Ticker

6/recent/ticker-posts

Dokin Zuciya Ba a Hawanka Sai An Yi Nadama: Tsokaci a Kan Ayyukan Son Rai Da Mutum Kan Yi a Karshe Ya Rinka Da-Na-Sani

Wanda aka gabatar a taron tallafawa Marayu da aka yi a zauren taro, Hanyar Likoro zuwa Kudan da ke Garin Kudan. Ranar Lahadi 7 ga Watan Ramadan 1440 Hijiriyya, daidai da 12 ga Watan Mayu 2019 Miladiyya.

DOKIN ZUCIYA BA A HAWANKA SAI AN YI NADAMA: TSOKACI A KAN AYYUKAN SON RAI DA MUTUM KAN YI A ƘARSHE YA RINƘA DA-NA-SANI

DAGA

MU’AZU SA’ADU MUHAMMAD KUDAN

JAMI’AR SULE LAMIƊO KAFIN HAUSA, JIHAR JIGAWA.

GABATARWA:

 Da sunan Allah Mai rahama Mai jinƙai, Mai kowa, Mai komai, Mai aikata abin da Ya so, ga wanda Ya so, a sadda Ya so, a yadda Ya so, ko ana so ba a so dole bayi su so. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban halittu Annabi Muhammadu, da Alayensa da Sahabbansa.

 Wannan maƙala na da niyyar yin bayani a kan ɗabi’ar son zuciya ko son rai. Nazarin zai dubi ma’anar son zuciya ko son rai, da dalilan da kan jawo su, tare da haɗarinsa ko illoilinsa ga wanda ya yi da kuma abokin zama. Sannan da kuma yadda son zuciya ke rusa al’umma. Kamar yadda Bahaushe yake cewa a wata Karin Magana, “Son zuciya ɓacin zuciya”, shi ne Bahaushe kan yi kinaya ya ce, “Dokin zuciya ba a hawanka sai an yi nadama”. Wannan maƙala za ta fito da shawarwari ta yadda za a kaucewa hawa dokin zuciya. Domin kaucewa faɗawa cikin haɗari da kuma yin nadama daga ƙarshe. Na rufe da kammalawa da manazarta

MA’ANAR DOKI: CNHN (2006) Dabbar gida da ta fi jaki da alfadari girma wanda ake hawa da sirdi don tafiya ko zuwa yaƙi. Wata dabba ce mai ƙafafu huɗu da kofato, yana da kunnuwa biyu da jela dambajejiya.

MA’ANAR ZUCIYA: CNHN (2006) Wata curarriyar tsoka da take cikin ƙirjin mutum ko dabba ko tsuntsu, wanda ke aika jini zuwa sauran sassan jiki.

 Wata tsoka ce mai launin ja, mai siffar ƙwai, wacce take aikin sarrafa jini a jikin Mutum ko dabba, daga ƙirji. Zuciya kuma ita ce muhalli inda tunani da Imani suke. Tunani na samuwa ne ta hanyar tuntuɓa tsakanin zuciya da ƙwaƙwalwa, domin shi hankali a kai (ƙwaƙwalwa) yake. Akan ce in rai ya ɓace hankali kan nemoshi.

DOKIN ZUCIYA: Wata kalma ce da ake kira harɗeɗɗen suna. Wadda take nufin bin son zuciya ko son rai, wato duk abin da zuciya ta riya wa mutum sai ya bi. CNHN (2006) Son zuciya wato mutum ya aikata abin da ya ga dama. Hawa dokin zuciya wato ya fusata.

 Da Larabci ana cewa “Hawan nafs”. Da harshen Turanci kuma ana cewa “Selfishness”.

A ƙur’ani Suratul Nazi’at aya ta 37 zuwa 41. Inda aka bayyana cewa duk wanda so duniya ya yi abin da yake so to jahannama ce makomarsa. Haka kuma duk wanda ya ji tsoron Allah ya hana zuciyarsa abin da take so, to aljanna ce makomarsa. Alhaji Aliyu Namangi Zariya na cewa:

 Zuciya ita goɗiya ce,

Wanda duk ya sake ta goce,

Sai ta kai shi cikin wuta ce,

Kar ka sau ragama ta kauce,

Ta fice da guda ta aika ɗanya.

Bisa la’akari da wasu abubuwa da sukan ingiza mutum ya hau dokin zuciya suna da yawa. A mafi yawan lokuta waɗannan guda goma su ne suka fi fazgar mutum mace ko namiji babba ko yaro, sai daga baya ya dawo yana da-na-sani. Malamai suka ba da shawarar cewar mutum ya yawaita faɗar: Hasbunallahu wani’imal wakilun.

