Bayan
wannan kuma akan alaƙanta baƙar mage da cewa dodo ce. Wannan ya
sanya Bahaushe ba ya son ta, ko magensa ta haifi ‘ya’ya, to in har akwai baƙa, sai ya jefar da
ita.
Bushiya: tana da irin nata
zargin da Bahaushe ke yi mata na rikiɗa ko dibilwa. Akwai inda akan kama bushiya a
rufeta da turmi, amma kafin safiya, sai a tarar ta gudu, ko kuma za aji tana
kukan jariri.
Wani Yaro da wata
Bushiya:
A wata
shekara ne a garinmu wasu yara su biyu suka kama bushiya da dare. Bayan da suka
wannan bushiya, sai suka nemi yayi da ƙirare domin su gasa. Suka
dogon lokaci suna gasa bushiyar nan amma taƙi gasuwa. Ɗaya daga cikinsu
watau ɗaya yaron yace, kai
wannan bushiya fa mu haɗura, tun da taƙi gasuwa. Shi kuwa ɗayan yasha alwashin
sai ya gasa ya ci, sai ya tafi ya samo kananzir ya zubawa bushiyar. Ƙyasta ashanarsa ke da
wuya, sai kawai wuta ta kama jikinsa. Aka yi ƙoƙarin a kashe wutar
nan, amma abin ya gagara. A wannan hali ne ta cinye shi ya mutu har lahira”. [13].
Beguwa: ana zargin ta da rikiɗa zuwa mutum, watau
Bafulatana. Mafarauta da yawa sun amince cewa beguwa kan rikiɗa zuwa Bafulatana har
da ƙwaryar
nono a kanta. Takan yi wannan ne idan ta ji motsin mutane musamman mafarauta,
sai ta rikiɗa don ta kifar da su.
Wasu mafarauta musamman waɗanda suke da wankin ido, sukan gane ta.
BEGUWA NA RIKIƊA ZUWA BAFULATANA.
Bahaushe
na zargin beguwa mai ƙaya a jiki da cewar tana rikiɗa zuwa Bafulatana, ta
shiga kasuwa da ƙwaryar nono. Maharba ne kaɗai ke iya gane ta, ta hanyar yawaita
sayen rogo. A wani lokaci kuma in a cikin daji ne sai su rikiɗa fulani su jero suna
hira akan hanya,,Maharba kaɗai ke ganesu. suna yin magani wannan ƙuƙuwa ne ta hanyar zuwa
daji ba wando to in suka yi haka sai su harbe su su yi nasara. [14]
TUNKU: mafarauta sun tabbatar da tunku na rikiɗa zuwa tsoho, ko
kuturu, ko ƙungiyar mata. A mafi yawan lokuta in ya zo shan ruwa, ba
zato ba tsammani, sai ya ji motsin mutane. Nan take sai ya zama tsoho ya
tsuguna kamar zai yi wanka. Yakan zama kuturu har ya tafi kasuwa don ya yi
bara, amma mafarauta na ganeshi ne ta yadda yake sayen kanwa. Da zarar aka ga
kuturu na sayen kanwa, mafarauta kan yi zargin ba kuturu ba ne, tunku ne. Bayan
haka yakan rikiɗa ƙungiyar mata su jero
suna yin surutu kamar sun dawo biki. A nan mafaruta kan ganeshi ne ta hanyar yi
masa kwanto a cikin sako da zarar suka ga mace ta gaba a jerin sai su harbeta.
Maciji: Bahaushe na zargin
maciji da cewa yana rikiɗa ko kuma iskoki na
rikiɗa zuwa maciji, ko
kuma su shige shi. Akan samu irin wannan idan ya tsufa, inda yakan samu wani
kogo itace, ko dutse, ko tsohuwar rijiya ko suri ya zauna. A wani lokaci idan
maciji ya gagara ya riƙa har yakan zama guguwa ya rinƙa tashi.
Ƙadangare: Akan zargi ƙadangare cewar yana
da wuyar sha’ani. Kamar yadda wani Bawan Allah yace; akwai ƙadangare iri huɗu, kamar haka: 1. Na
haƙiƙa wanda iska ya shiga.
2. Wanda iska ne ya rikiɗa. 3. Da wanda yake
na sihiri ne. 4. Ko kuma a sihirce shi.
