WANDA AKA GABATAR A TARON WALIMAR AUREN MUHAMMAD TANIMU HARUNA DA ZAINAB MUHAMMAD TAHIR A BADARAWA GARIN KADUNA A RANAR ASABAR 15 GA MARIS 2014, DA ƘARFE 04: 00 NA YAMMA.
JIBADAU KAYAN NAUYI (WANDA YA CE BABU YI MASA AKA YI): TSOKACI
A KAN RAYUWAR AURE DA KUMA MATSAYINTA
DAGA
MU’AZU SA’ADU KUDAN.
DEPARTMENT OF NIGERIAN LANGUAGES
JIGAWA STATE UNIVERSITY KAFIN HAUSA. (07030803404)
SHIMFIƊA:
JIBADAU: Wata ƙatuwar babbar riga ce, daga
cikin nau’o’in girke ta saƙi, ko ta tsamiya, ko
fari. [1]
KAYA: Dila, ko agigi, ko laftu wanda za a iya ɗauka a kai ko a kan
dabba. [2]
NAUYI: Duk abin da za a ɗaga, ko a ɗauka, ko jijjina a gaji, ko ya gajiyar. [3]
GABATARWA.
Da sunan
Allah Mai rahama Mai jinƙai, Mai kowa, Mai komai,
Mai aikata abin da Ya so, ga wanda Ya so, a sadda Ya so, a yadda Ya so, ko ana
so, ko ba a so, dole bayi su so. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban
halittu Annabi Muhammadu, da Alayensa da Sahabbansa.
Wannan muƙala z ata ɗan taɓo, wani abu da ya shafi rayuwar aure da matsayinta. Wannan rayuwa
ta aure saboda muhimmancin da take da shi, ga dukkan wani abu mai rai. Tun daga
mutum har dabbobi, da tsuntsaye, ƙwari, da tsirrai. Bisa
wannan dalili ya sanya Bahaushe ya bai wa aure babban matsayi. A inda yake
ganin duk namijin da ya riƙa (balaga) , ma’ana ya isa
aure amma bai yi ba, a matsayin mai rauni kuma ba cikakken mutum ba. Bahaushe
ya karkasa mutane marasa aure zuwa gida uku ko huɗu. Kamar haka, saurayi, ko tuzuru, ko gwadangwarƙi, ko gwauro, idan kuma mace ce sai a ce mata budurwa, ko karfa,
ko bazawara, ko gwauruwa. Kowane daga cikinsu akwai irin matsayinsa a al’adar
Bahaushe, tare da dalilai da suka sa aka bashi sunan. Haka kuma, saboda sanin
irin ɗawainiyar
dake tare da aure, musaamman ga sabon shiga,sai Bahaushe ya yi masa kirari da
dama. Wannan yasa na kira muƙalar da suna “Jibadau
kayan Nauyi’’ (Wanda yace babu yi masa aka yi). Ma’ana gashi aure yana
cikin matakan rayuwa da ya zama kusan dole, to amma kuma ana tunanin abubuwan
da suke tare da shi. Wannan muƙala zata tsakuro wasu
dalilan da suka Bahaushe ya faɗi wannan kirari mu kallesu, don mu ga irin tasirin da suka yi.
Bugu da ƙari, an kawo falalar da yin aure ke da shi, tare da kwaɗaitarwar da shari’ar
addinin musulunci ta yi. Bayan haka kuma, an jero wasu haƙƙoƙi da suke kan ma’auratan.
MA’ANAR
AURE:
Aure wani zama ne halastacce tsakanin mace da namiji a
matsayin mata da miji wanda al’ada da Addini suka yarda da shi. Babban dalilin
da yasa ake yin aure shi ne domin yaɗa iri tare da fatan al’umma ta wanzu. Aure baya inganta sai da rukunai kamar haka: sadaki, waliyi,
shaidu.
Bisa
wannan dalili, duk wanda ya ƙetare iyaka ya kutsa wata
mace ba tare cika waɗancan rukunai ba. Haƙiƙa ya saɓawa shari’a da kuma al’ada, saboda ladabtarwa shari’a tace ba
aure. Al’ada ta bashi sunaye, sannan kuma ta kira aikin da ya yi da sunaye
kamar haka:
Za’a kira
shi Kwarto, ya yi kwartanci, ko shige, ko fyaɗe. Ita matar kuma a kira ta farka, ko dadaro. Matar da kuma ta
sallamar da kanta ga kowa, ana kiranta karuwa. Shi kuwa ɗan ko ‘ya da aka haifa ba
ta hanyar aure ba, akan kira su da shege, ko shegiya, ɗan rariya, ko ɗan gaba da fatiya, ko ɗan dakan-kuka da sauransu.
