NA
Mu’azu
Sa’adu Kudan
TAKARDAR DA AKA GABATAR A KWALEJIN NAZARIN HARSHEN LARABCI DA ADDININ MUSULUNCI TA SHABABIL ISLAM UNGUWAR DOSA KADUNA, 16 SATUMBA 2011.
SHIMFIƊA.
Kalmar
riga-kafi kalma ce mai harshen damo, watau mai ɗauke da ma’anoni fiye
da ɗaya.
Bahaushe kan yi amfani da wannan kalma a wurare da yawa, kuma ta fuskoki
daban-daban.
RIGA: - Asalin gaɓar kalmar ta farko ta fara ne da “Riga” mai nufin ka shirya wa
wani abu kafin zuwansa, watau kafin faruwar wani abu ko ciwo to ya iske ka
cikin shiri, kamar ka tanaji magani kafin zuwan ciwon, ko kuma ka kawar da wani
abu da zai yi sanadin ciwon, ko kaucewa wani abu da zai jawo maka ciwon. Kamar
tsafta, riga-kafi ce ga cututtuka, barin gardama riga-kafi ne ga husuma (faɗa) da sauransu.
KAFI: - Gaɓar kalma ta biyu ta samo asali ne daga wani abu da Bahaushe ke yi
da ake kiransa da “kafi”, shi kuwa wasu dabarbaru ne da ake yi don neman tsari
musamman gida da iyali. Mai gida kan harhaɗa wasu saƙe-saƙi da ganyayyaki da sassan jikin wasu dabbobi ko tsuntsaye don haɗa wannan magani, don kariya
daga ɓarawo,
hari, gobara da sauran hatsararruka.
Bisa
bayanin da ya gabata, muna iya cewa, idan Bahaushe yace ka yi riga-kafi, yana
nufin ka ɗauki wani mataki na hana aukuwa ko faruwar wani mugun abu, kamar
ciwo da makamantansu. Musamman ta fuskar Magana ko kula da rayuwa ta hanyar yin
kaffa-kaffa tare da lura.
GABATARWA.
Da
sunan Allah Mai rahama Mai jinƙai, Mai kowa, Mai komai,
Mai aikata abin da Ya so, ga wanda Ya so, a sadda Ya so a yadda Ya so, ko ana
so ba a so dole bayi su so. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban
halittu Annabi Muhammadu, da alayensa da sahabbansa.
Kamar
yadda ake yin riga-kafin ciwon shan inna, ƙyanda,
mai baushe (amai da gudawa) , kuturta da sauransu. Ni kuma a nawa tunanin sai
na ga ya dace mu yiwa kan mu riga-kafin wasu abubuwa guda biyar, su ne kamar
haka: -
1- RIGA-KAFIN
CIWON HAUKA GA MATA.
1. Kasancewa
cikin tsarki.
2. Lizimtar
ambaton Allah.
3. Kama kai
(natsuwa ko a shiga bayan ɗaki).
4. Nisantar
kaɗe-kaɗe.
5. Nisantar
bayyana tsiraici (jiki gaba ɗaya).
6. Kyautata
niyya (Kishi da mu’amulla).
7. Lura
da ƙunzugu.
8. Mayar da
duk al’amari ga Allah (rungumar ƙaddara).
9. Kawar da
dogon tunani.
2- RIGA-KAFIN FAƊAWA WUTA.
1. Kyautata
tauhidi.
2. Mallakar
zuciya.
3. Yawaita
Istigfari.
4. Yawaita
Karatun Ƙur’ani.
5. Girmama
miji da mahaifa.
6. Gujewa
butulci da rainuwa.
7. Tsare
Allah.
3- RIGA-KAFIN
LALACEWAR ‘YA’YA.
1. Samun uwa
ta gari.
2. Ambaton
Allah yayin kwanciya.
3. Kame
harshe daga iyaye zuwa ga ‘ya’yansu.
4. Tarbiyya
mai kyau.
5. Addu’a
ta ƙwarai zuwa ga ‘ya’yansu.
4- RIGA-KAFIN
MUMMUNAN KISHI.
1. Imani
(Maganar Allah, Ƙaddara).
2. Nisantar
jita-jita.
5- RIGA-KAFIN
ZUWA GIDAN BOKA (MALAMIN TSUBBU).
Bayan
haka, wannan riga-kafi ya zama mana dole, mu kula da shi mu tsare, don ya zama
kamar maganin da Bature ke ce masa “Psycho-Theraphy”, (Magani
ta hanyar lallashi da shawarwari). Tabbas al’ummar mu na matuƙar buƙatar wannan magani, mazan mu da matanmu. Wannan dalili ne yasa na
kira wannan Muƙala da suna “Riga-Kafi”.
Bugu
da ƙari, wannan muƙala ta ɗan taɓo wasu abubuwa ne ba wai an
zurfafa ba, sai dai kawai don tunatarwa da faɗakarwa, domin kuwa dukkan abubuwan nan a sarari suke, kuma an
sansu, sannan ana aikata su.
A ƙarshe, ina fata wannan muƙala ta zama kamar allura ce
ta magance waɗannan matsaloli a cikin al’ummar mu gaba ɗaya amin.
1. RIGA-KAFIN
CIWON HAUKA GA MATA.
MA’ANAR HAUKA.
Hauka
wata cuta ce da kan kama mutum a sanadiyyar naƙasar
da ƙwaƙwalwa ta samu, wanda kan sanya tawaya ko raunin hankali, da na
tunani, ko kuma gushewarsu gaba ɗaya. Bisa dalilin ciwon yana kama ƙwaƙwalwa ne ita kuma a kai take, sai ace ciwon ya hau kai daga nan ya
koma ya hau ka = ya koma “hauka”. Mai wannan ciwo ana kiransa da mahaukaci idan
namiji ne, mahaukaciya idan mace ce, mahaukata idan suna da yawa (jam’i).