Wani Aljani ya Rikiɗa ƙadangare
Wata mata ta shiga bayan ɗaki (masai) don ta
biya bukata sai ta ga wani ƙadangare sai kawai ta watsa masa ruwa
wai don ya gudu, bayan ta fito daga bayi sai kawai ta kasa gani watau ta
makance. Aka kai ta asibitoci daban daban amma ba a ci nasara ba, sai wani yace
a yi mata ruƙƙiya. Da a ka kira mai ruƙƙiya ya fara sai wani
aljani ya bayyana ya fara Magana ta bakin matar da ta makance yana cewa; ‘’Ta
shigo bayi ba natsuwa ni kuma ina nan sai na yi gudun kar ta ganni ta tsorata
sai na rikiɗa na koma ƙadangare, amma kuma
sai ta watsa min ruwa to da na haƙura amma daga baya
wasu jikokina suka ƙi haƙuri akan abin da ta yi min shi ne suka
rufe mata ido. Aka ci gaba da ruƙƙiya sai jikokin suka
yi magana. To ashe su biyu ne Hassan da Husaini da ya ya haƙura ya fita amma daya
sai da aka sha wahala amma daga baya ya fita ta warke. [15]
BAREWA; Ita ma ana zarginta
da rikiɗa zuwa Bafulatana da ƙwaryar nono fara
kyakkyawa. Mafarauta na gane ta hanyar lura da Bafulatanar da ta cika sayen
gishiri.
DAMO ; iskoki ke shigar sa,
mafarauta da dama sun yarda cewa, idan damo ya tsufa, iskoki kan shige shi ya
rinƙa
aikata wasu abubuwa na ban mamaki.
KADA; Akan zargin kada da
rikiɗa ko hatsabibanci,
don kuwa, akan samu kada da yakan fito wajen kogi ya rinƙa kashe mutane da
dabbobi, ya kuma koma cikin kogin ko an sanya tarko ba ya kamuwa.
KADA YAKAN RIKIƊA:
Kada kan rikiɗa zuwa tsohon mutum ko kuturu. mu
mutanen Yawuri a zamanin da an rinƙa ganin abin mamaki. Domin
an rinƙa samun wasu lokutta da kada,idan ya rinƙa sai ya rikiɗa ya rinƙa shigowa garin
Yawuri. Babu mai gane haka sai masunta ko maharba don suna da masaniya. kamar
yadda sukan ce matuƙar mutum ya gamu da tsoho wanda ba a sanshi ba watau baƙo. A kan lura da cewa
ko yana da gashin gire,in har babu to lallai kada ne ya rikiɗa ya shigo gari. [16]
Rikiɗa A Adabin Bahaushe: Akwai jirwayen rikiɗa a kusan dukkan
rassan adabin baka, kamar a waƙoƙinsa da tatsuniya da
al’amara da tarihi.
TARIHI: WANI MACIJI
DA ZAKARA A ZARIYA
A Ƙasar Zazzau kuma a
cikin Birnin Zariya an yi wani shahararren Malamin addinin Musulunci, mai suna
Malam shehu na Malam Na'iya. “Wata rana ana cikin karatu a azure (zawuyya) yana
bayar da karatu, sai yara suka fito daga cikin gida da mushen zakara a hannunsu.
A ɗaya hannun kuma da
mushen maciji, sai Malam ya tambaye su ina zaku? Me ya faru?. Yara gaba ɗaya suka ce “ai
wannan maciji ne ya sari zakara ya kashe shi”, sai su kuma suka kashe macijin. Abin
mamaki za su fita da mushen zakara da na maciji, sai Malam yace su ajiye mushen
zakaran su tafi su jefar da mushen macijin. Bayan ɗan lokaci sai kawai
ana cikin karatu, sai ga wani maciji yana janye da mushen macijin da aka jefar
ya shigo cikin zaure. Nan da nan kuma nan take, sai malamin nan ya sanya ɗauko mushen zakara,
ya karɓa ya ajiye a gaban
macijin. Malamin sai ya ce “ga ɓarnar da ya yi mana, ya kashe zakara ne mu kuma muka
kashe shi?. Macijin Sai kawai aka ga ya ɗauki mushen macijin nan ya juya ya tafi. [17]
TATSUNIYA: akwai wasu tatsunniyoyi masu yawa, da
a ka samu jirwayen rikiɗa. Ga misali, kamar
haka: “tatsuniyar barewa ta auri mutum”.
Gata
nan gata nan ku, wata barewa ce sai ta rikiɗa ta zama mace kyakkyawa sai ta ɗauki ɗan kwatashinta ta ɗora a kanta, ta tafi
tsakiyar karofi ta ajiye. Ta ce duk wanda ya jefa ‘yar tsakuwa ta buɗe kwatashin shi ne
mijinta, sai wannan ya ɗauki tsakuwa ya jefa,
bai buɗe ba. Wancan ya jefa
tsakuwa bai buɗe ba, sai aka samu
wani ya jefa ‘yar tsakuwa sai ya buɗe, sai ta ce ta samu miji shi zata aura sai
suka tafi garin ita yarinya wurin iyayenta, za’a ɗaura mata aure da wannan mutumin. Da
aka ɗaura masu aure ta zo
ta zauna a gidan miji. Kullum ranar girkin ta sai a ce ta je, ta ciro kuɓewa a gonar miji ta
yi miya. Da ta je gonar sai ta yar da zaninta, ta yi birgima a ƙasa ta zama barewa. Bayan
haka sai ta yi kiran ‘yan uwanta,sai ta yi waƙa tace:
cikal-cinkal,cinkali
kalaya.