FALALAR YIN AURE
Tabbas akwai falala a kan aure mara iyaka wadda ba
za tya bayyanu ba sai dai a ɗan tsakuro kamar yadda
shari’a ta yi umarni da a yi aure tare da nuna muhimmancinsa, to haka ita ma
al’ada ta bayyana falalar aure ga al’umma. Falalar aure da ɗan Adam ke samu sun haɗa da: -
1. Cikar mutunci. 2. Natsuwa. 3. Kamun kai. 4. Runtse
idanu. 5. Yaɗa zuriyya (haihuwa)
UMARNIN YIN AURE: Bayan wannan falala kuma, sai maganar umarni
da shari’a ta yi a kan yin aure a Al-ƙur’ani aka ce:
وإن خفتم ألا تفسطوا فى اليتامى فانكحوا ما طاب
لكم من النساء مثنى وثلاث ورباع، فإنخفتم ألا تعدلوا فواحدة أو ما ملكت أيمانكم،
ذالك أدنى ألاتعولو.
“Ku auri abin da ranku yake so daga bibbiyu,
uku-uku, ko hur-huɗu, in kunji ba za ku yi
adalci ba, to ku tsaya a guda ɗaya”. Abin nufi shi ne ku auri mata 2 ko 3 ko 4 in
ba za ku iya adalci ba mata ɗaya (1).
Wani hadisi yace ku yi aure
ku hayayyafa ranar ƙiyama in yi alfahari da ku. Ko wani hadisin da yace: “Ku
yi aure samari shi yafi runtse idanu.
GIRMAMA MACE SABODA MATSAYINTA
Duk inda ka ga mace ka girmama ta saboda wasu
dalilai kamar haka: matsayin da Allah Ya bata na Uwa ga dukkan mahaluki kuma
makarantar farko ga dukan mahaluki.
1. Matar wani. 2. Uwar wani. 3. Kakar
wani.
Da farko dai ya zama wajibi a girmama mace bisa wasu
dalilai, na farko shi ne duk in da ka ga mace kamila to dole ne ta kasance
cikin ɗayan uku ko dai matar wani
ko uwar wani ko kakar wani, ko da yake wannan na ƙarshe ya danganci
shekarunta.
عن أنس رضى الله عنه قال: قال النبى صلى الله عليه وسلم قال: إذا
تزوخ العبد فقد استكمل نصف الدين, فليتق الله فى النصف الباقى.
An karɓo daga Anas (R. A) yace
Annabi (S. A. W) ya ce idan mutum ya yi aure to ya sami rabin Addininsa sauran
rabin sai ya ji tsoron Allah ya cika sauran. (Jami’ul hadis: Imamus-suyuɗi).
GIRMAMA MACE A MATSAYIN MATAR AURE
Akwai dalilai masu yawa da suka sa mutum dole zai girmama
mace ko ba don komai ba, ko saboda wani matsayi da take da shi al’umma na farko
a matsayin matar aure, wani babban mataki ne na rayuwa ga dukkan namiji. Babu
wani wanda rayuwar sa za ta kammala in ba shi da aure. To ashe kuwa in har haka
ne to mace ta zama abokiyar rayuwa, kuma abokiyar rufin asiri ga mai ita. Wata
hujja itace Allah (S. W. T) yace a cikin Al-ƙur’ani cikin Suratul Baƙara aya ta 237 ya ce miji
da mata tufa ne ga juna, sannan yace a Suratul Baƙara aya ta 228, 29-30 cewa
mata da miji a yi karamci ga juna.
Bayan wannan kuma, irin gudunmuwar da mace take bayarwa a
fagen aure wanda ba za su lissafu ba, kaɗan daga ciki sun haɗa da:
1. Kula da miji shi kansa.
2. Kula da gida da iyali.
3. Karewa da ƙarawa mutum mutunci a cikin al’umma.
4. Tsare kai daga faɗawa cikin wasu munanan ayyuka.
5. Runtse idanunsa daga wasu matan daban.
6. Taimakawa wajen samun zuriyya (yaɗa iri).
7. Matar ƙwarai na sanya miji ya yi
alfahari.
8. Ƙulla
zumunci da sauransu.
Wani sirri
kuma abin
mamaki game da dangantakar aure, ga ma’auratan nan biyu. Watau
mata da miji, shi ne kula da juna musamman aka ce auren farko tsakanin saurayi
da budurwa. Matuƙar an yi shi bisa so da ƙauna kuma an amincewa juna. To za
ka iske babu mai son ya rabu da juna, domin
samun kulawa. Akwai wata magana da masana ɗabi’ar Ɗan Adam suka yi na cewa duk wanda ya rasa matar farko ko
mace ta rasa mijin farko to da wuya ya/ta sake samun dai-dai sai kawai haƙuri. kai ko da wajen ba shi
shawara mai kyau.