1. Fushi

2. Ƙin karɓar gaskiya

3. Kwaɗayi

4. Haɗama / Babakere

5. Hassada

6. Mugunta / Ƙeta

7. Ƙarya

8. Yaudara / Saɓa Alƙawari

9. Girman Kai

10. Cin Amana

1. FUSHI: Bisa mahanga ta addini fushi yana da illa, don haka Annabi (S. A. W) ya yi hani da yin fushi, a wani Hadisi ya ce: “La tagadab” (Kar kai fushi) har sau uku. Haka kuma wani Hadisin Annabi (S. A. W) da ya tambayi Sahabbai cewa wane ne mai ƙarfi? Sahabbai suka ce wanda aka yi kokuwa ya yi kaye. Sai Annabi (S. A. W) yace a’a, mai ƙarfi shi ne wanda fushinsa ya taso, amma ya danne zuciyarsa. Duk wanda ya yi fushi aka ce ya yi haƙuri matuƙar dai ya yi, to Allah zai taimakeshi, in kuma ya ƙi to zai ga abin ƙi. Kamar yadda ya zo a Suratul Luƙman aya ta 17. Inda aka nunawa mumini ya tsai da sallah, ya yi umarni da aikin alheri, kuma ya yi da mummunan aiki, kuma ya yi haƙuri.

 Bisa al’ada mutum mai saurin fushi, Bahaushe na kiransa da kububuwa. Ba duka harkoki ake yi da shi ba. Domin ana kallon sa mai murɗaɗɗen hali. Misali idan miji da mata suka samu saɓani sai aka ga ana bas u haƙuri suna ƙi, da zarar ɓarna ta auku (saki) , sai kuma a koma nadama.

 A kimiyyance, wani Likitan ƙwaƙƙwalwa a Jami’ar New York Amurka ya ce: “Halaye huɗu kan sanya mutum yin haukar wucin gadi: 1. Fushi. 2. Tsoro. 3. Sha’awa. 4. Zaƙuwa”.

2. ƘIN KARƁAR GASKIYA: Haƙiƙa son zuciya ne kan hana mutum karɓar gaskiya. Ƙiri-ƙiri mutum na sane za a faɗa masa gaskiya amma sai ya yi ƙemudugus ya ƙI yarda. Daga baya kuma mutum ya zo yana yin da-na-sani da ban yi ba. Aliyu Namangi Zariya ya ce:

Tun da sauran hankalinka,

 Yaƙi birnin zuciyzrka,

 Nemi tanlidi kaza ka,

 San su alwala da wanka,

Tun ba a aiko ma mala’ika ba.

3. KWAƊAYI: A al’adance Bahaushe na cewa “Kwaɗayi mabuɗin wahala” ko “Idan da kwaɗayi da wulaƙanci” ko “Mai kwaɗayi shi ya san gidan mai rowa” ko “Duk wanda ya shiga motar kwaɗayi zai sauƙa a tashar wulaƙanci” ko “ Idan ka ga abincinka inda bai dace ba, ka haɗiye kwaɗayinka ka wuce, idan ba ka haɗiye kwaɗayinka ba, to kwaɗayinka zai haɗiyeka. ” Aliyu Namangi yace:

Ka ci ka sha ka yi teɓa,

Ka mace kabari karɓa,

Ka ruɓe tsutsa ta sharɓa,

Yanzu me ya fi kyau ka zaɓa,

 In ba farali da nafila ba.

 Ga shi ka tozarta kanka,

 Son kuɗi ya sa ka shirka,

 Da dubun miliyan gareka,

 Ran da ka mutu sai a kaika,

 Da tufan daba zai yi fan bakwai ba.

. Ɗabi’ar kwaɗayi: Bayan wannan kuma,sai ɗabi’ar kwaɗayi. Matuƙar a ka ce mutum makwaɗaici ne, mace makwaiɗiya ce, to haƙiƙa suna cikin haɗari. Domin Bahaushe yace : “kwaɗayi mabuɗin wahala”ko “idan da kwaɗayi da wulakanci” ko “idan baki ya ci dole ido yai kunya”. Da sauran maganganu da dama masu nuna illar kwaɗayi a rayuwa. To don haka duk wanda ke da kwaɗayi ƙuda ne yana iya faɗawa haɗari. Kwaɗayi ya ƙunshi son abin duniya (kuɗi da komatsan duniya) ,ko kuma son cin daɗi kamar nama, ko kifi, ko kayan ƙwalam da maƙulashe. Misali yawan son abin duniya ke sa mace karɓar kyauta, ko roƙo a inda bai dace ba. An sha samun matan da aka yiwa kyauta daga baya abin ya zama fitina. Ko kuma wasu matan a saboda tsire ko balangu ko kaza ko kuma atamfar anko, sai su ba da kansu. Wasu kuma a saboda kuɗi, ko a wurin talla, ko wurin aiki sai su ba da kansu a ballagazar arha.