Hauka
nau’i – nau’i ce dangane da sanadi ko ɗabi’un mahaukaci kamar haka: -
Ire-iren
hauka (Sanadoji). Ire-iren hauka (Ɗabi’un
Mahaukaci).
1. Haukar
Gado. 1. Haukar dariya.
2. Haukar
Sammu. 2. Haukar Sambatu.
3. Haukar
Iskoki. 3. Haukar kurum/kawaici.
4. Haukar
camfi. 4. Haukar kuka.
5. Haukar haɗari. 5. Haukar yawo (jewaɗe).
6. Haukar
Gigita. 6. Haukar hagaga.
7. Haukar
Damuwa. 7. Haukar Motsuwa.
8. Haukar
zamani. 8. Haukar din-din-din.
Bisa
ga al’amarin mata akan ga ciwon hauka, ana iya cewa, haukar iskoki (gamo) , ko
ta sammu, ko ta kome, ko ta damuwa. Waɗannan sune aka fi samun mata masu yawa suna fama da su fiye da
sauran nau’o’in ciwon hauka. Sakamakon fahimtar haka ne yasa na ga ya dace,
mu ɗan
tsakuro wasu matakan kare kai a matsayin riga-kafi.
Ya
kamata mata su kiyayi zuwa wurin ƙazanta ba tare da ƙwaƙƙwaran dalili ba, kuma dole ne su rinƙa
bin ƙa’idojin da shari’a ta tsara game da shiga bayi da kuma wasu
matakai kamar haka: -
1. Kasancewa
cikin tsarki.
2. Lizimtar
ambaton Allah (Zikiri).
3. Kama kai
(natsuwa wajen shiga bayi).
4. Nisantar
kaɗe-kaɗe.
5. Nisantar
bayyana tsiraici, gashin kai da jiki gaba ɗaya.
2- RIGA-KAFIN FAƊAWA WUTA.
1- Kyautata
Tauhidi: - Babban abin da ya
kamata mutum Musulmi ya yi a rayuwarsa shi ne kyautata tauhidi, watau ya
inganta imaninsa ta wajen kaɗaita Allah tare da kaucewa yi masa shirka, watau haɗa Allah da wani wajen
bauta, ko neman taimako ko tambaya.
Wannan
kuwa zai ƙudurta ne tun daga zuciya ya zuwa harshe, wato ya furta da baki,
sannan kuma ya aikata da gaɓoɓinsa.
2- Mallakar
Zuciya: - Mallakar zuciya na nufin
mutum ya ƙirƙiri ko sanyawa zuciyarsa linzami, watau ba komai da zuciyarsa ta
raya masa ba ne zai bi ko aikata ba. Dole ne ya yi ƙoƙari ya riƙa cijewa ko kaucewa tare da
danne zuciyarsa musamman in yayi fushi, ya daure ya danne fushin ya yafe in aka
saɓa masa,
idan sha’awa ta taso masa ya dage kar ya saɓawa shari’a ya tsaya ga matarsa.
Bayan
wannan kuma, idan harkar abin duniya ne da suka shafi kuɗI da sauran tarkacen
duniya, kar ya bi son zuciya ya faɗawa haramun. Ya tilastawa zuciyarsa aikata alheri da sauran
ayyukan ibada.
......... الا وإن فى الجسد مضغة, إذا صلحت صلح الجسد كله,
وإذا فسدت فسد الجسد كله, ألا وهي القلب. رواه البخارى ومسلم.
……… To haƙiƙa a cikin jiki akwai wata tsoka, idan ta gyaru duk jiki zai gyaru,
idan kuma ta ɓaci duk jiki zai ɓaci, watau ita ce zuciya. Buhari da Muslim ne suka ruwaito.
3- Yawaita
Istigfari: - Mutum ya yawaita Istigafari
safiya da maraice, saboda shi istigafari yana kankare zunubi kuma yana jawo
alheri, sannan kuma yana sanya Allah Ya so mutum. Istigfari yana sanya mutum ya
zama abokin gaba ga shaiɗan saboda shaiɗan zai rinƙa jin haushin mutum, domin
ko ya sanya shi ya yi saɓon Allah sai ya tuba, watau yayi istigafari. Dama kuma Allah Yayi
alƙawari cewar Yana son masu tuba, haka kuma idan mutum ya tuba da
niyyar ba zai koma ga saɓo ba, to kamar bai taɓa aikata saɓon ba ne.
Haƙiƙa istigafari garkuwa ne daga faɗawa wuta, kuma Manzon Allah ya kasance yana yin istigfari sau
saba’in (70) a wuni, to ina ga kai da ni da ke?
