DAGA
MU’AZU
SA’ADU MUHAMMAD Ph. D.
Phone:
07030803404 Email muazusaadukudan299@gmail. com
SASHIN
HARSUNA NIJERIYA
JAMI’AR
SULE LAMIƊO, KAFIN HAUSA
Tsakure
Wannan
nazari ya dubi dare da matsayinsa, da gudummowarsa, da tasirinsa a rayuwar
Bahaushe. Darene lokacin gudanar da kusan dukkan harkoki na al’adun gargajiya
wanda Bahaushe ya gada tun iyaye da kakanni. Manufar wannan bincike shi ne zaƙulo ko kawo bayanai tare da fito da rawar dadare yake takawa a
yanayin zamantakewar Bahaushe. Da farko za a kawo ma’anar dare tare da fagagen
da dare ya kankane, dalilai, da tsawon lokacin da yakan ɗauka. Hanyoyin tattara
bayanai sun haɗa d a adabin Bahaushe na baka da rubutacce, da hira jama’a.
Na ɗora aikin a kan ra’in zahirancin A’adun Al’ummma. Sakamakon
nazarin ya fito da irin yadda zamantakewar Bahaushe ta bai wa dare muhimmanci
kusan kamar na abinci, kamar a wajen bikin aure, da haihuwa, da sana’a, da
magani, da sauransu. Haka kuma za a kalli irin yadda Hausawa kan yi kasuwancin
dare a tsakaninsu a wasu wuraren. Maƙalar zata
kawo jirwayen dare a adabin Bahaushe na baka da rubutacce wato na zamani,
daga ƙarshe sai kammalawa da manazarta.
1.0. Gabatarwa.
Al’ummar
Hausawa sun taɓa kasancewa a wata irin rayuwa ta maguzanci, wato rayuwar da babu
wani addini saukakke daga wurin Allahu (S. W. T) da Ya aiko wani Manzo don ya
kawo wa bayin Sa. Gaba ɗaya rayuwar maguzanci, ta dogara ne ga tsare-tsare ko dokokin
gargajiya, watau dai Hausawa sun kasance suna bin addinin gargajiya watau
maguzanci, don haka ake kiran mabiyansa maguzawa. Wannan rayuwa ta gudana a
zamani mai tsawo kafin zuwan Addinin Musulunci. Muhammad()
Hausawa
sun karɓi Addinin
Musulunci tun a ƙarni na goma ko na
sha ɗaya 10thor
11thCentury, kamar yadda masana tarihi suka bayyana. Akwai masu cewa
addinin Musulunci ya shigo ne daga daular Borno, wasu kuma suka ce daga daular
Mali. Wangarawa suka kawo, wasu suka ce masu fatauci, fatake masu
cinikin ƙetare Hamada, da dai sauran bayanai damasana tarihi suka yi
daban-daban. ()
Al’ada na nufin wata hanya ce, wadda wasu al’umma suka ɗaukar wa kansu da suke
gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum. Wadda suka yarda da ita kuma suka yi
imani da ita. ()Al’ada ta ƙunshi duk wata harka ta
rayuwa, tun daga addini, da shugabanci, da abinci, da makwanci wato muhalli, da
bukukuwa, da tufafi, da magunguna da sauransu().
1. 1Manufar wannan bincike: shi ne, tattaro ko kawo
bayanai a kan matsayin dare, da gudummowarsa, da tasirinsa a rayuwar Bahaushe.
Takada ta kawo ma’anar dare, da fagagen da dare ya mamaye, tare da gano irin
shaƙuwar da Bahaushe ya yi da dare ta yadda har bai iya gudanar da
wasu abubuwa na rayuwarsa sai da dare.
Bugu
da ƙari wannan nazari ya ƙara fito da muhimmancin
dare a tunanin Bahaushe. Bayan wannan kuma, nazarin ya ƙara nuna muhmmancin dare a fagen magani da na tattalin arziki a
rayuwar Bahaushe. Hanyoyin da na tattara bayanai sun haɗa d a adabin Bahaushe na
baka da rubutacce, da hira jama’a. Na ɗora aikin a kan ra’in zahirancin A’adun Al’ummma. Sakamakon
nazarin ya fito da irin yadda zamantakewar Bahaushe ta bai wa dare muhimmanci
kusan kamar na abinci, kamar a wajen bikin aure, da haihuwa, da sana’a, da
magani, da sauransu. An kuma ƙara fito da tsoro, da irin
girmamawar da ake yiwa dare a Bahaushiyar al’ada. A ƙarshe sai kammalawa da manazarta.
1. 1.