Turmin
‘yankale ya yi fure,ceɗiya.
Tudu na
korar tudu marina.
tudu na
korar tudu da ƙaho.
Ban da
kwatsakwatsan ban da ƙanƙana.
Nan da
nan sai ‘yan uwanta su zo.
Su taro
su ciccinye kuɓewa.
Sa’anan
sai in sun gama sai tafi gida, ita kuma sai ta yi birgima ta koma mutum ta ɗauki zaninta ta ɗaaura sai ta koma
gida ta dinga cewa ni da gangan aka tura nig a shin an ban samo komai ba. To
ran nan sai mijinta ya bita gonar sai ya ganta tana birgima da t agama birgimar
sai ya gat a rikiɗe ta zama barewa sai
yaga ta yi kiran ‘yan uwanta bareyi da waƙa Bareyi suka taru a
gonar jingimduk suka cinye kuɓewar sunna cikin ci sai ya fasa su sai yaga matarsa ta
ganshi ya koma gida sai ta ɗauko kuɓewar ta biyo shi ta tarar das hi a gida yace wacece tace
niceyace ina zakitac ɗaki zani yace a’a
koma daji sai tace taƙI sai ya biyota a guje ya kora ta daji daga nan bat a
sake dawowa ba. [18]
ALMARA: Akwai almarori waɗanda ke ɗauke, ko tabbatar da
rikiɗa,kamar almarar biri.
ALMARAR BIRI
Akwai
inda aka ce wata Bafulatana ce ta dawo kasuwa sai yaronta yana jin kashi, ko da
ta sauke shi ya yi kashin ya gama, sai ta ɗauko waina daga cikin kayanta. Bayan da ta ɗauko sai ta karya
biyu ta share masa kasha da wainar nan take sai ya zama biri. Daga nan ya kama
tsalle ya faɗa daji da gudu, ya
bar tan an tsaye tana mamaki kuma tana kuka. [19]
WAƘOƘIN BAKA:
Akwai
mawaƙan baka
da suka yi waƙoƙi da a
ka samu jirwayen rikiɗa. MISALI: Danlami
Nasarawa a waƙar Maigari Amadu
Gindi: In ɓarawo ya zama kura
Mai gari zai zama
zaki
In ɓarawo ya zama ɓera
Mai garizai zama
kyanwa
In ɓarawo ya zama tsuntsu
Mai gari zai zama
shaho
Jagora: Ya buge shi ya ɗaure
: ya buga masa ankwa
: Ya miƙa ga yari.
: Ya shigo yana yin
shawagi
Gindin: Haka ne yara, duniya,
zaman ‘yan marina ne
Mai komo Dan Tudun Doki (ilaje)
Ilaje ya ga mugun
zaki
ko da ya harbe shi
Mugun zaki ya zaburo
zai kasshi Ilaje ya zam dawa
Gambu mai kiɗin ɓarayi (Nazaƙi ) inda Inuwa Ɗan Maɗacci ya tare shi akan
hanya a lokacin da suke tafiya tare tudun
Jagora: kora jakkai kora jakkai
Nic ce ga kura can tsugunne
Yac ce, bar su su wuce kar ka damu
Ai ba kura ta ba Gaambo
Muhd inuwa na ka bi na
Duk bai da rabo ɗiba ga baina,
Sai dai wata rana na gaya ma.
Duk bar shi ya ƙare ƙuƙuwa tai,
Sai ya hita hili in buge shi,
In bar shi ga kolaye su canye.
RIKIƊA A RUBUTATTACCEN
ADABIN BAHAUSHE;
Al’amarin rikiɗa a tunanin Bahaushe
ba ƙarami
ba ne. Domin kuwa wannan tunani ya yi naso a rayuwar Bahaushe gaba ɗaya. Wannan kuwa ya
haɗa har da rubutaccen
adabi. Kamar zube watau ƙagaggun labarai. Akwai littattafai irin su Magana jari ce
na 1 da 2 da na 3.