4- Yawaita
Karatun Ƙur’ani: - Yawaita karatun Ƙur’ani na kawo alherai masu yawa kamar yawan lada, ceto
ranar ƙiyama, shiryar da mutum, tsare shi daga shaiɗanu, jawo arziƙi da sauransu. Allah Ya yi alƙawarin cewa duk wanda ya
karanta Ƙur’ani yana da lada goma akan kowanne harafi. Bayani ya gabata a
hadisai cewa Ƙur’ani zai ceci masu karanta shi a ranar ƙiyama. Haka kuma yawan karatun ka da shi yawan darajarka a
aljannah. Sannan kuma Ƙur’ani na shiryar da mai
yawan karatunsa, saboda Allah da kanSa Ya kirashi da cewa: “Hudan Lil Muttaƙeen”. Bayan wannan kuma, karatun Ƙur’ani kan tsare mutum daga Shaiɗanu saboda mutum ba zai fara karatu ba sai ya yi Isti’aza, watau
(A’uzu Billahi Minash Shaiɗanir rajeem) ). Haka kuma duk gidan da ake karanta Ƙur’ani shaiɗanu basa zama, sannan duk wanda ya karanta Ayatul Kursiyyu da
dare, to har gari ya waye babu Shaiɗanin da zai kusanceshi, haka kuma in ya karanta da safe to har
rana ta faɗi babu
shaiɗanin da
zai kusanceshi. Karanta Ƙur’ani na jawo arziƙi da wadata, kamar wani hadisi da ya nuna cewa yawaita karanta
Suratul Waƙi’a yana kawo arziƙi, watau yana maganin
talauci. Bayan wannan, sai wani hadisi da ya nuna cewa idan mai gida ya dawo
gidansa, to yayi sallama kuma ya karanta Ƙulhuwallahu, lallai
arziƙi zai sauka a gidan.
5- Biyayyar
Mace ga Mijinta (Girmama Miji) : -
Biyayyar mace ga mijinta wajibi ne saboda wani hadisin da Annabi Sallallahu
Alaihi Wa-Sallam yayi umarni cewa da mutum zai iya yiwa wani mutum sujada, da
an umarci mace ta yi wa mijinta sujada.
To amma
da yake ba a yi wa kowa sujada sai Allah. Amma shari’a ta umarci mace ta yiwa
mijinta biyayya iyakar biyayya matuƙar dai bai umarce ta da ta
yi saɓon Allah
ba.
Da wani zai iya yi wani sujada da mata ta yi wa mijinta
sujada.
وعن أبى هريرة رضي الله عنه, عن النبي صلى الله
عليه وسلم قال ( لو كنت أمرا أحدا أنيسجد لأحد لإمرت المرءت أن تسجد لزوجها) رزاه
الترمذى وقال حديث حسن صحيح).
An karɓo daga Abu Hurairah (R. A) Daga Manzon Allah (S. A. W) ya
ce da wani mutum zai iya wa wani sujada da na umarci mata ta yi wa mijinta.
(Tirmiziy ne ya ruwaito shi. )
GIRMAMA
UWA.
Lallai ya zama wajibi a girmama uwa a matsayin ta
na uwa domin saboda irin wahalar da ta sha tun daga ɗaukar ciki, kamar yadda Allah (S. W. T) Ya tabbatar da
haka a Al-ƙur'ani a surori biyu watau Suratul Ahazab da Luƙman.
حملته أمه كرها ووضعته كرها
Mahaifiyar
ka ta ɗauki
cikin ka
حملته أمه وهنا على وهن
Mahaifiyar
ka ta ɗauki
cikin ka rauni bisa rauni.
Bayan
wannan kuma, sai wani hadisi da yayi bayanin girman uwa ga 'ya'yan ta don kuwa
wani ya tambayi Manzon Allah (S. A. W) cewa wa zai kyautata wa? Sai Manzon
Allah yace masa mahaifiyar ka har sau uku.
عن أبى هريرة رضى الله عنه قال: وحين سئل النبى
صلى الله عليه وسلم من أحد أصحابه: أى الناس أولى ببر يارسول الله؟ قال أمك، قال
ثم من؟ قال أمك، قال ثم من؟ قال أمك. قال ثم من؟ قال أبوك. متفق عليه.
An
karbo daga Abu Hurairah (R. A) yace wata rana wani ya tambayi Manzon Allah (S.
A. W) yace Ya Rasulillahi! Cikin mutane wa zan fi kyautata wa? Sai Manzon Allah
(S. A. W) yace mahaifiyar ka, ya sake tambayar Annabi har sau uku yana ce masa
mahaifiyar ka, sai a na hudu ne yace masa mahaifin ka.
Bukhari
da Muslim ne suka ruwaito.
GUJEWA
YAWAN BUTULCI (MANCE ALHERIN DA AKA YI MATA).
A
mafi yawan lokuta sukan mance duk alheri da abin arziƙin da ka taɓa yi musu, zasu ce maka me ka taɓa yi min?. Akan wannan ne ma Manzon Allah (S. A. W) yace ya leƙa wuta ya ga mata sun fi yawa, sai ɗaya daga cikin matansa
tace: “Ya Rasulillah! Saboda me? Sai Manzon Allah (S. A. W) yace saboda
butulcinsu domin komai daɗewar da mutum yayi yana kyautata muku da zarar wata rana ta zo to
sai aka samu saɓani, sai kuce me mutum ya taɓa yi muku?
HAƊARIN BUTULCEWA MIJI.
عن ابن عساكر، عن عائشة رضى الله عنهما: قال النبى
صلى الله عليه وسلم: إذا قالت المرأة لزوجها ما رأيت منك خيرا قط فقد حبط عمنها.
An
karɓo
daga Ɗan Askar, daga Aisha (R. A) tace: Annabi (S. A. W) yace: "Duk
macen da ta cewa mijinta bata taɓa ganin alheri daga wurin sa ba, to haƙiƙa ta ɓata ayyukan ta.
YAWAN AIKATA ALHERI NA
GYARA ZUCIYA.
Duk
wanda yake yawan aikata alheri kama mai yin wa’azi, matuƙar ya dage yana yin wa’azin ko ya samu karɓa ko bai samu ba, Allah (S.
W. T) zai ƙara masa imani a inda zai gyara masa zuciya.
Bayan
wannan, duk wanda ya tsare sallah ta zamar masa jiki ya saba, to lallai ne
Allah Zai shiryar da shi, zuciyarsa zata shiryu. Kamar yadda wata aya tace: -
إن الصلاة كانت تنهى عن الفحشاء والمنكر....