A mafi yawan lokutta akan samu a inda mata ke kula da
miji kuma har ta rinƙa lallashi da tattalinsa da kayansa kamar ɗanta ko na ƙaramin yaro ko da baya nan
kuwa.
Ban da wannan kuma, mata kan kula da gida tare da
iyali kai a wani lokaci har da dangi. Tun daga yi mu su abinci raino, tsabtar
jiki da ta tufafi (wanka da wanki) tarbiyya.
Mace ga mijinta takan zama ƙyaure da kuma ado ko
garkuwa ta mtunci a cikin al’umma. Game da wannan babu jayayya bisa ga wasu
dalilai kamar haka: ko ba shari’a a ɗabi’a ma kawai ya isa hujja a mutane musamman Hausawa
matuƙar aka ce ga namiji ya kai wani matsayi na minzalin isa
aure aka ce bai yi ba, har suna akan bashi da cewar “tuzuru”, ko “gwadankwarƙi”,/”goriyo”, shi kuwa
wanda matar ta fita watau ya taɓa yin aure amma suka rabu
to shi akan kira shi da “gwauro”. Haka ita
ma macen akan ce “karfa” ko kuma ta rabu mijin a ce “bazawara” ko a tsokaneta
da “gwauruwa”.
Wata daraja da Allah (S. W. T) ya baiwa matar aure ga
miji ba ƙarama ba ce, saboda falalar da miji kan samu a dalilin
yin aure, kamar a inda wani hadisis ya nuna ko da kallon fuskar matarsa kawai
ya yi, za a rubuta ma sa lada. Ga hadisin kamar haka:
“An karɓo daga Abu Hurairah (R. A)
cewa: Ya ji Manzon Allah (S. A. W) idan namiji ya dubi fuskar matarsa, Allah
(S. W. T) zan rubuta masa ladan kyawawan ayyuka guda ɗari a cikin littafinsa na lada, idan ya kama hannunta,
kuma ya sadu da ita, Allah Zai rubuta masa lada a kan kowanne silin gashin da
ke jikinsa, idan ya yi wankan janaba Allah Zai halicci Mala’ika a kan
kowanne ɗigon ruwan da ya ɗiga a ƙasa a lokacin da yake yin
wankan. Kowane Mala’ika zai rinƙa yi wa Allah tasbihi, kuma yana roƙa masa uban giji tun daga
wannan lokacin da ya yi wankan har zuwa ranar lahira. Kuma ladan dukkan
tasbihin da Mala’ikun za su yi za a rubuta masa ne a cikin littafinsa na lada.
Idan matar ta yi sa a ta ɗauki ciki a wannan saduwar,
dukkan mala’ikun da ke cikin Al’arshi da kifayen dake cikin ruwa za su rinƙa roƙa masa lahira gurin
ubangiji. Ita matar kuwa za a rinƙa rubuta mata lada guda dubu a kankare mata zunubai dubu,
kuma a bata ladar da mutane suka fita yaƙi (jihadi).
ZAƁARWA 'YA'YA UWA TA
GARI: Wajibi
ne ga dukkan mahaluki mai hankali da yayi niyyar yin aure, to ya yi ƙoƙarin zaɓarwa 'ya'yansa uwa ta gari, ma'ana mai
tarbiyya da son addini. Kar ya bi son zuciya ya auro mace don kyau, watau
kyakkyawa, ko 'yar wane, watau mai nasaba (mai kuɗi, sarauta, muƙami). Wannan
magana ta yi dai-dai da wani bayani da Manzon Allah (S. A. W) ya yi cewa ku
auri mace ma'abuciyar addini. Domin yace in ka aura don kyau to lallai kyau
kan ƙare in ta tsufa, ko nasaba don mulki na iya ƙarewa, amma shi addini ba ya ƙarewa.
Bayan
haka, zaɓarwa
'ya'ya uwa ta gari kamar hutar da kai ne, domin in ka haifi yara da mace
ta ƙwarai. To kamar ita ce makarantar su don zasu koyi komai na ƙwarai daga wurinta. Saboda masu hikima sun ce uwa itace makarantar
farko ga yaro. Haka kuma in mutum ya kurkure ya auri Ballagazar mace mara
tarbiya. To ya kashe kansa da kansa, kuma yaransa sun shiga uku. Babban dalili
shi ne, ita ba ta da tarbiya, ba ilimi balle addini, to a nan ina makarantar
farko take? Sai dai su koyi zagi da miyagun halaye.
KOWA NA
DA HAƘƘIN DA YA RAYATA A WUYANSA.