Ma’anar Dare:
Dangane
da ma’anar dare kusan baki ya zo ɗaya sai ɗan abin daba a rasa ba, saboda Masana da dama sun bayar da ma’anar
dare a matsayin; CNHN(2006: 98). wani lokaci ne mai duhu da yake biyowa bayan
faɗuwar
rana. Shi kuma Abubakar (2015: shf: 98),ya kawo cewa dare lokacin duhu ne a
tsawon rana daga faɗuwar rana zuwa goshin asuba. Bargery (2015) ya bayyana dare a
matsayin abin da ya fara daga faɗuwar rana da shigar duhu har zuwahudowar alfijir na safiya.
Bisa
la’akari da bayanan masana magabata, ana iya cewa dare wani lokaci ne wanda
yakan zo bayan rana ta faɗi. Kuma, a lokacin ne duhu kan fara. A lokacin dare ne, wata kan
yi haske kuma taurari kan haska sama.
Haƙiƙa lokacin dare wani lokaci ne babba kuma mai muhimmanci ga rayuwar
Bahaushe. Dalilin da yasa haka kuma shi ne, kusan duk wani abu da Bahaushe zai
gudanar, sai an samu tasirin dare a ciki. Wannan kuwa ya haɗa ne tun daga bautarsa tun
kafin zuwan musulunci wato tun a lokacin maguzanci. Bahaushe yakan gudanar da
wasu hidimomi da suka shafi abubuwan bauta kamar camfe-camfen Bahaushe. Bayan
haka an samu jirwayensa a maganganun azanci, kamar karin maganganu da waƙoƙin baka da na rubutattu().
Bugu
da ƙari, ana iya ganin tasirin dare a rayuwar Bahaushe tun daga
bukukuwansa, da sana’o’insa, da maganganunsa. Haka kuma Bahaushe yakan yi
amfani da dare wajen aiwatar da wasu ayyuka marasa kyau, kamar na ɓarna, don haka ne ma yakan
ce “Dare rigar mugu”(). Da yawa an fi samun aukuwar laifuffuka da dare,
misali, ɓarayi sun fi yin sata da dare kamar inda Alhaji Mamman Shata
Katsina kan ce:
Jagora:
Iyalan Mamman,
waɗandaba su son a yi haske,
sun fi
son a zabga duhu,
da ruwa
yaf-yaf.
Amshi:
Haka nan ne,
Ƙanin Idi wan Yelwa.
2. 0
Hanyoyin Gudanar Da Bincike
Hanyoyin
tattara bayanai sun haɗa da adabin Bahaushe na baka da rubutacce, da hira jama’a. A
dalilin haka ya sa a kan ce fatakan dare. A bisa dalilin baiwa dare muhimmanci
da Bahaushe ya yi, shi ya sa har dabbobi, da tsuntsaye da ƙwari, sai da ya yi nazarinsu kuma ya ware waɗanda suka fi yin harkokinsu
da dare shi ne sai ya kirasu da mabi-dare. Alhaji Mamman Shata Katsina a waƙar Umaru Ɗanɗanduna Na Gwandu yace:
Kura mabi
dare,
Umarun
gidan Ɗanduna
Umaru Ɗanɗanduna Na Gwandu.
Shi kuwa
Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun a waƙarsa ta Ɗanmaliki Umaru Sadauki yana cewa:
Kura mai
yawon tsakad dare
Tayo
yaucin babu nama
hankalinta
duk yaɓaci,
ta koma
gida tanabaƙin rai.
Ɗanmaliki Umaru Sadauki
Kana da
wuyar karo na Malam.
3. 0
Ra’in Bincike
Na ɗora wannan aikinbincike a
kan ra’in zahirancin A’adun Al’ummma.
4. 0.
Matsayin Dare da Tasirnsa ga Al’ummar Hausawa
Dare a
mahangar al’ada, ana iya cewa wani lokaci ne mai mahimmanci matuƙa. Wannan yasa gaba ɗaya al’adar Bahaushe ta girmamashi ta hanyar gudanar da wasu
harkoki da dare, sannan kuma ta ƙyamaci yin wasu da dare. A
mafi yawan lokuta, hatta yin mu’amala dake bukatar sirri, an fi yi da dare. Duk
da haka kuma, al’adar Bahaushe ta camfa dare, shi yasa wasu ayyuka ba a son yi
da dare, ko kuma wurare baa son zuwa da dare saboda gudun kar zuwan ya haifar
da mummunan sakamako. Bisa dalilin cewa dare rigar mugu ce, Bahausheya yi
imanin cewa akan iya gamuwa da mugayen mutane, ko iskoki, ko dabbobi, da ƙwari da sauransu a lokacin dare. Haka kuma an camfa yawon dare don
gudun kar a gamu dafatalwa().