Lallai
sallah tana hana aikata mummunan aiki (alfasha) abubuwan ƙi….
Akwai kuma yawaita
azumi, matuƙar mutum ya lizimci azumi na farilla ko nafila, Allah (S. W. T)
Zai gyara masa zuciya. Domi azumi na rage sha’awa kuma yana shiryar da zuciya.
YA KAI ƊAN’UWA! KA KIYAYE ABUBUWA SHIDA (6) KA SHIGA ALJANNAH.
Haƙiƙa duk Musulmin da ya lizimci abubuwa shida (6) , lallai Manzon
Allah zai lamunce masa shiga Aljannah. Wannan abubuwa kuwa su ne kamar haka: -
1. Faɗin gaskiya.
2. Cika alƙawari.
3. Kiyaye
amana.
4. Kiyaye
farji.
5. Kiyaye
ido daga kallon haramun.
6. Kiyaye
dukiyoyin mutane.
Baihaƙi ya ruwaito shi daga Ubadata Ɗan samit.
3- RIGA-KAFIN LALACEWAR
‘YA’YA.
ZAƁARWA 'YA'YA UWA TA GARI.
Wajibi ne ga dukkan mahaluki mai hankali da yayi niyyar yin aure,
to ya yi ƙoƙarin zaɓarwa 'ya'yansa uwa ta gari, ma'ana mai tarbiyya da son addini. Kar
ya bi son zuciya ya auro mace don kyau, watau kyakkyawa, ko 'yar wane, watau
mai nasaba (mai kuɗi, sarauta, muƙami). Wannan magana ta yi
dai-dai da wani bayani da Manzon Allah (S. A. W) ya yi cewa ku auri mace
ma'abuciyar Addini. Domin yace in ka yi aure don kyau, to lallai kyau kan ƙare in ta tsufa, ko nasaba don mulki na iya ƙarewa, amma shi Addini ba ya ƙarewa.
Bayan
haka, zaɓarwa
'ya'ya uwa ta gari kamar hutar da kai ne, domin in ka haifi yara da mace
ta ƙwarai, to kamar ita ce makarantar su don zasu koyi komai na ƙwarai daga wurinta. Saboda masu hikima sun ce uwa ita ce
makarantar farko ga yaro. Haka kuma in mutum ya kuskure ya auri Ballagazar mace
mara tarbiya, to ya kashe kansa da kansa, kuma yaransa sun shiga uku. Babban
dalili shi ne, ita ba ta da tarbiya, ba ilimi balle addini, to a nan ina
makarantar farko take? Sai dai su koyi zagi da miyagun halaye.
HAƘƘIN AMBATON ALLAH
وعن معاذ رضى الله عنه قال: قال النبى صلى الله
عليه وسلم: "أكثرو ذكر الله تعالى على كل حال, فإنه ليس عمل أحب إلى لله ولا
أنجى لبعده من ذكر الله تعالى فى الدنيا والآخرة".
An
karɓo daga
Mu'azu (R. A) yace: Manzon Allah (S. A. W) yace: "Ku yawaita ambaton Allah
a kowane lokaci da hali domin cewa babu wani aiki da Allah Yafi so kamar
zikiri.
HAƘƘIN RANTSUWA.
A musulunce, haramun ne musulmi in ya tashi yin rantsuwa ya rantse
da wani abu da ba Allah ba. Wajibi ne in musulmi ya tashi zai rantse, to ya
rantse da Allah (S. W. T).
HAƘƘIN ADDU'A.
A shari'ar musulunci, wajibi ne musulmi in ya tashi yin addu'a to
ya roki Allah (S. W. T) kar ya roƙi wani abokin halitta, sai
dai Allah. Addu'a ibada ce don haka yi wa wanin Allah shirka ne, dole ne kuma
musulmi ya guji yin shirka ta kowacce fuska.
HAƘƘIN AMBATON ALLAH (ZIKIRI).
عن أبى الجوزاء مر سلا قال: قال النبي صلى الله
عليه وسلم: أكثرواذ كرو الله تعالى حتى يقول المنافقون إنكم مرائون.
An
karɓo daga
Jauza'iy Mursalam (R. A) yace: Manzon Allah (S. A. W) yace: "Ku yawaita
ambaton Allah (zikiri) har munafukai suce ku masu riya ne.
HAƘƘIN UWA A KAN ƊANTA.
Matsayin da uwa take da shi a wajen ɗan da ta haifa ba ƙarami ba ne. Dalilin wannan matsayi ne ya sa Allah Ya baiwa uwa
muhimmin matsayi na baiwa da martaba wanda ko da baki (magana) , ba addu'a ba
yake kama yaron (ɗanta). Matuƙar aka ce uwa ranta
ya ɓaci a kan
wani al'amari da ɗanta ya yi a wani lokaci ko ba tayi addu'a ba, duk abin da ta
furta Allah kan karɓi addu'ar.
Haka
kuma matuƙar uwa ta yi wa ɗanta kyakkyawar addu'a ba zai taɓe ba a rayuwarsa. Misali wani bawan Allah mai bauta a cikin Banu
Isra'ila wanda yana ibada uwarsa ta zo tana kira bai amsa ba, ranta ya ɓaci ta yi masa muguwar
addu'a tace Allah Ya haɗa fuskar sa da ta karuwa, cikin ikon Allah sai da ya ga mugun abu.