Akwai haƙƙi na ƙasa ko ƙarami ko mai rauni ko talaka, akan na sama, shugaba, iyaye da duk
wani jagora. Wajibi ne a tsare-tsare da lura da waɗannan haƙƙoƙi ta kowacce fuska. Wani hadisi wanda Bukhari da Muslim suka
ruwaito, wanda yayi bayani a kan cewa duk wani jagora akan al'amari to lallai
ne ya tsare amana da aka bashi. Domin kuwa za a tambaye shi ranar lahira. Ga
yadda hadisin yake kamar haka: -
وعن ابن عمر رضى الله عنهما قال: سمعت رسول الله
صلى الله علسه وسلم يقول: كلكم راع, وكلكم مسئول عن رعيته, ألإمام راع, ومسئول عن
رعيته, والجل راع فى أهله ومسئول عن رعيته, والمرأة راعية فى بيت زوجها, ومسئولة
عن رعيتها, والخلدم راع عن مال سيده ومسئول عن رعيته, فكلكم راع, ومسئول عن رعيته.
متفق عليه. رواه البخارى و مسلم.
An
karɓo daga
Ibn Umar (R. A) yace: Naji Manzon Allah (S. A. W) yace: "Dukkan ku
makiyaya ne, kuma dukkan ku abin tambaya ne a kan abin da aka bashi kiwo.
Shugaba abin tambaya ne a kan na ƙarƙashin sa. Kowane mutum mai kiwo ne a kan iyalan sa, kuma abin
tambaya ne, ita kuma mace mai kulawa ce a kan dukiyar (gida) mijinta, kuma abin
tambaya ce a kan su. Mai yin hidima (bara) , mai kulawa ne ga dukiyar uban
gidansa, kuma abin tambaya ne a kan su. Dukkan ku makiyaya ne kuma abin kulawa
ne. An yi ittifaki a kan wannan hadisin. (Bukhari da Muslim suka ruwaito shi).
Shari'ar
musulunci ta tsoratar da cewa duk wanda ya take haƙƙin wani ɗan'uwansa na kusa ko nesa, musulmi ne ko wanda ba musulmi ba? Kai
hatta dabbobi su ma an yi hanin a cutar da su haka kurum.
Haka
kuma shari'ar musulunci ta kwaɗaitar tare kuma da yin albishir ga duk wani mahaluki da ya tsare
tare da sauke haƙƙin wani da yake kansa, baya ga tarin lada da falala da ƙauna da zai samu a nan duniya, sannan kuma ga tanajin gidan
aljannah. Misali a cikin Al-ƙur'ani a cikin Suratul
Zilzilat inda Allah (S. W. T) yace: فمن يعمل مثقال ذرة خيرا يره.
"To,
wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarrah, na alheri, to zai gan
shi". ومن يعمل مثقال ذرة شرا
يره.
"Kuma
wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarrah na sharri, zai gan shi".
HAƘƘIN MATA A KAN MIJINTA: Matar
aure da na haƙƙoƙi masu yawa da suka zama tilas mijinta da yake aurenta ya tsare
su. Tun da farko dai shari'a ta sharɗanta babu aure sai da abubuwa uku, sune waliyyi, sadaki, sai kuma
shaidu. Daga cikin waɗannan abubuwa guda uku to ɗaya shine mafi ƙarfi a cikinsu a matsayin
haƙƙi na ita matar, shi ne sadaki, domin kuwa wajibi a baiwa mace
sadakin ta a hannun ta, ko kuma a saya mata wani abu muhimmi wanda za ta rinƙa amfani da shi.
Bayan waɗannan kuma, sai maganar
wasu haƙƙoƙin kuma, bayan an ɗaura are, wajibi ne miji ya tsare su, sune ciyarwa, shayarwa,
tufatarwa, ɗakin kwana, sannan da biya mata buƙata wajen
kwanciya. Matuƙar aka rasa ɗaya daga cikinsu, to ana iya raba aure.
Bisa ga
maganar magani kuwa, baya cikin sharaɗin aure, cewar mutum ya yi wa matarsa magani ba ta da lafiya, sai
dai in ya yi mata maganin to ya kyautata, amma ba dole ba ne. Sai dai kuma
malamai sun yi Ijtihadin cewar in miji ya yi wa matarsa magani to ya kyautata,
haka ita ma ba dole ne ta yi masa girkin abinci ba, amma in ta yi to ta
kyautata.
An karɓo daga Amru Ɗan Ahwas, Aljushami (R. A) , yaji Annabi (S. A. W) a hajjinsa na
bankwana bayan ya yi yabo da godiya ga Allah, kuma ya yi wa'azi, kuma ya yi
gargaɗi, sannan
yace: "Ku saurara! Ku karɓI wasiyyar alheri dangane da al'amarin mata, lallai su (mata)
kamar kamammu ne, a wurinku baku mallaki komai ba a kan su in ban da (igiyar
aure) , sai dai in sun zo da alfasha bayyananniya. Idan sun aikata (alfasha) ,
ku ƙaurace musu a wurin kwanciya, ku buge su duka ba mai tsanani ba.