Labarin ‘Yan birni da
Ɗan ƙauye,
Wani Baƙauye ne ya shigo gari
da jakinsa,sai ya ga wani mai wasan nakiya da garma (ɗan hoto) ya ta yin
wasa. Baƙauyen nan ya saki baki yana kallo yana riƙe da jakinsa. zuwa
can sai wasu yan birni suna zaune. wani daga cikin yan birnin nan ya ce yanzu ƙwace jakin can wuri
muzin can ba zai yi wuya ba. Abokansa suka ce haba wannan ba zai yiwu ba wane
kai saboda a ƙarfi dai ba zaka iya ƙwacewa a hannunsa ba,
kuma yan zu rana ce ba dare ba. shi kuma sai yace ku biyoni da isarsu sai ya saɓule igiyar dake ɗaure a wuyan jakin Baƙauyen nan ya rataye a
wuyansa. Ya miƙawa ‘yan uwansa jaki suka tafi da shi. Baƙauye bai san abin da
ke gudana ba. Ko da Ɗan birni ya lura abokansa sun ɓace, sai ya fara
daddagewa yana turjewa Baƙauye kuwa sai jan igiya yake yi. Bayan da ya ji abin ya
gagara,sai ya waiwayo da niyyar ya bugi jakinsa sai ya ga mutum ɗaure da igiya a wuya
mamaki ya kama shi. Baƙauye ya ka da baki y ace me yake faruwa? Dan birni ya buɗe baki yace ;Ni ne
jakinka,tun farko ni mutun ne wataran haukar ƙuruciya ta ɗebe ni na sha giya na
zagi mahaifiyata,sai ta tsine min shi ne na koma (rikiɗa) jaki ina ganin ta
yafe min ne Baƙauye ya ji tausayinsa ya sake shi yace kar ka ƙara irin wannan. [20]
RIKIƊA TA BAIWA DAGA ALLAH:
Akwai rikiɗa ta baiwa daga Allah
kamar Mala’iku da iskoki da kuma wasu dabbobi ko tsuntsaye. Rikiɗa ta baiwa, Allah (SWT)
Ya bai wa Mala’iku wata baiwa ta sauya (rikiɗa) halittarsu ta asali zuwa wata halitta ta
daban. Kamar in da suka rikiɗa zuwa mutune. Haka kuma su ma iskoki suna da wannan
baiwar sauya halittarsu ta asali zuwa mutum, ko dabba, ko tsuntsu. Kamar irin
su tunku da barewa,da beguwa,da hawainiya da makwarwa.
DANGANTAKAR
DABBOBI DA ISKOKI.
Iskoki a wajen Bahaushe wasu halittu ne masu
kama da mutane ta fuskar halittarsu, da surarsu, da ayyukansu, da al’adunsu, daɗabi’unsu, da
harshensu, da siyasar rayuwarsu, da dai makamantansu. Bahaushe ya yi imni da
samuwarsu a kowanne tudu, da rahi na bangon duniya, wuraren da ake samun ‘yan
Adam, da wuraren da ba’a samun su. [21]
Bisa
ga bayanan da suka gabata, muna iya cewa, iskoki wasu halittu ne waɗanda Bahaushe ya yi
imani da su, duk da yake ba ya ganinsu. Al'adar Bahaushe ta tabbatar da
samuwarsu, tun kafin zuwan musulunci. Haka kuma, addinin Musulunci ya zo, sai
ya tabbatar da samuwar su. Wannan ya ƙarawa Bahaushe ƙarfin gwiwa a kan
tunaninsa, a game da iskoki.
“
Hausawa na danganta dabbobi da yawa da iskoki saboda irin siffarsu,da ɗabi’unsu, da
ayyukansu. Iskoki kan sauya siffarsu zuwa manyan dabbobi ko ƙanana. Waɗannan dabbobi
Bahaushe na yi masu kallon iskoki ko wakilansu: a. Baƙin kare. b. Baƙar karya. c. Farin
kare. d. Baƙar mage. e. Baƙin Jaki. f. Farar
kura. g. Ayyu. h. Tsohon Kada. i. Tsohon Damo. j. Ani. Idan manyan Maharba ko
Masunta suka karo da waɗannan dabbobi sukan ɗan raga masu,gudun
kada su faɗa masu iska ya ɗauki fansa. Duk
watadabbar da ake has ashen iskokina shigar burtu da siffarta,idan za’a
farauceshi sai an shirya”. [22]
Bahaushe na da hasashen cewar akwai wata alaƙa a tsakanin iskoki
da wasu dabbobin gida da dabbobin daji. Wannan dagantaka akwai ta sarari akwai
kuma ta ɓoye. A al’adance
akwai wasu dabbobi da ke da wasu halaye da suka saɓa da na sauran
dabbobi. Akwai wasu tattabaru da iskoki sukan shige su, sai mai su yakan gane. Bisa
ga bayani game da alaƙar dabbobi da iskoki ana iya raba su kashi-kashi ko
fuska-fuska, kamar haka: A wani lokaci iska kan rikiɗa ta koma wata
halitta, don ta tsoratar da wani, ko don ta ɓatar da kama. A wasu lokutta akan gane sabo
da ɗabi’a da ta saɓa da ita irin dabbar
da iskar ta koma, amma a wasu lokuttan ba a gane su. Haka kuma, iska kan shige
dabba ko tsuntsu, saboda sha’awar da dabbar ta ba su, ko a sanadin zama wuri ɗaya da iskar ko kuma
tsufa.