A
wannan matsayi ina kiran 'yan uwana da mu lallaɓa mahaifan mu ko rayuwarmu ta yi kyau. Su kuma iyaye su danne
fushinsu, su daina furta miyagun maganganu ga ‘ya’yansu don samun kyakkyawar
al’umma nan gaba.
TARBIYYAR ‘YA’YA YA RATAYA
WUYAN IYAYE.
Nauyin yiwa ‘ya’ya tarbiyya ya rataya ne a wuyan iyaye watau uba
da uwa. Wanda ya haɗa da: -
1. Sanin
Allah.
2. Son
Annabi da Alayensa.
3. Karatun Ƙur’ani.
4. Sallah.
5. Girmama
na gaba.
6. Koyar da
magana.
7. Koyar da
tafiya.
8. Koyar da
cin abinci.
9. Koyar da
kwanciya.
10. Koyar da
kunya.
11. Gudun kwaɗayi.
12. Barin
hassada.
13. Koyar
da ƙwazo.
14. Koyar da
tsafta.
15. Koyar da
tattali.
16. Koyar da
zumunci.
17. Koyar da
tausayi.
18. Koyar da
kallo.
19. Koyar da
tsare amana.
20. Gujewa ƙarya da gujewa gaskiya.
FALALAR RAINON 'YA'YA MATA.
Akwai
wata garaɓasa wadda
Allah (S. W. T) ya tanadarwa duk mutumin da ya raini 'ya'ya mata har zuwa
girmansu kuma suka yi aure. Wannan kuwa ya bayyana a wani hadisi da Manzon
Allah (S. A. W) ya yi bayani a kan haka.
Kamar
haka: -
"Manzon
Allah (S. A. W) yace dukkan wanda ya ɗauki nauyin 'ya'ya mata guda biyu ko uku ko 'yan uwa biyu ko uku
har suka girma (suka yi aure) , ko kuma ya mutu ya bar su, zan kasance ni da
shi a cikin Aljannah kamar haka, sai yayi nuni da hannunsa manuni da wanda yake
binsa. Kuma zai samu ladar mai jihadi don ɗaukaka kalmar Allah, wanda yake azumi da sallar dare a wurin
jihadin. Sai wata mace tace har 'ya ɗaya? Sai Manzon Allah (S. A. W) yace har da mai 'ya ɗaya. "
وعن أنس رضى الله عنه، عن النبى صلى الله عليه
وسلم قال: من عال جاريتين حتى تبلغا جاء يوم القيامة أنا وهو كهاتين.
An
karɓo daga
Anas (R. A) yace, daga Manzon Allah (S. A. W) yace, duk wanda ya raini (riƙe) yara mata biyu har suka girma, watau suka balaga, ranar ƙiyama zai zo ni da shi haka…..
عن عبد الرحمن ابن مرقع رضى الله عنه قال: قال
النبى صلى الله عليه وسلم: إنه لا وعاء إذا ملئ شر من بطن، فإن كنتم لا بد فاعلين،
فاجعلوه ثلثا للطعام وثلثا للشراب، وثلثا للريح أو النفس.
الإمام السيوطى.
An karɓo daga Abdurrahman Bin
Marka'a (R. A) yace: Manzon Allah (S. A. W) yace: "Babu wata jaka da za a
cika ta fiye da ciki, in ya kasance babu makawa ku masu aikata haka ne, ku
sanya shi kashi ɗaya don abinci, kashi ɗaya domin abin sha (ruwa) , kashi ɗaya domin shaƙar iska ko numfashi.
Suyuɗi ya ruwaito.
1. An hana
yin mugun ci.
2. An hana
cin abinci mai zafi.
3. An hana
hura abinci da baki.
4. An hana
da an gama cin abinci a kwanta.
5. An hana
cin abinci ham-ham, (hannau baka hannu ƙwarya).
6. An hana
cin abinci har sai an ji yunwa.
7. An hana
surutu in ana cin abinci.
4- RIGA-KAFIN MUMMUNAN
KISHI.
IM ANI.
Imani
shi ne yarda da abu, watau yarda da ƙaddara. Abin da yasa
Bahauhshe yake cewa haka shine, imani yana da rassa shida sune: -
ü Imani da Allah.
ü Imani da Mala’iku.
ü Imani da LittattafanSa.
ü Imani da ManzanninSa.
ü Imani da tashin ƙiyama.
ü Imani da Ƙaddara mai daɗi da mara daɗi, (mai kyau da mara kyau.
)
Bugu
da ƙari, Allah Yace: “Ku shiga Addini gaba ɗaya”. Sannan Yace: Zaku yi
imani da wani sashe na Ƙur’ani ku kafirce wani
sashinsa? Allah (SWT) da kanSa yake cewa musulmai su yi aure, sannan kuma da
mata biyu ya fara yin umarni sannan uku, sannan huɗu, sai a ƙarshe ne aka ce ku auri mace ɗaya in kuna tsoro ba zaku yi adalci ba a tsakaninsu.
KYAKKYAWAR ƊABI’A.
HARAMCIN ƘAURACEWA MIJI A SHIMFIƊA.
Shari’ar
Musulunci ta yi hani ko haramta mace ta ƙauracewa
mijinta a shimfiɗa, watau lokacin kwanciya in ya buƙace ta,
ma’ana ya kira ta, saboda zata shiga fushin Allah, Mala’iku zasu yi ta tsine
mata har sai gari ya waye.
وعن أبى هريرة رضى الله عنه قال: قال رسول الله
صلى الله عليه وسلم: إذا دعا الرجل امرأته إلى فراشة فلم تأته فبتا غضبان عليها
العنتها الملائكة حتى تصبع. متفق عليه.