Idan suka yi muku biyayya kada ku nemi wata hanyar kama su da laifi. "
"Ku
saurara! Lallai kuna da haƙƙi a kan matan ku, kuma
matanku suna da haƙƙi a kan ku. Haƙin ku a kan su shi ne kada
su zaunar da wanda baku so a kan shimfiɗar ku, kuma kada suyi wanda baku soizinin shiga gidajen ku. Ku
saurara! Haƙƙin su a kan ku shi ne ku kyautata musu, tufatarwa da ciyarwa.
" Imam Tirmiziy ya ruwaito.
An
karɓo daga
Mu'awuya Ɗan Haida (R. A) yace: Ya Manzon Allah! Mene ne haƙƙin matar ɗayan mu a kan sa? Sai yace: "Idan ka ci, kaciyar da ita, ka
tufatar da ita idan ka tufatu, kuma kada ka doke ta a fuska, kuma kada ka
musguna mata, kuma kada ka ƙaurace mata sai a
cikin ɗaki.
"
An
ruwaito daga Abdullahi Ɗan zama'a (R. A) cewa:
Annabi (S. A. W) yayi wa'azi dangane da al'amarin mata, yace yanzu ɗayanku zai tasarwa matarsa
ya yi mata duka irin dukan bawa, sannan kuma idan dare ya yi ya kwanta da ita?
Bukhari da Muslim suka ruwaito.
HAƘƘIN MIJI A KAN MATARSA: Akwai haƙƙi mai nauyi kuma mai girma da miji ke da shi a kan matarsa wanda
ya shafi na girmamawa na, bin umarni ko hani. Haƙiƙa biyayya ga miji ba ƙaramin al'amari ba ne,
saboda ko da sha'awa ta taso wa miji in ya buƙaci
matarsa to dole ne ta masa kira, domin kuwa matuƙar taƙi to lallai za ta shiga fushin Allah, saboda in har mijinta na
fushi to sai ta bashi haƙuri sannan za ta kuɓuta.
وعن أبى هريرة رضى الله عنه قال: قال رسول الله
صلى الله عليه وسلم: إذا دعا الرجل امرأته إلى فراشة فلم تأته فبتا غضبان عليها
العنتها الملائكة حتى تصبع. متفق عليه.
An karɓo daga Abu-Hurairah (R. A)
, yace Manzon Allah (S. A. W) yace: Idan miji ya kira matar sa zuwa shimfiɗarsa, watau ya nufi ya
kwanta da ita amma ta ƙI, ma'ana ta ƙi yarda da shi, har shi mijin ya yi fushi da ita, Mala'iku zasu yi
ta tsine ma ta har zuwa asuba. Bukhari da Muslim suka ruwaito.
فى رواية قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: والذين نفسى بيده
ما من رجل يدعوامرأته إلى فراشة فتأبى غليه إلاكان الذى فى السماء ساخطا عليها حتى
يرضى عنها.
A wata
ruwayar, an ce Manzon Allah (S. A. W) yace: Na rantse da wanda raina ke hannun
sa, babu wani miji wanda zai kira matar sa zuwa shimfiɗarsa don su kwanta amma
ta ƙi, har sai waɗanda suke sama (Mala'iku) sun yi fushi da ita har sai ya yafe ma
ta.
Akwai wani hadisi
ya ƙara nuna ƙarfin yin biyayya ga miji,
kamar inda Manzon Allah (S. A. W) ya ce da zan yi umarnin wani ya yi wani
sujada da na umarci mata ta yi wa mijinta sujada.
Bayan
wannan kuma akwai wani hadisi kuma da yake nuna matsayin haƙƙin miji kamar inda aka yi bayanin cewa Aljannar mace tana ƙarƙashin duga-dugin mijin ta in ta bi shi, ta shiga Aljannah.
Bugu
da ƙari, akwai inda aka nuna cewa ko da ibada ce mace za ta yi, sai ta
nemi izinin mijin ta, kamar misalin azumin nafila, hadisi ya nuna cewa ta sanar
da miji, ko ta nemi izini sannan ta ɗauka.
Duk
dai a kan nuna girman biyayya ga miji, inda aka nuna ko da mace tana tuya
gurasa ko waina, in har miji ya nuna yana buƙatar ta,
wato sha'awa, manufa yana so ya kwanta da ita, to dole ta amsa kira, ta je su
kwanta, ya biya buƙatarsa ko da kuwa gurasar ko wainar za su ƙone.