A addinance an ce duk wanda ya guji duniya kuma ya guji abin hannun mutane zai yi daraja a idon al’umma.

4. HAƊAMA KO BABAKERE: Son kai ya yi wa mutum yawa, tare da son tara abin duniya. Son zuciya kan lulluɓa tunanin mutum, a inda ya kan fifita kansa ko buƙatarsa a kan ta waninsa. Idan wani abu aka ba shi ya raba wa jama’a sai ya handame ya hana wasu. A wani lokaci kuma sai ya tattare ya babbake ya hana wani samu da yawa sai kaɗan.

Masu cin rashawa da soke,

Masu fince da masu tarke,

Mai ganin nassi ya take,

Zuciyarsa ba za ta warke,

Su yi nesa da cin haramiya ba.

5. HASSADA: Son zuciya ne kan sanya mutum ya yi baƙin ciki don wani ɗan uwansa ya samu alheri. Ko kuma mutum ya yi fatan arziƙi ko alheri da wani ya samu to ya lalace. Bahaushe ya ce “Hassada ga mai rabo taki”, “Hassada ga mai rai ba ta hana arziƙi” Kamar mummunan kishi da mata ke da shi a wannan zamani. Domin irin wannan kishi kamar jayayya da ƙaddara ne.

Kishi a rashin kishi: Kishin banza (kishin mai dadaro). A inda take ƙyamar mijinta ya ƙara aure, amma kuma yana da farka a waje. Domin son zuciya ta ƙi zama da kishiya, amma ƙawar Alhaji ko Amimiyarsa ko abokiyar aiki za ta zo gidan, kuma ta karɓe ta hannu bibiyu. Duk ɓarnar da miji zai yi indai ba maganar kishiya to daidai ne.

Bisa la’akari da bayanan da suka gabata. Kai tsaye muna iya cewa,duk macen da ta kasance da ɗaya daga cikin waɗannan ɗabi’u da aka lissafa. To ta zama mara wayau,kuma ba ta da tsafta, kuma ta zama ƙazama. Ta zama Ballagaza komai ilminta,komai barikinta, tana yin ɗigirgire ko kan-tafi da rayuwarta

6. MUGUNTA KO ƘETA: Son zuciya ne kan sanya wani ya yi tanajin mugun abu ga wani ɗan uwa, don ya cutar das hi. Bahaushe na cewa “In zaka gina ramin mugunta ginashi gajere”. “Mugunta fitsarin faƙo”. A mafi yawan lokuta ana samun wasu mutane sukan shirya mugunta amma kuma sai ta dawo kansu.

Alhaji Baba Maigyaɗa agege yana cewa:

Mun gode tabara sarki mai kyauta,

Da yayyo bayinsa galibi masu maganta,

Yayyo waɗansu galibi masu mugunta,

Halin ‘yan duniya na ke son in kwatanta,

Sun fir ƙaunar tajiri fa ba mara samu ba.

Idan ba ka da dukiya a yau an raina ka,

Sa’o’in ;ya;yanka su sukan riƙa takaka,

Da gangan wasu ja’irai sukan riƙa darjeka,

Idan yai Magana a c eta wane yana hauka,

Da ka yi shiru, sai a ce fa wane bai cika farai ba.

7. ƘARYA: Son zuciya ne kan sanya mutum ya shirya abin da ba a yi ba ya faɗa. Ko ya ƙirƙiri wata Magana ya shirya ƙarya. A yau saboda son zuciya babu babban babu yaro wajen ambaton abin da ba gaskiya ba.

 A addinance Annabi (S. A. W) yace, “Lallai gaskiya tana yin shiriya ko jagora ga zuwa aikin alheri, shi kuma yana yin jagora zuwa aljanna. Ita ɗarya kuwa tana yin jagora zuwa ga fajirci (Ɓarna) , ita kuma ɓarna tana yin jagora zuwa wuta. Idan mutum ya saba yin ƙarya Allah zai sa a rubuta masa maƙaryaci a duk inda yai Magana a ɗaukeshi maƙaryaci.