Bisa al’adar Bahaushe, akan
fifita dare ta fuskar bauta, wannan kuma ya haɗa da addinin gargajiya har da na musulunci. Ana iya ganin hujjar
haka a cikin Littafin Habibu A. Sarki (2000) zuwan musulunci Afrika da
shigowarsa Ƙasar Hausa. da ya bayyana cewa: a lokacin mulkin Barbushe a
farfajiyar dutsen Dala ta Kano. Kamar haka:
“Daga cikin ire-iren bautar waɗannan maguzawa da akwai
bikin cikar shekara. Dukkansu sukan taru a kan dutsen dala, su kewaye bukkar
tsunburbura su tuɓe tsirara su kwana bauta. Su yanyanka baƙaƙen karnuka da bunsura. Daga
nan sai Barbushe ya yi wa tsurburbura kirari ya ce: “jamuna a kasa mun gama
(karagaya laya tsunburbura). Sauran maguzawa su amsa masa da cewa:
“ga tsunburbura Kanawa ga Magajin Dala”. [1]
Kamar a
addinin musulunci ana keɓe lokutan dare musamman ga tsayuwar dare(ƙiyamul laili), da wurudi da sauran ibadu. Akwai wata Karin Magana
mai cewa ba faɗa da malami ke tsoro ba tsakad dare ke tsoro, wato ana tsoron kar
malam ya tashi da dare ya zauna kan buzu ya ya yi masa addu’a.
Bahaushe
ya ɗauki dare
a matsayin wani lokaci ne na yaƙartalauci ko na neman
arziki, da neman suna ko ɗaukaka. Domin tun a zamanin maguzanci akan yi wankan mararraba don
a yi kuɗi, haka
kuma da Bahaushe ya karɓi addinin musulunci sai aka samu addu’o’i na neman arziki, kamar
karanta suratul waƙi’a tana korar talauci. Ban da wannan kuma akwai wurudin rauhanai
wanda malaman tsubbu ke aiwatar wa har akan ce: wane ya dace. Kuma akan ce
Yaro ɓata
hankalin dare kayi suna(ɗaukaka).
Ban da
wannan, samari da ‘yammata kan yi zancen samartaka a tsakaninsu shi ma da dare,
mafi yawa an fi zuwa gidan su budurwa, amma akan haɗu a dandali shi ma da dare.
4. 2.
DareA Matsayin Sutura:
Bahaushe
ya ɗauki dare
a matsayin wata sutura ce da take lulluɓe sirrin mutum. A mafi yawan lokuta wasu abubuwa na sirri an fi
yinsu da dare. Bahaushe ya fi samun natsuwa da dare,saboda duhun da kuma ƙarancin idanu jama’a domin har a kan ce a bari sai sawu ya ɗauke can talatainin dare
sannan a yi abu kaza. Bisa dalilin kunya Bahaushe ya keɓe dare wajen kwanciya da
iyali, wannan kan ba shi damar sakewa saboda yara sun yi barci, kuma maƙwabta sun yi barci. Bisa wannan dalili ne yasa al’adar Bahaushe ta
yi hani idan an ji mata da miji na faɗa da dare to ba a zuwa rabo().
Bahaushe
kan yi amfani da lokacin dare don yin wasu tarurruka na tattaunawa a tsakanin
manyan mutane. Alal misalineman aure, a wajen neman akan kai sallama ko neman
izini, da kai sadaki duk da dare. Haka ma sulhu a tsakanin ma’aurata kamar biko
idan mace ta yi yaji. Bugu da ƙari hatta yin sulhu a
tsakanin mutane abokai ko maƙwabta mafi yawa an fi yinsa
da dare.
Baya ga
wannan kuma, a yanzu a wannan zamani ‘yan siyasa sun fi amfani da lokacin dare
wajen tarurrukansu. Haka kuma, hatta jami’an tsaro sun fi yin amfani da dare
wajen kama masu laifi. A kan yi bincike da sauran tsare-tsare na gano masu
laifi da rana, amma an fi kai samame da dare don kamasu.
4. 3.
Dare A Matsayin abin Tsoro
Ma’anar
Tsoro
Babu
shakka Bahaushe na tsoron dare ko yin wasu harkokinsa da dare. Wannan kuwa ba
ya rasa alaƙa da yanayin duhu da kuma kasancewar dare rigar mugu. Tun daga
mutane da iskoki (Aljannu) da dabbobi, da tsuntsaye da ƙwari duk sun fi cutarwa da dare, saboda fakewa da duhu.
Bayan
haka, Bahaushe ya yi wasu dabaru na rage ko sauƙaƙa duhu da dare ke ƙunshe da shi ta
hanyar ƙirƙirar fitilar alaƙa, zuwa aci balbal, har
kuma Bature da ci-gaban zamani ya kawo masa fitilar ƙwai, da cocila, da lantarki don samar da haske. Tabbas haske da
dare yana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da sauran harkoki da suka rage
daga harkokin rana.
Ba wai
amfani da fitila kamar wani labarin makaho mai fitila………Littafin Ƙaramin sani. Ba mutum ba hatta dabbobi kan bai wa haske wani irin
kulawa wannan yasa maharba kan yi amfani da fitilar goshi.