Akwai
bayani da ya zo da ya nuna a lokacin Manzon Allah (S. A. W) yana raye a zamanin
wata matar wani sahabi ya yi tafiya sai aka aiko cewa mahaifin ta bashi da
lafiya, don haka sai ta aika tana neman izini daga wurin Annabi (S. A. W) don
ta tafi ta dubo shi, Annabi yace shin mijin ta ya bata izini? Sai tace a'a, sai
yace to ta haƙura. Bayan haka sai kuma aka aiko cewa mahaifinta ya rasu, duk da
haka ba ta fita ba, ta haƙura har sai da mijin ta ya
dawo. A kan wannan ne Annabi (S. A. W) ya aiko cewa an sanar da shi cewa an
gafarta wa mahaifinta, saboda biyayyar da ta yi, duk da mijin ta baya nan, kuma
ta haƙura har ya dawo.
BIYAYYA
GA MIJIN TA. Biyayyar mace ga mijinta
wajibi ne, saboda wani hadisin da Annabi (S. A. W) yai umarni cewa: Da mutum
zai iya yiwa wani mutum sujada da an umarci mata ta yi wa mijinta sujada. To
amma da yake ba zai yiwu ba, ba a yi wa kowa sujada sai Allah (S. W. T) , amma
shari'a ta yi umarni mace ta yi wa mijin ta biyayya matuƙar dai bai umarce ta da ta yi saɓon Allah ba.
DA WANI ZAI IYA YI WA WANI
SUJADA, DA MATA TA YI WA MIJINTA.
وعن أبى هريرة رضى الله عنه، عن النبى صلى الله عليه وسلم قال:
"لوكنت أمرا أحدا أنيسجد لأحد، لأمرة المرأة أن تسجد لزوجها. رواه الترمذى
حديث حسن صحيح.
An
karɓo daga
Abu hurairah (R. A) , daga Manzon Allah (S. A. W) yace: Da mutum zai iya yiwa
wani mutum sujada da an umarci mata ta yi wa mijinta sujada. Tirmiziy ne ya
ruwaito shi.
MACE BA
ZA TAYI AZUMIN NAFILA BA SAI DA IZININ MIJIN TA.
وعن أبى هريرة رضى الله عنه أيضا، أن رسول الله
صلى الله عليه وسلم قال: لايحل لأمرأة أن تصوم وزوجها شاهدا إلا بإذنه، ولا تأذن
فى بيته إلا بإذنه. متفق عليه، وهذا لفظ البخارى.
An
karɓo daga
Abu hurairah (R. A) yace: Manzon Allah (S. A. W) yace: "Bai halatta ba ga
mace ta yi azumin nafila ba kuma mijin ta na nan, sai da izinin sa. Kuma ba za
ta shigar da wani cikin gidansa ba sai da izinin mijinta. Bukhari da Muslim
suka ruwaito.
HAƊARIN BUTULCEWA MIJI.
عن ابن عساكر، عن عائشة رضى الله عنهما: قال النبى صلى الله عليه
وسلم: إذا قالت المرأة لزوجها ما رأيت منك خيرا قط فقد حبط عمنها.
An karɓo daga Ɗan Askar, daga Aisha (R. A) tace: Annabi (S. A. W) yace: "Duk
macen da ta wa mijinta bata taɓa ganin alheri daga wurin sa ba, to haƙiƙa ta ɓata ayyukan ta.
ADADIN
MATAN ZA A IYA AURA: A tsari irin na shari'ar
musulunci, ba a bar komai haka ba, sai da aka yi masa iyaka tare da ƙa'idoji. A kan wannan ne, aure ma ba a bar shi haka ba, sai da aka
shimfiɗa ƙa'idoji da hukunce-hukunce. Allah (S. W. T) a cikin Al-ƙur'ani ya ƙayyade ko iyakance adadin
mata da za a iya aura tun daga mata biyu ko uku ko huɗu, amma sai aka yi gargaɗI in mutum ya san ba zai yi
adalci a tsakanin matansa ba, to ya auri mace ɗaya.
وإن خفتم ألا تفسطوا فى اليتامى فانكحوا ما طاب لكم من النساء مثنى
وثلاث ورباع، فإنخفتم ألا تعدلوا فواحدة أو ما ملكت أيمانكم، ذالك أدنى ألاتعولو.
MATAN DA
SUKA HALASTA A AURA.
Allah (S.
W. T) ya baiwa mata wani irin matsayi a ƙarƙashin inuwar shari'ar Musulunci, wanda babu wani tsari da aka taɓa samu a kafin musulunci da
kuma nan gaba.
Wannan
irin matsayi ya sanya dole a girmama mata. Allah (S. W. T) cikin hikimar sa ya
halasta yin aure, to amma duk da haka, sai ya tsara mata kashi biyu, kashi na
farko ya haramta aurensu ga dukkan mutum musulmi, kashi na biyu kuwa waɗanda basu faɗa cikin waɗancan da aka ambata ba da
farko, ya halasta su, watau za a iya auren su.