 A al’adance duk inda mutum ya kasance maƙaryaci to ana ɗaukarsa mutumin banza. Ba ma haka ba, ko da yawan santu mutum ya cika yi, akan ce maganar wane ka ji ta hauka barta a nan. A maganganun yau da kullum a kan ce “Ai wane durum ne uban ‘yan ƙarya”, ko “ƙarya kamar kuɗin duba”, ko “ƙarya kamar guntun yaƙi”, Ibrahim Narambaɗa na cewa:

Na bar ƙarya ko ina kiɗi,

Nai sittin saba’in naka jira,

Mai saba’in ƙarya ana ta zunɗai nai.

A wannan zamani ƙarya ba ɗauketa laifi ba, musamman da wayar hannu ta zo. Domin son zuciya da raina zunubi sai mutum ya kantara ƙarya da waya ba kunya ba tsoron Allah.

8. YAUDARA KO SAƁA ALƘAWARI: Son zuciya ne ke sanya mutum yin yaudara. Wato ya san abu ba zai yiwu ba, amma sai ya nuna zai yiwu, daga baya ya fasa. Tun da farko shi wanda aka yi wa alƙawarin zai sakankance da al’amarin, a ƙarshe ya yaudareshi ya saɓa alƙawari.

 A al’adance Bahaushe na cewa: “Wani ya faɗa ya cika, ya faɗa bai cika ba Allah ya tsinewa mai ƙarya. Dalilin da yasa ake ɗaukar mayaudari a matsayin maƙaryaci kuwa shi ne, tun a zuciyarsa ya san ba zai yi ba, amma sai y ace zai yi. Duk wanda bai cika alƙawari na kallonsa ba dattijo ba ne. Aƙilu Aliyu yana cewa:

Malam nemi ɗiyar dattawa,

 sanda kake riya neman aure,

Ba mai gemu ko saje ba,

Ba mai faffaɗar riga ba,

Ba mai mota ko babur ba,

Mai Magana ka ji tamkar ƙyaure.

 A addiniance kuwa, ana ɗaukar mayaudari a matsayin munafuki mai fuska biyu. Kamar a wani Hadisi da Annabi (S. A. W) yake cewa: “Alamun munafuki uku ne: 1. In yai Magana ya yi ƙarya. 2. In aka amince masa, ya ci amana.

3. Idan ya yi alƙawari ya saɓa.

9. GIRMAN KAI: Wannan munguwar ɗabi’a babu abin da ke sanya wa a yita, sai son zuciya. Zuciyar mutum za ta riya mashi cewar ya fi kowa, sai shaiɗan ya rinƙa tunkuɗashi. Girman kai ne kan sanya mutum ƙin karɓar nasiha ko shawara, ko wa’azi, saboda yana ganin shi ya fi ƙarfin a faɗa masa Magana. Shaiɗan kan raɓe ne a bayan wani matsayi da mutumin yake da shi. Misali, mulki, wato shugabanci, ko wadata kamar dukiya ko ilimi. A irin nan sai shaiɗan ya rinƙa nuna masa ai kowa na ƙasa da shi. Alhali kuwa a Alƙur’an Suratul Luƙuman aya ta 13 zuwa 19 an nunawa mumini yadda zai girmama iyaye, da kuma yadda zai yi tafiya ban da taƙama, da yadda zai yi magana ban da ɗaga murya wato hargowa. Alhaji Aliyu Namangi Zariya yana cewa:

Shi fa girma kai hali ne,

Wanda ke cutar mutane,

Shi tafarkin gargara ne,

Wanda ko ke bi shi ƙone,

Ba san mafita a lahira ba.

 A addinnance Allah ya haramta girman kai. Domin Annabi (S. A. W) ya ce: “Duk wanda ya mutu da girman kai a zuciyarsa daidai da ƙwayar zarra ba zai shiga aljanna ba. ”

 A al’adance Bahaushe na cewa “Girman kai rawanin tsiya, don ya kan hana hanyar arziƙi”. A mafi yawan lokuta mutum mai girman kai bai cika yin kwarjini ba a cikin al’umma.