Bugu
da ƙari, Bahaushe na tsoron dare shi yasa ya ƙyamaci fitar dare don yin fitsari ko kasha. Bisa wannan dalili ne
yasa Bahaushe ya ƙirƙiri kaskon fitsari, saboda taƙaita fitar dare. Wannan
dalili ne ya haifar da wata karinmagana mai cewa. “In ka ji rakani kasha ba
zawo ba ne”. Ko “Ƙanƙanta kamar kashin tsoro”. “Babu gara ga kashi, da na dare da na
rana duk wari garesu”. ()
4. 4.
Tasirin Dare a Wasu Sana’o’in Bahaushe
Ma’anar
Sana’a
Akwai
wasu sana’o’in Bahaushe da dama waɗanda an fi yinsu da dare. Akwai sana’ar kaɗin zare da matan Hausawa ke
yi, a zamanin da, mafi yawa an fi yin wannan sana’a da dare. Haka kuma, akwai
sana’ar saƙa da mata kan yi a ɗakinsu sun fi yi da dare. Sana’ar yin daddawa an fi yin dahuwar
kalwa da dare ta kwana a kan wuta. Tsofaffin mata Hausawa sun fi yin harkokinsu
da dare, kamar ɓarar gyaɗa wanda har sukan gayyaci ƙananan
yara su tayasu ɓarar gyaɗar a inda su kuma suna yi masu tatsuniya. Haka kuma da dare ne
suke sanya yara su taya su gyaran auduga, kamar cire angurya daga auduga().
Bugu
da ƙari, Bahaushe kan yi amfani da dare wajen rage wasu ayyukan da
suka shafi sana’o’insa. Kamar sana’ar ɗinki akwai waɗanda kan yi da dare ko kuma su rage aikin da zasu yi gobe. Haka
kuma Bahaushe kan yi sana’ar gadi da dare, sannan masunta ko kwarawa kan tafi
kogi su kwana a can don kamun kifi. Bayan wannan kuma sai maharba ko mafarauta
masu zuwa daji da bindigar baushe ko kwari da baka da dare. Akwai kuma masu
sana’ar ɗibar zuma, su ma waɗannan sun fi zuwa da dare. Kamar yadda wani marubucin waƙoƙin Hausa Alhaji Auwalu Isah Bungudu a waƙarsa ta Mulkin Satsi Yaudara ne, yace:
“Raggo ba
zai sha zuma ba,
Baya cin
naman maharba,
Don ya
kashe ba zai iya ba,
Inda ba
sammai a kai ba.
Mulkin
Satsi Yaudara ne,
Ba
cika alƙawari suke ba.
4. 5
Tasirin Dare A Wasannin Yaran Bahaushe
Bisa
nazari da aka yi, wanda ya nuna a sarari yadda dare yayi tasiri a rayuwar
Bahaushe. Wannan bai bar yaran Hausawa ba, don kuwa ko a wasanni da yara kan
gudanar mafi yawa da dare bayan sunci abincin dare, wato jibi. Sukan fito
wasannin motsa jiki da dare a dandali musamman lokacin farin wata. Bayan wannan
kuma yaran kan shirya wasan tashe da dare a watan azumi.
Bugu
da ƙari, Bahaushe ya shirya tare da tsara tatsuniya don yaransa,
sannan kuma ba a yenta sai da dare. In kuma har ya zama dole sai an yi
tatsuniya da rana to dole sai an ɗaure gizo don kar wanda ya yi tatsuniya da rana ya yi makuwa.
Wasan
Yara Maza Wasan Yara Mata (Gaɗa)
4. 6.
Tasirin Dare A Magungunan Bahaushe
A mafi
yawan lokuta, Bahaushe kan yi amfani da dare wajen aiwatar da maganinsa. A wani
lokaci wajen ɗebowa, ko haɗawa, ko dafawa, ko amfani da maganin. Idan muka dubi masu
magungunan Bahaushe, tun daga ‘yanbori, da magori, da ‘yarmaiganye, da sarkin
mayu, da malaman tsibbu, da bokaye, kai tsaye ana iya cewa kowanne daga cikinsu
ya bai wa dare muhimmanci, saboda babu wandaba ya bayar da magani kuma yace
wani sai da dare za a yi amfani da shi ta hanyar sha, ko ci, ko ayi turare da
garwashin wuta ko ayi wanka da ruwan maganin.
Wannan
kuma ya shafi magani na neman waraka da na riga-kafi, da na cutarwa har da na
neman suna ko ɗaukaka.
4. 7.