An
karɓo daga
Abu-Hurairah (R. A) , yace Manzon Allah (S. A. W) yace: Idan miji ya kira matar
sa zuwa shimfiɗarsa, watau ya nufi ya kwanta da ita amma ta ƙI, ma'ana ta ƙi yarda da shi, har shi
mijin ya yi fushi da ita, Mala'iku zasu yi ta tsine ma ta har zuwa asuba.
Bukhari da Muslim suka ruwaito.
KYAKKYAWAR ƊABI’A. (HANIN CUTAR DA JUNA. )
Shari'ar
musulunci ta yi hani tare da cutarwa a kan ɗan uwa musulmi ya cutar da wani ko ta wacce irin fuska kuma
komai ƙanƙantar abu, in dai zai cutar da ɗan'uwa, to aguje shi. Babban misali shi ne, ba wani aiki ba ko
magana, hatta kallo ba a yarda ka yi wa ɗan'wan ka ba. Ku zama kamar jiki guda in wata gaɓa ta kama ciwo, to sauran
ma su amsa. Ku zama masu ƙaunar juna. Ga wani babban
misali, shi ne a wani hadisi: -
عن أبى هريرة رضى الله
عنه، أن النبى صلى الله عليه وسلم قال: ولا تحاسدوا، ولا تناجشوا، ولا تباغضوا،
ولا تنابروا، ولا يبع بعضكم على بيع بعض، وكونوا عباد الله إخوانا. المسلم
أخوالمسلم، لايظلمه، ولايخذ له، ولا يكذبه، ولا حقره، التقوى ههنا، وبشر إلى صدره
ثلاث مرات. بحسب أمرئ من الشر أن يحقر أخاه المسلم غلى المسلم حرام، دمه وماله،
وعرضه. رواه مسلم.
An
karɓo daga
Abu hurairah (R. A) yace: Manzon Allah (S. A. W) yace: "Kada ku yi wa juna
hassada, kuma kada ku yi wa juna ƙyashi, kuma kada ku
yi ƙiyayya, kuma kada ku yi wa juna ruɗi a ciniki, kuma kada waninku ya yi ciniki a kan cinikin waninsa.
Ku zama bayin Allah 'yan uwan juna. Musulmi ɗan uwan musulmi ne, kada ya zalunce shi, kuma kada ya taɓar da shi, kuma kada ya yi
masa ƙarya, kuma kada ya wulaƙanta shi. Tsoron Allah a
nan yake, (ya faɗi haka sau uku yana nuna ƙirjinsa).
Ya isa sharri ga mutum ya wulaƙanta musulmi ɗan uwansa. Musulmi, jininsa
da dukiyarsa da mutuncinsa haramun ne. " Muslim.
NISANTAR
JITA-JITA.
Jita-jita
na nufin ɗauka ko yarda da labarai ko maganganu barkatai daga bakin mutane
ba tare da bincike ba. Misali akwai labarin cewa mijin ki yayi kaza, ko yace
kaza, ko an ganshi da wata ko a wani wuri da sauransu.
Allah
Yace idan fasiƙi ya kawo labari to ku bincika. Domin duk wanda ake kawo masa
labari ba tare da yayi bincike ba, kuma har ya ɗauki mataki to zai yi
nadama wataran.
5- RIGA-KAFIN ZUWA GIDAN
BOKA (MALAMIN TSUBBU).
BOKANCI.
Bokanci
wata daɗaɗɗiyar hanyar binciken
cututtuka da nazarce-nazarcen itace da ƙwari da
dabbobi da halittun sama da ƙasa, da na sarari da
na ɓoye
(iskoki) domin samar da magani da warkarwa da mabuƙata. Babu wanda ya san lokacin da Bahaushe ya fara sarrafa
magungunansa.
Bayan
Boka, akwai magori da ‘yar maiganye shi magori wani mutum ne da yake ɗaukar jaka da ake kira
jakar magori, mai ɗauke da saƙe-saƙI, ganyayyaki, guraye, layu, fatun sassan jikin wasu dabbobi da
tsuntsaye da sauransu don yin talla layi-layi kwaro-kwaro, ita kuma ‘yar mai
ganye tana yawo da Kwando cike da tarkace saƙe-saƙI, ganyayyaki kamar dai magori. Tana shiga gidaje don yin talla.
Bayan
waɗannan,
sai sarkin mayu wanda shi ma yana tallar magani da jakarsa, kuma har yakan
fitar da ƙanƙarar maita daga cikinsa.
Magani:
- asalin Kalmar ya samo ne daga sha-ma-gani, sha-mu-gani, gwada-mu-gani, sai ya
koma sha-mu-gani, magani sai da gwaji. Magani sai Allah don itace sinadari ne.
TSUBBU.
Tsubbu
wata kalma ce da ta samo asali daga harshen larabci wadda ake kira “Ɗibbu” mai nufin magani. Bahaushe sai ya ɗauki wannan kalma ya bata
wata ma’ana mai nufin magani ta hanyar addini da aka harmutsa ta hanyar duba,
watau ilmin taurari ko kuma a haɗa jiƙe-jiƙen magunguna da rubuce-rubuce ta hanyar amfani da wasu ayoyi ko
surori daga Alƙur’ani, ko kuma a zaɓo wasu laƙuna da asirai daban-daban.
ƊIBBU.
Malamai
masu ɗibbu ba
su da ilmi da yawa galibinsu sai Alƙur’ani kaɗai suka sani, wasu kuwa sai
su fara da karatun huru’a kawai, kamar su Ahalari da ishimawi da su Ƙawa’idi har Risala. Amma su waɗanda suka yi zurfi, wani lokaci suna yawo da ‘yan ƙullinsu, watau almajiransu, waɗanda suka isa sai a iske su a gidajensu.