RIKIƊA MAI ALAƘA DA ISKOKI
Iska ba
abin da zai yi idanun mutane su gan su ba ne ƙuru-ƙuru. Iskoki idan suna
son su ziyarci mutane cikin siffar da ba zasu tsorata su ba,suka rikirkiɗa da yawa. Ba
Bahaushe kaɗai ke da imanin cewa,
iskoki na rikiɗa. Labarawa,da
Turawa, da mutanen Asiya,da dukkanin Ƙabilun duniyar baƙar fata suna da
wannan tunanin. Iskoki suna sauya kama su yi shigar burtu su kutsa cikin mutane
da siffa irin ta: a. Mutane,b. Dabbobi, c. Kwari. [23]
Akan samu dabbobi, ko
tsuntsaye su rikiɗa su sauya halitta
daga tasu ta asali zuwa wata ta daban. Wannan bai rasa nasaba da hulɗa da iskoki, da farko
iskoki kan shiga jikin wasu dabbobin, sai su zama gagararru, ko shu’umai. Bahaushe
na zargin dabbobi irin su baƙin kare, da ƙadangare, da baƙar mage, da maciji,
da sauransu.
Mafarauta sun
tabbatar da cewa duk a cikin namun daji babu mai hatsabibanci irin gwanki. Domin
idan aka harbeshi ba ya faɗuwa sai ya yi gudu mai nisa. Ko da kuma in ya faɗin, sai a tarar yana
zaro harshe yana lasar ƙasa, ko ciyawa, kamar bai mutu ba. Ko ka ga ƙudan zuma na fitowa
daga kunnensa, ko kuma kan gwankin ya ƙi yankuwa da dai
sauransu. A waƙoƙin bakan Bahaushe, akwai mawaƙa da suka nuna hakan.
Misali: Alhaji Mamman Shata a waƙar Widi Ɗan Usman Salgare
yace;
Jagora: Baba kan kada mai ƙwari,
: kan gwanki mai rangwagwan,
Gindi: Widi Ɗan Usman Salgare.
Wasu dabbobin idan
suka tsufa, shekarunsu suka yi yawa iskoki kan shigesu. Kamar raƙumi, da maciji, da ƙadangare, da kada, da
tsari. A mafi yawan lokuta, idan waɗannan dabbobi suka tsufa sai a rinƙa nuna wasu halaye na
daban. Kamar maciji da zarar ya tsufa sai ya zama gamsheƙa ba wuya iskoki sun
shigeshi. Daga nan sai ya zama masha-ruwa ko bakan-gizo a inda zai samu
wata tsohuwar rijiya ko suri. Haka kuma wani macijin yakan zama guguwa shi ma
alaƙar
iskokin ne.
ISKOKI
KAN RIKIƊA ZUWA
DABBA.
Allah Ya bai wa iskoki wata baiwa,wadda zasu
iya rikiɗa komai
suka ga dama. Domin sukan rikiɗa zuwa
mutum, ko dabba, ko tsuntsu.
WANI ANGO DA WANI
MACIJI
A zamani Manzon Allah Annabi Muhammadu (SAW) An
fita da sahabbai ana aikin gayya, sai wani matashi Ango wanda bai daɗe da yin aure ba. Ya
nemi izini daga wurin Manzon Allah (SAW) cewar yana son zuwa gida. Annabi (SAW)
Ya ba shi izinin, ya tafi gida ke nan sai ya tarar da amaryarsa a waje tana
tsaye. Da isowarsa, sai ya tambaye ta meke faruwa ya ganta a waje? Amaryar tace
ya shiga ɗaki maciji ne. Ko da
ya shiga,sai ya ga wani maciji ya yi gammo a kan gado. Wannan matashi yana fita
sai ya ɗauko sanda,don ya
kashe maciji. Bayan ya kai wa maciji duka da sanda. Ba a san wanda ya riga
mutuwa ba tsakanin maciji da Angon ba. Wannan labarin na isowa wurin Annabi (SAW)
sai ya ce, ku guji kashe macizai a garin [24]
RIKIƊAR MUTUM ZUWA DABBA
Akwai rikiɗa wadda wasu mutane
kan yi daga mutum zuwa dabba. Wannan rikiɗa kan faru ne a sanadiyyar, ƙwatar kai, ko nuna
buwaya, ko ɓatar da sawu. Mutanen
da aka fi sani da irin wannan hali, su ne, kamar haka: Maharba, da mayu, da
masu dabo da sauransu. Akwai wasu mutane da ya zama masu al’ada, su rikiɗa zuwa dabba. Kowanne
dalilan da kan sanya su haka ya bambanta. Kamar a Ƙasar Birnin gwari
akwai ƙabilar Kamukamawa (kamuku) , da ƙabilar Katafawa su
duka a jihar Kaduna, sukan rikiɗa zuwa kura. A Ƙasar Katsina kuma a
gundumar Ɗanmusa, da akwai masu rikiɗa kura. A Ɗandume akwai mutane
idan suna biki sukan rikiɗa kura, ko zaki ko
kuma yaro ya koma tsoho tukuf. A Ƙasar Gaidam a jihar
Yobe, nan ma akwai masu rikiɗa kura da dai sauransu.