MATAN DA
SUKA HARAMTA A AURA: Shari'ar musulunci ta
haramta auren wasu mata ga musulmai maza. Wannan haramci ya dogara ne bisa ga
wasu dalilai, sannan kuma an kasa kashi huɗu kamar haka: -
1. Akwai
mata waɗanda
dangantaka ta jini (haihuwa).
2. Akwai
mata waɗanda alaƙar auratayya ta hana (surukai).
3. Akwai
mata da alaƙar shayarwa ta hana (mariƙiya).
4. Akwai
mata da saɓanin
addini ya hana (mushirikai).
1.
Haramci a dalilin nasabar jini (haihuwa).
a. Kaka
(mahaifiyar uwa ko uba. b. Uwa. c. Inna (yar uwa, ƙanwar uwa).
d. Gwaggo
('yar uba, ƙanwar uba). e. 'Yar tsatso. f. Jikanya. g. 'Yar jika.
h. Yaya
da 'ya'yanta mata. i. Ƙanwa da 'ya'yanta mata.
2.
Haramci a dalilin auratayya.
a. Matan
uba (kishiyoyin uwa). b. Uwar mata (Suruka).
c. Ɗiyar mata (agola). d. Matar ɗa (suruka).
e. Ƙanwar ko 'yar mata (idan tana da rai) , ba a haɗa su a lokaci ɗaya.
3.
Haramci a dalilin shayarwa (raino).
a. Matar
da ta shayar da mutum nonon ta. b. 'Ya'yan ta.
4.
Haramci a dalilin saɓanin Addini (waɗanda ba musulmi ba, ba kiristoci ba, ba Yahudawa ba).
a.
Maguzawa. b. Riddaddu (waɗanda suka yi ridda). c. Matsafa.
HARAMCIN ƘAURACEWA MIJI A SHIMFIƊA.
Shari'ar Musulunci ta yi hani ko haramta mace ta ƙuracewa mijinta a shimfiɗa, watau lokacin kwanciya in ya buƙaceta,
ma'ana ya kirata saboda haka zata shiga fushin Allah, mala'iku zasu yi ta tsine
mata har sai gari ya waye.
وعن أبى هريرة رضى الله عنه قال: قال رسول الله
صلى الله عليه وسلم: إذا دعا الرجل امرأته إلى فراشة فلم تأته فبتا غضبان عليها
العنتها الملائكة حتى تصبع. متفق عليه.
An
karɓo daga
Abu-Hurairah (R. A) , yace Manzon Allah (S. A. W) yace: Idan miji ya kira matar
sa zuwa shimfiɗarsa, watau ya nufi ya kwanta da ita amma ta ƙi, ma'ana ta ƙi yarda da shi, har shi
mijin ya yi fushi da ita, Mala'iku zasu yi ta tsine ma ta har zuwa asuba.
Bukhari da Muslim suka ruwaito.
JIRWAYEN
AURE A ADABIN BAKA:
Tabbas an
samu jirwayen jigon a adabin bakan Bahaushe, musamman a rassansa guda biyar.
Kamar Karin Magana, da take da kirari, da tatsuniya, da almara, da maganganun
azanci da sauransu. Wannan ya ƙara nuna matsayin aure a
al’adar Bahaushe.
KARIN
MAGANGANU: Game da karin maganganu a kan aure da al’adar
Bahaushe ta
yi, suna da yawa, kamar haka:
1. Idan da
rai saurayi ma ango.
2. Da kamar
wuya tsohuwa da nesa.
3. Yakamata
auren na gida.
4. Amarya ba
kya laifi ko ta kashe ɗanmasu gida.
5. Ango hana
gaɗa.
6. Ango baka
ji asalatu.
7. Allah ya
yi aure da mara wuri (kuɗi).
8. Biki na
farar kaza belbela ba gayya ba.
9. Biki wan
shagali.
10. Biki-biki
da zani kowa ya raina ka ba nashi ba ne.
KIRARIN
AURE: Game da kirarin aure da al’adar Bahaushe ta yi, suna da
yawa, kamar haka:
1. Aure jibadau kayan nauyi.
2. Auren fari na
dakushe haukar balaga duk wanda aka yi wa zai yi hankali.
3. Auren
fari dabaibayi ga tuzuru.
4. Aure
yaƙin ‘yanmata.
5. Na
guga marmari daga nesa.
6.
Aure kafi ƙarfin yaro.
IRE-IREN
AURE.