10. CIN AMANA: Son zuciya wato son rai, shi ke sanya mutum ya ci amana bayan an yarda das hi, amma kuma ya yi cuta. Akwai inda a kan samu cin amana ta fuskoki da yawa kamar: Karɓar ajiya ta dukiya ko kaya ko mutum ko dabba. Rike sirri ko rufa asirin wani na Magana ko na wani aiki. Misali, mutum ya daɗa maka wata Magana a matsayin sirri y ace amana kar wani ya ji. Kai kuma sai ka tafi ka bad a labara, to ka ci amana. Haka kuma idan aka baka ajiyarr wani abu, sai aka zo karɓa maimakon a sameshi yadda yake, son zuciya sai ya sanyaka ka ɓata shi ko ka cinye. Aliyu Namangi na cewa:

Kar ka so bidi’a ta zamna

 Zuciyarka balle hinaya,

kar ka zam mai so ka raina,

 ‘yan uwa ka tsare amana,

ka bi sunna ba da kangara ba.

11. SAƁON ALLAH: A mafi yawan lokuta son zuciya ko bin son rai shi ne kan ingiza wasu mutane aikata saɓon Allah, Shaiɗan da zuciya su ne ginshiƙan da suke tura mutane yin saɓon Allah. A nan ne ake hawa dokin zuciya sai daga baya mutum ya dawo yana nadamar abin da ya aiakata na ɓarna. A Suratul Hashri aya ta 16, inda Shaiɗan kan tura mutum ya yi saɓo, sai bayan ya aikata sai Shaiɗan yace: ba ruwa na da kai, ni ina tsoron Allah. Aliyu Namangi Zariya ya na cewa:

Ko da dai laifi tudu ne,

Naka wanda ka tattara ne,

Ke hawa ka gano na wane,

Ga mutum mai gargaɗI ne,

 Bai bar saɓon Ubangiji ba.

Mu Kaucewa Aikin Da Zai Jawo Mana Zargi:

 An samu wani Hadisi a muwaɗɗa a babin ittiƙafi, wanda ya yi bayanin cewa: Annabu (S. A. W) yana Ittiƙafi a masallaci, sai ɗaya daga cikin matarsa ta kawo masa ziyara. Ko da Annabi (S. A. W) ya fi to zai raka ta, sai wasu samarin Madina suka zo wuce wa, suka yi masa sallama suka wuce. Bayan har sun wuce, sai Annabi (S. A. W) ya kirasu, ya ce, “Zainab bintu Jashim, yace ni ne Muhammadu Ɗan Abdullahi wannan kuma Zainab mata ta. sai Annabi (S. A. W) ya ce, “a’a kamar yadda jini ke yawo yana zagayawa a jikin mutum, to haka Shaiɗan yake yawo a jikin mutum.

 Wannan Hadisi ya koyar da mu abubuwa kamar haka: Idan mutum yana ittiƙafi matarsa za ta iya kawo masa ziyara. Dole ne mutum ya yi ƙoƙarin kaucewa duk wani abu da zai sanya zargi a zuƙatan mutane. Wannan ya ƙara nuna mana haɗari ko illar keɓewa da mace don zai sanya ƙaiƙayi a zukatan mutane. Dole ne mutum ya guji tsayawa da mace a inda za a iya zarginsa, ko da matarsa ce.

Alaƙar mace da shaiɗan abu ne da yake a bayyane, wanda kuma aka yi bayanin haka a wurare da dama tun daga Al-ƙur’ani mai girma har ya zuwa hadisan Manzon Allah (S. A. W) , da kuma maganganun magabata. Baya ga wannan, ko a maganganun mu nay au da kullum a kan ci karo da karin maganganu, maganganun azanci da sauransu.

Tun farkon al’amari in muka dubi abin da ya faru tsakanin Annabi Adamu da Hauwa’u a Al-jannah, shaiɗan bai rinjayi Annabi Adamu ba sai ta hanyar Hauwa’u ya ci galabarsu ya yi sanadiyyar fitar su daga Al-jannah.

Suratul Baƙara: aya 36. Bayan wannan kuma, saboda alaƙar da ke tsakanin mace da shaiɗan, Manzon Allah (SAW) ya yi hani da a keɓe da mace, saboda da zarar sun keɓe to na ukun su shaiɗan ne, nan da nan kuma ba zai bar su ba sai ya yi sanadin da suka yi ɓarna. Haka kuma shaiɗan kan yi amfani da mace a matsayin wata kibiya da yake harbin mumini da ita. Yana da kibiyoyi guda biyu, in har ya harbi mutum da kuɗi ya ga bai same shi ba, to sai yasa ɗayar kibiyar ita ce mace. Shaiɗan kan yi amfani da mace a matsayin tarko na kama wasu mutane ta hanyoyi da yawa.