WATA MATA TA RIKIƊA BAREWA
A wani ƙauye a Ƙasar Ilori ta jahar
kwara wani maharbi ya fita farauta a daji, sai kawai ya ga wata barewa. Nan
take sai ya harbe ta, ta ɗan ƙara gudu kaɗan sai ta faɗi. Shi kuwa ya nufi
barewa da ta faɗi tana shure-shure da
ƙafafunta.
Da isarsa sai kuma barewa ta rikiɗa tsohuwar mace. Maimakon ya ga barewa sai ga
mace tsohuwa matacciya. Nan da nan ya ruga da gudu zuwa gidan sarki. Bayan da
sarki yaji abin da ya faru sai ya tura maharbin nan zuwa ofishi ‘yan sanda. Ya
yi wannan dabarar ne don gudun kar jikokinta su ɗauki fansa ta hanyar kai masa hari don
su kasheshi. [25]
RIKIƊAR SIHIRI, TSAFI, DABO, DA
RUFA-IDO.
Kalmar sihiri baƙuwar kalma ce daga
harshen Larabci, mai asali daga “sihir. ” Wannan kalma na nufin aikata wani abu
wanda ya saɓa wa rayuwa ta haƙiƙa. A da can Bahaushe
na kiran sihiri da sunaye masu yawa da suka haɗa da tsafi, ko dabo, ko rufa-ido, ko
kanbulku da sauransu. Akwai misalai da yawa da suka shafi rikiɗa da suka faru a
wurare da yawa. Misali:
MUTANE MASU RIKIƊA ZUWA BUNSURU
Muna garin Patakwal akwai wasu ‘yan Arewa waɗanda sukan rikiɗa zuwa taure (bunsuru).
Abin da yake faruwa kuwa shi ne, idan suka ga kirsimati ta matso, kuma ba su da
kuɗi, sai su shirya a
tsakaninsu wani ya rikiɗa zuwa bunsuru. Ɗaya daga cikinsu sai
ya ɗaura masa igiya yana
zagayawa a cikin gari a matsayin talla. Idan har wani ya sayi bunsurun ya kai
gidansa ya ɗaure, sai kawai dare
ya kwance kansa ya gudu. Irin wannan abu ya sha faruwa a garin Patakwal. [26]
RIKIƊAR MASU DABO: Rikiɗa masu dabo, ana iya
cewa ta kasu kashi biyu, akan rikiɗar da wani abu ya koma dabba, ko tsuntsu. Ko
a rikiɗar da wata dabbar
zuwa wata, ko tsuntsu ya koma wani tsuntsu ta hanyar dabo. Akwai kuma inda su
da kansu sukan rikiɗa su koma zuwa dabbar
ko tsuntsu. Duka wannan na faruwa ne bisa dalilin nuna buwaya ko gagara. Misali.
ANA MAYAR DA TUSHIYAR DAWA ZAKARA
Tabbas irin wannan ta sha faruwa ko kuma ince
yana faruwa har ya zuwa yau. Matuƙar a kace sallah ta
kusa an fara hada-hadar sallah. Lallai in mutum bai yi sa’a ba to zai sayi
tushiyar dawa a matsayin zakara. Abin da ke faruwa shi ne, akwai wasu mutane da
suka ƙware wajen dabo. Waɗannan mutane sukan samu tushiyar dawa, sai su
cika kwando su yi wani sidabaru. Nan take sai tushiyoyin dawar nan su koma
zakaru. Wani abin mamaki kuma shi ne ko mutum ya sayesu, ba za su koma tushiyar
dawa ba, har sai ya kai gida. [27]
RIKIƊAR KANBULKU: Wata irin rikiɗa ce da wasu mutane
ke yi mai kama da rufa-ido. A inda zaka ga wata dabba ta nufoka, amma kuma ba
ita ba ce. Wannan rikiɗa akan yi ta ne don
nuna gagara da kuma firgita abokan gaba. Wasu lokuta akan yi ta ne a wararen
tararruka na biki, kamar kalankuwa, taron daba, ko bikin nuna amfanin gona, ko
farauta tsakanin wani gari da wani gari. Ko da yake akan yi irin wannnan rikiɗa ne a Ƙasar Hausa da maƙwabtansu. To amma
kuma akan samu ‘yan bambance bambance daga wannan gari zuwa wancan.
a
RIKIƊAR MATSAFA: Akwai rikiɗa wadda matsafa kan
yi idan suka tashi yin tsaface-tsafacensu. Wani lokaci sukan yi ne don nuna
buwaya, ko fifiko ga junansu. A wani lokaci kuma sukan yi domin neman biyan
bukata ga iskokai ko abin bauta. Akwai wasu matsafa waɗanda kan rikiɗa da daddare zuwa
wata dabba ta hanyar surkulle ko saddabaru, da sukan yi.