Malaman ɗibbu su sukan yi rubutun
sha, maganin farin jinni da na tsautsai, da sauran irinsu, kuma sukan yi ɗibbu su rubuta laya su ba
mutane, su kuwa mutanen su basu kuɗi. wannan shi ne iyakar batun ɗibbu.
MALLAMI.
Kalmar
malami ita ma kalma ce da ta samo asali daga harshen larabci mai cewa:
“Mu’allimu ko Mu’allim”. Bahaushe ya datse ya komar da Kalmar zuwa Mallam, mai
ma’anar masani watau wanda ya san ilmi a fagage da yawa.
MALLAMIN TSUBBU.
Na
nufin malamin da ya san ilmin taurari (ilmin nujum) , da kuma wasu asararru da
wasu malamai suka ciro daga littattafai da Ƙur’ani da
hadisai. Amma wasu suka fara haɗawa da ƙulunboto da aljani da
sauransu.
HAƊARIN ZUWA GIDAN BOKA (TSUBBU)
(Mu kiyaye mu samu
tsira da mutunci da imani).
Bisa dogaro da wasu
hujjoji na zahiri kuma bayyanannu da suka faru a garuruwa da dama, sannan a
lokutta daban-daban. Waɗannan abubuwa da suka faru, sun shafi mutane daban-daban. Ga
dukkan mai hankali wannan bayani ya wuce jayayya in dai ba a sa son zuciya ba.
Akwai haɗurra masu yawa da ake iya
gamuwa da su, ko faɗawa ciki, a dalilin zuwa gidajen bokaye da ‘yan tsubbu. Tun da
farko dai zuwa gidansu tare da gaskata su saɓawa Manzon Allah ne. domin yace duk wanda ya tafi wurin boka ya
kuma gaskatashi to an saɓa wa (Annabi (S. A. W) ).
Haɗarin zuwa gidan Boka da
Malaman Tsubbu.
· Kaɗaicewa.
· Tonewa
kai asiri.
· Asarar
dukiya.
· Shirka.
· Jayayya
da Allah.
· Ridda.
· Zina.
· Cin
Amana.
· Kome.
· Tozarta/Nadama.
Bayan
wannan kuma, sai wani saɓon shi ne keɓewa da mace da namiji su biyu, bayan kuwa Annabi ya hana, to ashe
yin haka shi ma saɓawa Annabi ne.
Bayan
wannan sai tonawa kai asiri, domin zaki tonawa kan ki asiri ta hanyar bayyana
sirrinki da na mijinki ga wani, wanda kin roƙi Allah
ke da shi ki yi addu’a ko aikata wani aiki na alheri ko lada sai ki yi
tawassuli da aiki ki yi addu’a. akwai asarar dukiya da za ki yi, domin wasu ba
sa yin wani aiki ko roƙon Allah da akan ce, sai
dai kawai su yi maki wayau su karɓe maki kuɗi, wanda waɗannan kuɗi da kin bar su kin yi wa mahaifanki wani aikin alheri ko abokan
mahaifa ko wasu gajiyayyu, ko yara marayu ko maƙwabta,
kai ko mijinki ki bai wa sadaka ko kyuta zaki samu lada a wurin Allah kina kuma
iya yin tawassuli da aikin a wurin addu’a.
Akwai
wani mummunan haɗari da ake iya gamuwa da shi a dalilin zuwa gidan boka shi ne haɗarin shirka. Matuƙar boka ya riƙa baya aiki shi kaɗai sai da taimakon shaiɗanu ko iskoki wanda su ba
sa yi maka aiki sai kai ma ka yi masu wanda yayi kama da bauta ko haɗa Allah da wani.
Wasu
dalilai da suke kai mata wurin boka sun haɗa da neman haihuwa, korar kishiya ko mallamakar miji.
Game da maganar
haihuwa, kowa ya san Allah ke bada haihuwa ba boka ba, don haka ki roƙi Allah don Shi ke bayarwa. Tafiya nema wurin wani kuskure ne.
Dangane
da maganar kishiya, korar ta ko hana ta zuwa gidan mijinki. Dukkan Musulmi yayi
imani da ƙaddara, don haka abin da Allah ya ƙaddara, ba boka ba, in duk duniyar nan zaki tara don su taimake ki
ba za su iya ba. Haka kuma wani bai haihuwar ɗan wani, Allah Ya rubutawa
mijinki ‘ya’ya 10 ko 15, ke kin haifi 7 ko 9, to kina tsammanin sauran ba zasu
zo ba ne? to gaskiyar al’amari shi ne kowa an rubuta abin da zai Haifa tun
alimiz zarri, don in kika ce wai baki yarda ba, to kina jayayya ne da ƙaddarar Allah.
Haka kuma al’amarin
da ya shafi mallakar miji kuwa, boka bai kai yadda ke zaki yi ki samu kan mijin
ki ba. Matuƙar ki ka gyara halayenki da dabaru na nuna ƙauna ko tsare amana da sauran abubuwa, suna iya baki matsayin
mallakar miji ba boka ba. Shi dai zai sa ki cikin halaka da shirka. (Hikayar
mai macizai).