12. KAUCEWA CIN HARAM: Haƙiƙa an hana musulmai cin abin da yake haramun. Akwai wanda aka samu ta hanyar haram, kamar ta hanyar sata, ko ƙwace, ko yaudara. Haka kuma akwai wasu nau’o’in abincin da suke haramun ne, kamar wasu dabbobi da giya da wasunsu.

 Akwai Hadisin day a nuna cewar duk jikin day a ginu da haramun, to ƙarshensa wuta. Duk wanda ya ginu da haramun, ba za a karɓi addu’arsa ba. Duk da sanin haka sai son zuciya ya sanya wasu cin haram.

13. SHAWARWARI: Zamu fara da wata aya daga Ƙur’ani mai girma, mai cewa: Ita dai zuciya ba a bin ta. A Suratul Yusuf aya ta 53. Innan nafsa la’amaratu bi su’i, illa man rahima Rabbi. Lallai zuciya ta kasance mai ummarni da yin ɓarna, sai wanda ya tsare. A wata ayar kuma a Suratul Nazi’at aya ta 41, aka ce: “man hafa maƙama rabbihi wanahan nafsun anil hawa fa’inaj jannati hiyal ma’awa. ”. Duk wanda ya ji tsoron Allah ya ƙI bin son zuciyarsa, to aljanna ce makomarsa.

 A al’adance kuwa, Bahaushe na cewa: “Daga ƙin gaskiya sai ɓata”. Wanda wannan ne nufin duk aiki mara kyau ya ƙi ji ya bi son zuciyarsa, to zai kasance mai yin nadama. Kamar inda Bahaushe kan ce “Kowa ya ƙi jib a zai ƙi gani ba” ko wanda bai ji bari bay a ji hoho. Wannan na ƙara nuna mana illar bin son zuciya.

 Dole ne mu faɗawa kan mu gaskiya, haƙiƙa akwai wasu dabaru ko abubuwa waɗanda Bahaushe ya yi tanaji don sarrafa doki na haƙiƙa. Domin haka shi ma dokin zuciya akwai wasu dabaru ko abubuwa a ake amfani da su don sarrafashi. Ga guda uku daga ciki kamar haka: Linzami, da dabaibayi, da tarnaƙi.

1. Linzami na hana doki gudu ko tafiya, shi ne kamar birki ga abubuwan hawa na zamani. To shi ma dokin zuciya yana da linzami, shi ne kamar hakai hakuri da azzakar wato Ambato\n allah. Idan an ɓata maka rai ka ji fushi ya taso maka, to ka tuna Allah ka ambaceshi ta hanyar yin a’uzubillahi minas shaiɗanur rajim. Ko ka yi wata addu’a, sannan kuma ka yi haƙuri domin an ce “Haƙuri maganin zaman duniya”.

2. Dabaibayi, yakan hana doki yawo ko ya yi nisan kiwo. To shi ma akwai abubuwan da dokin zuciya kan hana shi yawo har ya ja mutum zuwa ga halaka. Dabaibayi kuwa shi ne barin yin garadama, wato jayayya, Bahaushe na cewa: “Gradama matsirar sababi an bar gamata ran wani bai ɓaci ba. Haka kuma an ce ja-in-ja shi ke kawo tsinkewa. Don haka duk inda ka lura gardama za ta kunno kai to ka kauce mashi.

A addinance Annabi ya hana jayayya ko gardama. Akwai inda yace ka bar gardama ko ta addini ce. Kamar yadda Aƙilu aliyu yake cewa:

‘Yan uwa ga shawara, In muna son gafara,

To mu yarda da ƙaddara,Sai mu gaskata lahira,

Kar mu ruɗu da duniya.

To mu juya gargaɗI, wanda shi ne zai biɗi,

Taimako in farfaɗi, aibukanta, na bankaɗi,

‘Yan kaɗan daga Duniya.

Kar ka dinga yawan fushi, Ban da kai wani babu shi,

Wanda zan auraniya.

Mu’azu Sa’adu Kudan yana cewa:

Ya Allah ka tsaremu da sharrin nan uku,

Sharrin Shaiɗan da kuɗi da na zuciya,

TUNA MUTUWA NA RAGE DOGON BURI:

 A wani Hadisi da ya zo a Littafin Kitabu Ahadis y ace: Mumini ya rinƙa tuna mutuwa, yawan tuna mutuwa na sanya mutum ya rage dogon buri.