Tasirin Dare A Tsafe-Tsafen Bahaushe
A
mafi yawan lokuta tsafe-tsafen da Bahaushe ya rinƙa yi
kafin zuwan addinin musulunci da kuma bayan zuwan musulunci, an fi gudanar da
shi da dare ne. Bautar tsumburbura a dala, da madara a madarkaci, da magiro a
kwatarkwashi da mafi yawan hatsabibanci da ake yi an fi yi da dare. Ko daga
baya da ake sauya wa gyambo ƙafa Bokaye da malaman
tsubbu da mayu duk an fi yi da dare. Rawar maita, da harbin kasko, da wankan
mararraba, duk da dare aka fi aiwatar da su. Duk wani samun da za a yi don a
bunne shi ko juji ko suri ko marabar hanya ko kabari ko maƙabarta da dare ake yi.
Dare
Rigar Mugu
Bahaushe
na amfani da Karin Magana ne a bisa dalilin cewa: A mafi yawan mugu ciki an fi
aikatashi da dare ne. Kamar sata, fyaɗe, kwartanci, shige, maita, sammu, da sauransu.
Sata:
Kusan nau’o’in sata da ake da su da ta shiga ɗaki, da ta tare hanya da
fizge, an fi yi aikatasu da dare.
Alhaji
Mamman Shata Katsina a waƙar ɗiyar Bayye yana cewa:
Jagora:
Iyalin Mamman,
waɗandaba su son ayi haske,
sun fi
son a zabga duhu da ruwa ya-yaf.
Amshi:
Haka nan ne Mamman ,
Ƙanin Idi wan Yalwa.
Alhaji
Musa ƊanƙwairoMaradun a waƙar Sarki Muri yana cewa:
Jagora: In
dare ya yi har kun shige barci,
indai
kunji karnai suna haushi,
In
ba kura ta wuce nan ba,
to wata
baƙin ɓarayi ne.
Amshi:
Zaki ba ja ka gaba ba,
Sarki
Muri Uban Galadima
MakaɗaKasu Zurmi a waƙar Ɓarawo masifa in dare ya yi
yana cewa:
Jagora: Ɓarawo bala’i ne in dare ya yi,
Ajiya ɗaka ba ajiya ba,
Ka
iske mai abu na ja,
Mara
abu na ja,
Kai mai
abu sau mai.
Dabbobi
Mabiya Dare
Bisa
lura da kiyayewa da Bahaushe ya yi dangane da halaye da ɗabi’un wasu dabbobin daji.
An ware wasu dabbobi na daji musamman maciya nama wato mafi fiƙa da dagi, kamar zaki, da damisa, da siyaki, da kura, da kyarkeci,
da dila da sauransu. Dangane da dabbobin gida sun haɗa da kare, da mage. Game da
wannan batu ana iya kawo wata waƙa da Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun waƙar Ɗanmaliki Umaru Sadaukiya ce:
Jagora:
Kura mai yawon tsakaddare,
ta yo
yawonta babu nama.
Amshi: Ɗan maliki Umaru Sadauki
Kan
wuyar karo na malam.
Alhaji
Musa Ɗanƙwairo Maradun a waƙar Sarkin Muri ya ce:
Jagora:
In dare yayi duk shige barci,
in dai
kun ji karnai suna haushi,
in ba
kura tab biya nan ba,
to wataƙila bakin ɓarayi ne”.
Amshi:
Zaki ba ja ka gaba ba,
Sarki
Muri Uban Galadima.
Alhaji
Mamman Shata Katsina a wata waƙarsata Umaru Ɗanɗanduna na Gwandu matuƙin mota sai ya ce,
Jagora:
Kura ma bi dare ,
ummar
gidan ɗanduna.
Amshi:
Umaru Ɗanɗanduna na Gwandu.
Bayan
dabbobi kuma Bahaushe ya keɓe wasu tsuntsaye kamar mujiya, da jemage, da mikiya, da yaburbura,
da birbiri.
Dangane
da ƙwari su ma akwai waɗanda suka fi yin harkokinsu da dare kamar kunama, buzuzu tsanyar
biri, rozozo, kyankyaso da sauransu.
Bugu
da ƙari, dabbobi irin su ɓera, da gafiya, da kwaɗo, da jaɓa, da maciji, da bushiya, da tsaka. Dukkan waɗannan jeri sun fi yin
mu’amallarsu da dare. Ko da yake Bahaushe ya rarraba su bisa halayensu. Da
farko akwai mugaye waɗanda da an gansu sai kisa. Kamar maciji da jaɓa da tsaka, bisa dalilin
cewa suna cutarwa. Bayan su sai kuma gafiya da ɓera, bushiya su laifinsu
shi ne ɓarna da
sata. Duk da yake Bahaushe nakashe su a wani lokaci in an dace a kan yanka
gafiya da bushiya don a ci namansu. Shi kuwa ɓera ba a cika cin namansa
ba sai dai ɓeran daji. Baya ga dabbobi mabiya dare, Bahaushe ya keɓe wasu tsuntsaye masu
harkarsu da dare. Tsuntsaye irin su, mikiya, da yaburbura, da birbiri da
jemage, ko da yake ana lissafa jemage a jerin dabbobi masu tashi.