RIKIƊAR MAYU: Mayu kan rikiɗa zuwa wata dabba, ko
kuma su rikiɗar da kurwa wani
mutun da suka kama zuwa wata dabba ko tsuntsu. Akan samu irin wannan ne idan
maye ya so ya ɓatar da sawu, sai ya
sanya kamannu ya rikiɗa zuwa wata dabba
kamar kura, ko zaki, ko mage, da sauransu. Bayan wannan mayu kan rikiɗar da kurwar mutumin
da suka kama, idan basa son cinyeshi sai su mai da shi wata dabba ko tsuntsu. “Ni
ina zama kura ne, shi kuma yana zama zaki”. Sule Butu wushishi (2012) D V D
Plate mai kama mayu da cire maita.
RIKIƊAR MAHARBA: Akwai wata rikiɗa mai dangantaka da
sihiri, ko tsafi, ko dabo, wanda Maharba kan yi, don su kuɓuta daga wani haɗari da suka tsinci
kansu a ciki. Misali in suka gamu da wata dabba mai haɗari. A wani lokaci
kuma idan maharbi ya so ya nuna gagara ko kuma wani maharbi na son ya faɗa masa ko halakashi,sai
ya rikiɗa ya koma wata dabba
don ya tsira daga shairin abokin a dawa.
RIKIƊAR ƁARAYI: Ɓarayi da suka riƙa (gagara) , kan rikiɗa wata dabba. Akwai
dalilan da kan sanya su rikiɗa, kamar shiga runtsi (hatsari) kamar zasu halaka sai su
rikiɗa. Wasu kuma in suka
so shiga wani gida sai su nuna buwaya. Wasu kuma sai an kama su sai su ɓace. Tunanin Bahaushe
game da rikiɗa da dabbobi kan yi
zuwa wata dabba ko iskoki su rikiɗa zuwa dabba, ko mutane su rikiɗa zuwa dabba. Babu
jayayya akan haka,saboda abin har yanzu yana faruwa.
SHIGAR BURTU: Ita wannan ba za’a
kira ta rikiɗa ba, sai dai a ce
ba-saje. Domin abin dake faruwa shi ne, maharba kan samu kan wani tsuntsu wanda
ake kira burtu. Bayan sun ɗaura shi a jikin wata sanda sai kuma su ɗaura a kansu sannan
su lulluɓe jikinsu da wani
mayafi. Dabarar da suke yi a nan ita ce, zasu rinƙa duƙawa suna duƙar da kansu kamar
yadda tsuntsaye ke yi. Irin wannan shiga kan yaudari tsuntsaye su saki jikinsu
su yi zaton wani tsuntsu ne ɗan uwansu yake yin kiwo. A irin wannan lokacin ne maharba
kan mamayi tsuntsaye su harbesu, su kamasu. A wani lokaci kuma idan maharba
suka shirya biki sukan yi wasan burtu, don kawai su nuna buwaya da kuma cewa su
‘yan gado ne.
NAƊEWA.
A wannan muƙala ta ƙunshi wasu bayanai, a
kan irin yadda Bahaushe ke kallon rayuwar dabbobi da tsuntsaye. Ta fuskar abin
da ya shafi rikiɗa a tunaninsa. Wannan
irin matsayi ne har ya haifar da Bahaushe ke alaƙanta wasu ɗabi’u waɗanda akan yi tarayya
tsakanin ɗan Adam da dabbobi da
tsuntsaye. Bayan wannan muƙala ta kawo bayanai game da ma’anar
rikiɗa da ire-irenta, tare
da dalilan dake yin sanadinsu. Haka kuma muƙalar ta dubi irin
yadda Bahaushe yake alƙanta tasirin iskoki ga dabbobi da tsuntsaye.
Bisa dogaro da wasu
hujjoji da aka samu ta fuskar al’ada, da addinin Musulunci sun ƙara ƙarfafa tunanin
Bahaushe. Bayan haka kuma tare da duba wasu rassa na adabinsa, don ƙara wa bayanan da aka
kawo a wannan bincike, turaku. Wannan muƙala ta fito da wasu
abubuwa waɗanda a baya ba a damu
da su ba. Waɗannan abubuwa kuwa
sun haɗa da: rikiɗa, da ire-irenta, da
dalilai da kan sa a yi, da rikiɗar dabo, da kanbulku. Tare da gano cewar ana yin magani
da naman wasu dabbobi ko tsuntsaye don a rinƙa rikiɗa. Misali naman wasu
dabbobi kamar hawainiya, da kuma tsuntsaye irin makwarwa.
MANAZARTA.