DOGARO GA ALLAH: Matuƙar mumini ya dogara ga Allah, ya mayar da al’amuransa zuwa ga Allah to zai samu nutsuwa, kuma zai samu wadatar zuci, tare da samun mafita a rayuwarsa. Kamar yadda ya zo a Alƙur’ani mai girma: Duk wanda ya dogara ga Allah to Allah ya isar masa. Kuma duk wanda ya ji tsoron Allah zai samar masa mafita.

 JIRWAYEN SON ZUCIYA A ADABIN BAHAUSHE:

 Akwai inda aka samu jirawayen son zuciya a adabin Bahaushe da dama. Kamar a Karin Magana, Alal Misalai: -

v Dokin zuciya mutum biyu ba sa hawanka.

v Son zuciya ɓacin zuciya.

v Ba a bin son zuciya don ba ta ƙashi.

v Zuciyar mutum burinsa.

v Ƙafa ba ta zuwa inda zuciya ba ta je ba.

v Zuciya mai mugun nufi.

v Saurin fushi na kawo da-na-sani.

v Karayar zuciya mafi karayar ƙafa lalacewa.

v Zuciya kin fi tukunya tafasa.

v Sunɓulalle marar kishin zuciya.

v Dokin zuciya ba ka jin linzami.

v Aikin da zuciya ta ɗauka ba a jin nauyinsa.

WASU ABUBUWAN LURA:

 Babu wani abu mai yi wa dokin zuciya zagi, wato jagora, kamar shaiɗan ko wakilansa. Ana iya samun na sarari ko na ɓoye, Misali, Aljani ko mutum, mace ko namiji. Da zarar mutum ya hau Dokin zuciya zai kasance ba ya sauraron kowa, ba ya jin nasiha, a lokacin kuma ko an ba shi haƙuri ba zai yi haƙuri ba.

 Duk wanda ya hau dokin zuciya ya kan rasa wasu abubuwa, kamar haƙuri, da kunya, da hankali. Ma’ana yakan yi haukar wucin gadi a wani lokaci ma har tunani yakan rasa. Amma kuma yana sauka daga dokin zuciyar, sai ya dawo hayyacinsa a ƙarshe ya fara nadamar aikin da ya aikata.

 Duk wanda ya hau dokin zuciya zai iya cin mutuncin kowane ne, babu maganar ragowa domin idanunsa sun rufe.

 Duk wanda ya hau dokin zuciya bai san ya kamata ba. A wurinsa ba babba ba yaro. Mahanar tausayi ko haƙuri babu.

 Duk wanda ya hau dokin zuciya bai damu da muhallin da yake ba. Babu ruwansa da kunyar kowa zai yi abin da yake so, sai ya biya buƙatarsa shaiɗan ya sake shi, sai ya fara nadama. Mafi yawan masu aikata laifi ba sa sauraron nasiha, sai a ƙarshe sun faɗa hannun hukuma ko an kai kotu, sannan su kan yi nadamar cewar, ai wane abokina ne ya ja shi suka aikata laifin. Aliyu Namangi Zariya:

Haka zai riya ma da sata,

Hassada, kushe da ƙeta,

Sa ƙazaf da yawan mugunta,

Manta sallah a lokacinta,

Zunubi ne ba abin musu ba.

Yawancin masu waɗannan ayyuka, shaiɗan ne kan ƙawatawa zuciya ita kuma ya ingiza mutum ya aikata, shaiɗan kan sanyawa mutum asurka a hancinsa ya yi masa jagora har sai ya aikata ɓarna sannan ya kauce ya bar shi yana nadama. Bayan shaiɗan

RIYA: Yin aikin alheri don wani ko wasunsu don su gani su yabawa mutum. Ko kuma bayan an yi aikin alherin mutum ya rinƙa bayar da labari, don a ji a yaba masa. A Suratul Baƙara aya ta 264, inda aka hana mumini yin gori, da zobe, da riya, saboda dukkansu suna ɓata aikin alheri.

ROWA: Ƙin bayar da wani da mutum ya mallaka ga kowa. Rowa ita ce kishiyar kyauta, rowa na haifar da ƙiyayya da ƙyamar juna.

RAINI: Na nufin rashin girmama kowa da ganin fifiko a kan kowa raini kan sanya mutum ya ƙi sauraron kowa ta fuskar nasiha ko shawara balle kuma wa’azi. Duk wanda yake da raini a ransa to bai ganin darajar kowa, babu wanda ya isa sais hi. Duk mai raina mutum za ka sameshi da ɗagawa wato girman kai. A wurinsa tunaninsa ya fi na kowa, duk wanda ya yi wani aiki ko wani tutiya faɗi wata Magana in ba shi ba to ba daidai ba ne.