4. 0 Dare
Mahutar Bawa
Babu
shakka Bahaushe ya ɗauki dare a matsayin wani keɓaɓɓen lokacin da yakan huta bayan gudanar da harkokin rana. Wannan
kuwa ya bayyana ne tun daga lokacin da bahaushe kan cin abincin dare wato jibi.
Al’adar ciyayya wacce magidanta kan yi a ƙofar
gidansu, kowanne magidanci zai fito da abinci a taru a ci tare. Bayan ciyayya,
sai kuma lokacin hira, da zarar an kammala cin abincin dare sai kuma a kafa
dandalin hira ko majalisar hira. A irin wannan hira ce kowa kan faɗi irin gwagwarmayar da ya
sha a wannan wuni. Bayan hira kuma sai tafiya unguwa da matan Hausawa kan yi a
inda sukan ziyarci ‘yan uwa da dangi, saboda gaisawa, ko jaje, ko barker
haihuwa, da sauransu.
Bayan
wannan kuma sai zuwa kwanciya barci, kwanciya barci kusan ana iya cewa shi ne
aiki na ƙarshe da Bahaushe kan yi da dare.
5. 1.
2Jirwayen Dare A Camfin Hausawa
An camfa
fitar dare.
An hana
zuwa juji da dare.
An hana
ratsa kasuwa da dare.
An camfa
kukan mujiya da dare.
An camfa
jifan baƙin kare da dare.
Baƙin Kare: Bahaushe
ya camfa, kuma bai cika yarda da baƙin kare, sabo da alaƙarsa da iskoki. A wasu lokuta iska kan rikiɗa zuwa baƙin kare, ko kuma su shiga jikin baƙin kare
na haƙiƙa. Don haka ne ba a duka ko jifansa. Wannan ya wuce hasashe ko
zargi, saboda waɗansu hujjoji da suka tabbata a wurare, da lokutta da kuma mutane
daban-daban. Misali.
Labarin
wani mutum da baƙin kare
“Na dawo yawo da dare na shiga wani lungu sai na ga baƙin kare sai na ɗauki dutse na jefe shi, sai ya gudu ba a ɗauki wani lokaci ba, sai
naga wani mutum ya bayyanar min. Nan take sai yace kai yaro kar ka ƙara jifan kare ka ji. ” [2]
6. 0
Jirwayen Dare A Mahangar Addinin Musulunci
Idan
muka kalli dare, ana iya cewa lokaci ne da yake da daraja a musulunci. Dalili
kuwa shi ne, ana kwaɗaitar da musulmi da yawaita ibada da dare musamman sallar dare da
ake cewa Ƙiyamul laili. Ban da wannan kuma an kwaɗaitar da cewa ana karɓar addu’a da dare.
Haka
kuma, muhimmancin dare ya ƙara bayyana ta inda aka
ambaci dare a cikin Alƙur’ani a wurare da yawa a
surori da dama. Akwai wasu surori inda Allah ya yi rantsuwa da dare.
Bugu
da ƙari, Allah yace, “mun sanya dare ya zama hutu a gareku”.
Akwai
inda aka nuna a nemi tsari da dare lokacin da ya yi duhu. suratul Falaƙ
An nuna
cewa: Cikin dare aka hallakar da mutanen Annabi Luɗu.
An nuna
cewa: Cikin dare aka hallakar da Fir’auna da mutanensa.
An nuna
cewa: Cikin dare ne aka yi Isra’I da Mi’iraji.
An nuna
cewa: Cikin daren watan Ramalana ake samun lailatun ƙadari.
An nuna
cewa: Annabi yakan tafi maƙabartar baƙiya cikin dare.
An nuna
cewa: Ba a son a bar mutum a kasuwa ya zama na ƙarshen fita.
An nuna
cewa: Ana girmama darare goma na ƙarshen watan azumin
Ramalana.
5. 1.
Dare A Adabin Baka
Akwai
jirwayen dare a adabin Bahaushe, a rassan adabin baka da rubutacce. A karin
magana, da almara, da tatsuniya, da barkwanci, da waƙar baka.
5. 1. 1
Dare a Karin Maganganu:
1. Tsakad
dare maraicen kura.
2. Dare ga
mai rabo asalatu.
3. Da’u
fatakan dare, da rana kuke barci.
4. Dare
mahutar bawa.
5. Dare
rigar mugu.
6. In dare
yai dare buzuzu ma nama ne.
7. Sai dare
yai dare a sai da fatar kura, na ‘yan awaki ta kare.
8. Mai daren
tuwo kya ci da buzuzu.
9. Mujiya
wasa da ranaba naki ba ne.
10. Komai
nisan dare gari zai waye.
11. Allah yai
dare gari ya waye.
12. Dare mai
danne duniya
13. Ba faɗa da Malam ba, tsakad dare
ke tsoro.