Abraham R. C. (1947) Dictionary of the Hausa
Language, London Hodder &Stoughton
Bargery. G. F. (1993)
A Hausa-English Dictionary andEnglish-Hausa
Vocal Amadu Bello University Zaria.
Bello M (2011) Mahaɗin Dabbobi A
Magungunan Hausawa M. A. Hausa Jami’ar Usman Fodiyo Sakkwato.
Bukar. B. A. ( 2008) Mu
Yangidan sarautar Macina,muna da alaƙa ta jini da
Jaridar Leadership Hausa.
Bunza A. M. (2006)
“Gadon Feɗe Al’ada”,Tiwel Nigeria Limited
Lagos.
Bunza A. M. (2009)
“Narambaɗa”,Ibrash Islamic
Publication Centre Limited Lagos
Bunza A. M (2011) “Kura
a ma’aunin Adabin Hausa”, Muƙala.
Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua a Katsina
Haruna A. (2010) “Maharbi
ya harbe wata tsohuwa a matsayin
Barewa”. Jaridar Aminiya.
Kutama. M. (2008) Wata
budurwa ta rikiɗa zuwa macijiya a
Fatakwal.
Jaridar Aminiya.
MaiYama. U. H. (2008)
Sata a zamantakewar Hausawa. Nazari a kan Waƙoƙin Ɓarayi Na Muhammadu
Gambo Fagada. Ph. D. Hausa.
Usman Ɗanfodiyo university
Sokoto.
Mu’azu. A. H. (2009) “Gurbin
Dabbobi da Ƙwari a cikin Waƙoƙin Baka na Hausa”.
M.
A Hausa Proposal. Usman Ɗanfodiyo University, Sokoto.
Mahe I.
A (2008) “Amfani da Dabbobi a fagen gina Adabin Hausa”.
M. A. Hausa. Bayero University Kano.
[1]
Encarta Softwire English Dictionary (2009) :
[2] A
dubi Ƙamus mai suna Almaurid na Ingilishi zuwa
Arabiyya. AlƊaba’at Al-Hadiyata
Asharat (eleventh edition) , 1977, Shafi na 681.
[3] A
dubi A.A.Dunfawa “Tunanin Bahaushe a cikin Littafin Ruwan Bagaja” Shafi na biyu
cikin Special Research Project in Humanities,2013, U.M.YU.Katsina.
[4]
Oxford Advanced Learner’s Dictionary Oxford New York (6th edition) 2000,
pg 872,
[5].Bargery,
G. F. (1993) A Hausa-English Dictionary
and English-Hausa Vocabulary Ahmadu Bello University Zaria.
[6]
Encyclopedia Britanica Volume iv page 350
[7] A English-Hausa Dictionary
Skinner (1970) N.N.P.C. Zaria.
[8]
Hornby.A.S (2006) Oxford Advanced Learner’s Dictionary University Press NewYork
[9]
ENCARTA Softwire English Dictionary2009
[10] Ƙamusun Hausa B.U.K. ( 2006).
[11]Oxford
Advanced Learner’s Dictionary Oxford New York (6th edition) ( 2000) 739
[12]
Sa’idu Abubakar hira da shi a bakin Kasuwar Sati Kaduna 18/6/2012.
[13]
Sulaiman Muhammed hira da shi a Kasuwar sati Unguwar Dosa Kaduna laraba
17/4/2013.
[14]
Baturen Dutse Wusasa Zariya Sarkin Baka KSMC Rediyon jahar Kaduna
[15] Alasan Muhammad Kano
hira da shi a garin Sokoto.22/7/2004
[16]
Muhammad Dahiru Yawuri hira da shi a Runji Sambo Sakkwato.10/1/2013.
[17]
Hira da Idris Shu’aibu Gimba a Kwalejin Tunawa da Sardauna Kaduna 23/6/2009
[18]
Yahaya I.Y. (1971) “Tatsunniyoyi da Wasanni”, Oxford University
Press,Ibadan.
[19]Yusuf
Sadau hira da shi a Bakin Kasuwar Sati unguwar Dosa Kaduna 23/8/2012
[20] Abubakar Imam Magana
jari ce littafi na I,1937.N.N.P.C.Zaria.
[21]
Dubi Littafin Gadon Feɗe al’ada na Bunza AM (2006)
[22]
Bunza AM (2006) Gadon Feɗe al’ada
[23]
Dubi littafin Gadon feɗe al’ada BunzaAM (2006)
[24]
Imam Malik littafin muwaɗɗa malik
[25]
Haruna A. (2010) “Maharbi ya harbe wata tsohuwa a matsayin Barewa”.
Jaridar Aminiya.
[26]Jauro Muhammad hira
das hi Unguwar D osa 17/12/2012
[27]
Malam Jafaru Kano hira das hi a kasuwar sati Unguwar Dosa Kaduna 13/10/2012
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.