GORI: Ka yi wa mutum kyauta ko wani alheri ko taimako sannan daga baya ka goranta masa. Ka rinƙa cewa “ka ga kamar ban yi masa kaza ba, ko ni na ba shi kaza ba”. Tabbas gori na ɓata aikin alheri. A Suratul Baƙara aya ta 264, inda aka hana mumini yin gori, da zobe, da riya, saboda dukkansu suna ɓata aikin alheri.

ZOBE: Bayan mutum ya yi wa wani mutum kyauta, sai kuma daga baya ya dawo ya ƙwace. Duk wannan na faruwa a sakamakon son zuciya. Musamman na bayan an ɓata wa mutum rai wato ya yi fushi. A Suratul Baƙara aya ta 264, inda aka hana mumini yin gori, da zobe, da riya, saboda dukkansu suna ɓata aikin alheri.

ZUGA: Ingiza wani don ya aikata wani mugun aiki, ta hanyar faɗa masa wasu kalmomi da za su tunzura shi. A ƙarshe sai a samu tashin hankali a tsakanin mutane.

GANGANCI: Yin wani abu bisa kasada ko da kuwa an san mutum zai cutu sai ya aikata saboda son zuciya. Aliyu Nmangi Zariya y ace a Littafinsa na Infiraji:

Kar ku yarda da cin amana,

Ko mutum mai son hiyana,

Ko gani balle ka zauna,

Wanda ka san fasiƙina,

Ba a yarda kuyi abokantaka ba.

Annabinmu y ace da tsoka,

Ɗaya mutum a cikin jikinsa,

In ta ɓaci duk jikinka,

Ma’ana ko zuciya ya duba.

Zuciya ita goɗiya ce,

Wanda duk ya sake ta goce,

Sai ta kai shi cikin wuta ce,

Kar ka sau ragama ta kauce,

Ta fice da guda ta aika ɗanya.

Gyaruwanta barin ayyuka,

Masu janye ƙafa su kaika,

Nan da nan a cikin tarukka,

Wanda ko a zatonka,

Ba ka riski abin da kai nufi ba.

Shi fa girma kai hali ne,

Wanda ke cutar mutane,

Shi tafarkin gargara ne,

Wanda ko ke bi shi ƙone,

Ba san mafita a lahira ba.

Masu cin rashawa da soke,

Masu fince da masu tarke,

Mai ganin nassi ya take,

Zuciyarsa ba za ta warke,

Su yi nesa da cin haramiya ba.

KAMMALAWA:

A ƙarshe dai wannan muƙala ta yi nazari ko bayani a kan son zuciya ko son rai wanda aka yi masa kinaya da abokin zuciya. An kawo ma’anar son zuciya da dalilan da kan jawo haka, haɗarin haka ko illolin. Nazarin ya kawo wasu shawarwari da za su taimaka domin samun mafita. Muƙalar ta ɗora bayananta a kan mahangar addini, sannan da mahangar al’adar Bahaushe, da kuma bayani a kimiyance.

MANAZARTA:

Aliyu A (1976) , Fasaha aƙiliya. Northern Nigerian Publishing Company. Zaria

Bunza AM (2000) Muhallin Hankali Da Bagiren Hauka A Hausance” Muƙala cikin mujallar Hausa Studies22: 122 Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.

Gumi A. (1980) Fassara Arba’unna Hadis. Northern Nigerian Publishing Company Zaria.

Gumi A (1970) Fassara Hausa Alƙur’ani mai girma, Hadimaini Haramaini Makka.

Namangi A (2012) , Waƙoƙin Infiraji a kammale Juz’ul na 1-9. Northern Nigerian Publishing Company, Zaria.

Harold. I. K. (1994) Synopsis Psychiatry Behavioural Sciences/Clinical Psyciatry. Eight Edition.

Imam A (1989) , Magana Jari ce. Littafi na ɗaya. Northern Nigerian Publishing Company Zaria.

Tafida U (1870) , Jiki Magayi. Northern Nigerian Publishing Company Zaria

Imam A (1939) , Ruwan Bagaja. Northern Nigerian Publishing Company Zaria.

Sa’adu M (2010) , Zuciya Sarauniya Ce. Unpublish Book.

Lawrence M. B. (1960) Therapeutic Counseling and Psychotherapy. PrintedIn Engfewood Cliffs New Jesey USA.

Malik I (Ba Shekara) , Muwaɗɗa Malik. Darul Fika Beirut Lebanoon.

 Hausa Post

Post a Comment

0 Comments