14. Bari in
tashi ciwo ya ji dare.
15. Katankatana
mutuwar almuru.
16. Duk ɗaya makafi sun yi dare.
17. Ruwan
dare tada hankalin baƙo.
18. Dare mai
ban tsoro.
19. Ruwan
dare mai game duniya.
20. Mai gari
ba ya daren tuwo.
21. Yunwar
dare mai hana barci.
22. Rigima
kamar daren Sallah.
23. Wane dare
ne jemage bai gani ba?
24. Duk wanda
ya ce kasuwa gida ne, bari dare ya yi.
25. Ɗan tsakad dare jikar asuba.
26. Damuna
dare in kaka ta yi gari ya waye.
27. Yaro ɓata hankalin dare ka yi
suna.
28. Dare ɗaya Allah kan yi Bature.
29. Arziƙi kashi ne, da dare kan taka shi.
30. Dare maƙura yawo.
5. 1. 4.
Dare A Tatsuniya
Tatsuniyar Ɗan auta da Dodo:
A tsakar
dare ne dodo ya shigo gari sai ya ji warin mutum, tun daga nesa ya fara waƙa shi Ɗan auta yana bas hi amsa
kamar haka:
Wa ya yi
ni,
ni Dodon
nana,
wa ya yi
ni.
Na
yi yake,
Ɗan auta iya
ya yi ya
kai har fika.
Tatsuniyar
Ta-kitse:
Da dare
gizo ya zo bara gidan tsohuwa ya ga bijiminsa, ya dawo ya ga ‘yan mata.
Tatsuniyar Ta-kitse.
Bayan Sarki ya hana a sanya Ta-kitse aiki, sai wata rana ya tafi
yaƙi. Kishiyoyinta kawai sai suka ceta fito ta yi. Fitowar ta ke da
wuya, saboda zafin rana, da zafin wutar girki, sai ta fara narkewa. Nan da nan
gida ya fara ruɗewa, kowa na kawo shawara ta yadda za a faɗawa Sarki. Ana cikin haka,
sai kurciya ta zo tace, zata iya faɗawa Sarki a bakin daga, aka yarda ta tafi, da isar ta sai tace:
Sarki Sarki a mai da yaƙi baya. Ta-kitse ta narketa
narketa zamagulbin tsakar gida. Sarki na jin wannan waƙa da kurciya ke yi, sai ya dakatar da yaƙi ya koma gida. [3]
Tatsuniyar
Gizo da Dodanniya.
Wata rana gizo ya tafi gidan dodanniya ya karɓo bashin bajimin sa, da alƙawarin zai biya shekara mai zuwa. Ya zo ya cinye, ya hana kowa. Ko
da shekara ta zagayo, sai dodanniya ta zo bin bashi gidan gizo. Bayan dodanniya
ta iso gidan sai ƙoƙi tace gizo ya mutu. Har ta kama hanya zata koma, sai kurciya
tace ƙarya ne. Daga nan sai suka koma gidan gizo, ta fara waƙa tana cewa: [4]
Kurciya:
Mabiyan bashin gizo sun iso,
Mabiyan
bashin gizo sun iso,
Zai
yi biyan bashi a kushewa,
Gizo:
Un uhun wai ya kurciya,
Ki
biyo ta gidan mu ki sha ruwa,
Ruwanki
na nan a kururrumi,
Bari
in fita in taɓa ‘yar rawa,
Bari in
fita in taɓa ‘yar rawa.
Daga nan
sai gizo ya fito dodonniya ta kama shi ta tafi da shi gidanta.
Ø Tatsuniyar Ruwan Bagaja.
Ø Tatsuniyar Ɗanƙashin guiwa da namun daji.
Ø Tatsuniyar Gizo da hankaki.
Ø Tatsuniyar Gizo da Dodanniya.
Ø Tatsuniyar Gizo da ‘yan ruwa.
Ø Tatsuniyar Gizo da kura.
5. 1. 3
Dare A Waƙoƙin Baka
Waƙar Bikon Aure:
Dare,
dare baba,
dare da
rana abin kallo.
A wata waƙa wadda Uwaliya Mai Amada ta yi inda take cewa:
Jagora:
Dare Allah magani.
Annabin
Allah na magani,
Dare
Allah magani.
Zan taɓa maku waƙar kishiya,
Amshi:
Dare Allah magani.
Mamman
Duka mai goge a wata waƙa yace:
Jagora:
Sai dare ya yi dare
Sai dare
ya yi dare
a sai da
fatar kura,
Sannan ta
bunsuru,
Ta ƙare kwata-kwata.
Alhaji
Mamman Shata Katsina a waƙar Umaru Ɗanɗanduna Na Gwandu yake cewa:
Jagora:
Kura mabi dare,
Umarun
gidan Ɗanduna.