Bayan haka, kuma boka
yana iya sanya ki kiyi ridda ba tare da kin sani ba. Akwai wasu bokaye da sukan
haɗa ƙulonboto tare da sunan Allah ko ayoyin Alƙur’ani, sai kuma su saki ki sanya wata laya a cikin najasa, masai
(shadda) , juji, kwata, suri ko tsohuwar rijiya, ko ace ki sa a cikin mushen jaɓa. duk mutumin da ya aikata
wannan ya wulaƙanta ayar Ƙur’ani don haka ridda ne.
ban da wannan kuma, in kika yi wa wata sihiri (tsafi) ta haukace, to duk saɓon da ta yi haƙƙin na kanki, in kuma mutuwa ta yi, to kin yi kisan kai. Allah kuma
yace “Duk wanda ya kasha mumini da gangar sakamakonsa Jahannama mai dauwama a
cikinta”…….. in wani ciwo ne kika sanya mata ki saurrari naki ko akan ‘ya’ya ko
jikoki a matsayin komen sammu.
Wani
babban haɗarin da
mata kan gamu da shi a dalilin harka da bokaye shi ne faɗawa tarkon zina, saboda sau
da yawa wasu mata sukan faɗa tarkon da bokaye ke yi musu ta hanyar sihiri ko dabaru har sai
sun yi zina da su. Akwai wasu matan har cikin shege suke samu a sakamakon zina
da bokaye. An samu shaidun faruwar haka a garuruwa a kafafen watsa labarai,
kamar rediyo da talabijin da jaridu, kuma har yanzu wasu basu bari ba.
Wani
haɗarin shi
ne, zuwa wurin boka na jefa mata cikin cin amanar mazajensu, kamar ya yarda da
ita, amma da zarar ta fara zuwa wurin boka zata fara ha’intarsa, don kuwa babu
izininsa zata tafi, ta tona asirinsa ga wani ya ba ta wani magani ko laya ta sa
masa a abinci ko filo (matashin kai) , ko a takalmi da sauran wurare na ha’inci
kuma a munafunce, saboda ba zata so ya sani ba.
Akwai
wani haɗarin da
mata kan gamu da shi, saboda zuwa gidan boka, shi ne kome, kome na nufin mutum
yayi sammu ko makaru don ya cutar da wani, to in aka yi rashin sa’a sai ya
komowa wanda yayi. A irin nan ne ake samun haukar kome da ake cewa aniya
makomiya, ko aniya-bi-aniya, ko ƙaiƙayi koma masheƙiya.
Bayan
wannan, sai tozarta tare da nadama da mata masu zuwa gidan boka kan gamu da su.
Mafi yawan mata dake hulɗa da bokaye asirinsu kan tonu, a wani lokacin ma basu ci nasara
ba, mazajensu su kore su, kuma a yo kishiya har ta haihu, ita kuma ba ɗan, kuma bata mallaki mijin
ba, ga saɓon Allah
da ManzonSa ga asarar kuɗI da mutunci (ta yi rasasa-rasasa).
Aƙarshe ina kira da babbar murya mata har da maza ma da mu kiyayyi
bokaye don gudun kar mu yi saki-na-dafe, ba tsuntsu ba tarko, Allah Ya tsare
mu.
KAMMALAWA.
Wannan ɗan ƙaramin bincike ya kammala cikin ikon Allah. Domin ƙoƙarin gano wasu hanyoyi ko dabaru waɗanda nake ganin za su taimakawa al’umma ta fuskar kare kai a
matsayin riga-kafi daga faɗawa ko kamuwa da wasu abubuwa a rayuwar mu gaba ɗaya.
Da
farko dai mun ga taken da na baiwa wannan Muƙala tare
da dalilai na, domin na kalli abin ta fuskoki da dama, kuma ina fatan an karɓi wannan take da na sanya.
Bugu
da ƙari, in aka kalli wannan Muƙala ana iya cewa ta yi
harshen damo, ko kuma ace mata hatsin bara, bisa dalilin ta shafi al’ada, ta
kuma shafi addini, koda yake daman abubuwa ne guda biyu da ba mai ‘iya raba su
don sun yiwa juna shigar giza-gizai, haka kuma ta shafi duniya da lahira da
kuma lafiya da tattalin arziƙi da sauransu. Ina fatan
Allah ya taimaka mana amin. Alhamdu lillah.
MANAZARTA.
Sa’adu M. M (2007) HAUKA DA
IDON BAHAUSHE. Kundin bincike digiri na biyu M. A-Hausa. Usman Ɗanfodiyo University, Sokoto.
Saulawa M. I. (2000)
Jagorar Fahimtar Ciwon taɓin hankali.
Al’sam Printers
Katsina.
Bunza A. M. (2006) GADON FEƊE AL’ADA.
Tiwal Nigeria limited
suru lere Lagos.
Bunza A. M. (1995)
MAGUNGUNAN HAUSA A RUBUCE (Nazarin Ayyukan Malaman Tsibbu) ,Kundin digiri na
uku Phd Hausa,
Bayero University
Kano.
Bunza A. M. (1990) “Hayaki
fidda na kogo” (Nazarin sihiri da siddabarun hausawa)
Kundin digiri na Biyu
M. A. Hausa.
Bayero University
Kano.
Abubakar Gumi (1980)
FASSARAR HADISAI ARBA’IN.
Northan Nigeria
publishing company. Zaria
Ibni Hajar Askalani (1988)
BULUGUL MARAMI.
Darul Fikr Bairut
Lebenon.
Suyudi A ( ) JAMI’UL
HADITH.
Zaid A. A. ( ) RISALA
FASSARAR HAUSA.
Abubakar M. G. (1980) ALƘUR’ANI MAI GIRMA.
Hadimul
Haramainish-Sharifaini Makka.
Malik. I. (1970) MUWAƊƊA MALIK.
Darul Fikri Beirut
Lebanon.
Annawawi. I. ( )
RIYADUSSALIHIN.
Darul Fikr Beirut
Lebanon.
Imam Z. ( ) KITABUL
KABA’IR.
Darul Fikr Beirut
Lebanon.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.