Aure
dai kalma ɗaya ce manufa ɗaya, sai dai kuma yana da rabe-rabe kamar kashi goma sha biyu. Duk
da rabe-raben zaka samu ƙudurin su ɗaya ne, ko da za a samu
bambanci, sai dai ɗan abin da ba a rasa ba. Don kuwa zaka sami mata da miji
suna ƙaunar juna da girmama juna ko da haihuwa ko babu. Muna da
aurarraki kamar haka: -
1. Auren Kuɗi. (wanda aka biya sadaki,
da sauran ɗawainiya. )
2. Auren
Sadaka. ( wanda aka sadaukar da sadakin)
3. Auren
Zumunci. (aure na ‘yan uwa, dangin uwa ko na uba. )
4. Auren
Dole/Ƙi. (an yi bisa tilas, ko ango, ko amaryar wani bai so. )
5. Auren ɗauki sandar ka/takalmi. (a
auri mace tana gidanta daban )
6. Auren
Jeka da kwarinka. (a auri mace tana wani gari daban. )
7. Auren Jari. (a auri mace saboda kuɗinta ko na iyayanta. )
8. Auren Ɗaukar buta. (auren tsoho da tsohuwa,don ta zuba mai ruwa).
9. Auren Ɓoyon wata. (auren da akan yi kafin azumi, in ya wuce a fita).
10. Auren
kashe wuta. (auren da akan yi don a koma gun tsohon miji).
11. Auren
huce takaici. ( auren da akan yi don a share hawaye)
12. Auren
kangara. (auren da masu arziki kan yi, a tayar baikon wasu).
TATSUNIYA: Akwai tatsuniyoyi da dama da aka samu jirwayen jigon aure aa
cikinsu. misali:
1.
Tatsuniyar Barewa ta auri mutum.
2.
Tatsuniyar auren gaurakiya da biri.
3.
Tatsuniyar shaida kurciya.
4.
Tatsuniyar kaza ta mazuru.
5.
Tatsuniyar Gizo da ƙoƙi.
KAMMALAWA;
A ƙarshe wannan muƙala ta ɗan taɓo, wani abu da ya shafi
rayuwar aure da matsayinsa. Haka nan an nazarci matsayin aure da muhimmancinsa
ga dukkan wani abu mai rai. Tun daga mutum har dabbobi, da tsuntsaye, ƙwari, da tsirrai. An kuma fito da dalilai da suka sanya Bahaushe
ya bai wa aure babban matsayi. An bayyana yadda Bahaushe ke kallon duk namijin
da ya riƙa (balaga) , ma’ana ya isa aure amma bai yi ba, a matsayin mai
rauni kuma ba cikakken mutum ba. Bugu da ƙari kuma,
an kawo yadda Bahaushe ya karkasa mutane marasa aure zuwa gida uku ko huɗu. Kowane daga cikinsu
akwai irin matsayinsa a al’adar Bahaushe, tare da dalilai da suka sa aka bashi
sunan. Haka kuma, an kawo falalar dake tare da aure, sannan ga jirwayen adabin
bakan Bahaushe da sauransu.
Domin
haka,ina fatan wannan muƙala, ta zama kamar
matashiya ce ga masu hankali daga cikinmu maza da mata. Allah Ya sa mu dace
amin. Assalamu alaikum.
MANAZARTA
A
SuyuɗI ( )
Jami’ul Hadisi
Bargery
G. F. (1993) A Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary Ahmadu
Bello University Zaria
Yaro Y.
I. (1971) Tatsunniyoyi da Wasanni. Oxford University Press, Ibadan.
S. Aliyu
(2001) Addu’a’u min kibabi was’sunnah
Maktabatu
Anwaru Abdullahi, Kurmi Market, Kano.
Abdullahi
Fodiyo ( ) Sabiblil Najati. Jafaru Bin Alhaji, Hussaini Alkamawa Sakkwato.
Zaid A. A
( ) Risala Fssarar Hausa. Kurmi Market, Kano.
Gumi A M.
(1980) Al-ƙur’ani mai girma,Tarajamar Hausa.
Hadimil
haramaini, Sharifaini Makkah.
Malik I.
(1970) Muwaɗɗa Malik.
Darul fikri, Beirut Lebanon.
Annawawi
I. ( ) Riyadus salihin. Darul fikri, Beirut Lebanon.
Ladan Y.
(1980) Zaman Duniya Iyawa ne. Northern Nigerian Publication Company, Zaria.
East R.
(1966) Ikon Allah (Dabbobi). Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Imam Z. ( ) Kitabul
Kaba’ir, Darul fikri, Beirut Lebanon.
[1] Bargery G.P. (1934) A Hausa-English Dictionary. And
English-Hausa Vocabulary.pg498.
[2] Bargery G.P. (1934) A Hausa-English Dictionary. And
English-Hausa Vocabulary.pg1189.
[3] Bargery G.P. (1934) A Hausa-English Dictionary. And
English-Hausa Vocabulary.pg813.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.