Amshi:
Umaru Ɗanɗanduna Na Gwandu.
5. 2Dare
A Rubutaccen Adabi
A
rubutacce adabi ma an samu jiwayen dare da dama, akwai littattafai kamar zube,
da wasan kwaikwayo, da rubutacciyar waƙa.
daga
Littattafan Zube.
Littafin
Ruwan Bagaja:
1. Malam ya
tunkuɗa Alhaji
Imam cikin ɗaki da ya zo kwartanci.
2. Ɓarayi sun damu Alhaji Imam
ya koma gidan sarkin gardi.
3. Alhaji
Imam ya kai cin hanci wurin Alƙali.
4. Saƙimu da dare ya kasha Liman / Uwar Alhaji Imam.
Littafin
Jiki magayi:
1. Abubakar
ya zo hira wurin Zainabu da dare.
2. Abubakar
ya shiga gidan Malam Shehu ya yanki gashin kan Kyauta don haɗa sammu, ya tafi ya bunne a
kabari da dare.
3. A garin
Zanna da Shirinka ana kwana ana yin garaya.
4. Abubakar
ya tafi neman ƙaron kalgo da dare.
Littafin
Magana Jari ce:
1. Jarabawar
Sarkin ɓarayi
Noman ta uku da dare aka yi mafi yawa.
2. Jarabawar
Yusha’u Narimi da dare aka yi.
3. Masu
satar Likkafani a kabari da dare.
4. Masu
satar rogo da dare.
5. Mansur da
dare ya ɗauki fansa ga Ɗanshedan.
6. Bawa
mai ƙusumbi da dare ya yi gamo.
7. Telu fari
da sarkin fawa da dare ya kama.
Littafin
Nagari Na kowa:
1. Ɗanduna ya gana da Mai dubu
da dare ya bar mashi amanar Salihi.
2. Salihi ya
rinƙa a toka ba da sauri Mai dubu ba.
3. Sarauniyar
Bori ta ba uwar gida turare da borkono.
4. Addu’ar
Mai dubu don dukiyarsa ta ɓace da dare.
5. Cikin
dare aka tura Salihi a rijiya.
6. Cikin
dare aka ba Salihi Sarauta.
Littafin
Shehu Umar:
1. Da dare
ne su makan suka kai harin kama bayi.
2. Da dare
ne kura ta cinye ɓarawon umar.
Littafin
Dare Dubu Biyu da Ɗaya:
1. Lokacin
dare aka ba da labari.
Littafin
Kitsen Rogo:
1. Lokacin
da aka sace madubin mota da dare ne.
2. Da dare
ne aka je wurin Malamin tsibbu.
Littafin
Da’u fatakan dare:
Da’u da
Sambo baƙin duhu.
Littafin
Iliya Ɗan mai ƙarfi:
Haɗuwar Iliya da Gogaji.
Littafin
Tauraruwar Hamada:
Malam Ɗanye da dare yake haɗa kayan tsibbu.
5. 2Dare
A Rubutattun Wasan Kwaikwayo
Littafin
Kulɓa
na Ɓarna:
1. Lokacin
da Alhaji Ruwan Ido yake zuwa da dare ya ɗauki Zaliha.
2. Ɗan London da dare yake zuwa
zance da Zaliha.
Littafin
Zaman Duniya Iyawa ne:
1. Tagudu da
dare ta faɗa da
mijinta wai bai dawo da wuri.
2. Tagudu
tai faɗa da wata
karuwa da dare.
Littafin
Tabarmar kunya:
1. Da dare
ne Idi ya je ya sato geron turunkuna ya faɗa ɗakin surukansa.
2. Cikin
dare ya gudu don kaucewa abin kunya.
Littafin
Uwar Gulma:
1. Hayatu
sai dare ya yi yake dawowa a buge kuma ya bugi Halima.
Hujja
daga Alhaji Sule Buttu, Mai Maganin Mayu Jihar Naija:
1. Ana gwada
tona asirin mayu ne da dare.
2. Ana cire
masu maita da dare.
Daga
Jakar Magori Rediyo Nigeria Kaduna:
1. Wata mata
mayya ta damu surukarta, matar ɗanta. Don ya bugeta da dare.
2. Wata
yarinya ta faɗa rijiya a garin Kudan 2003
3. Kwalekwale
ya kife a kogin Ɓagwai da mata da amarya da
dare.
8. 0
Kammalawa:
A ƙarshe wannan nazari ya hararo matsayin dare, da gudummowarsa, da
tasirinsa a rayuwar Bahaushe ta mahanga al’ada. Maƙalar ta kawo ma’anar dare, da bayyana fagagen da dare ya mamaye,
tare da gano irin shaƙuwar da Bahaushe ya yi da
dare ta yadda har bai iya gudanar da wasu al’amura na rayuwarsa sai da dare.
Babu
shakka wannan nazari ya ƙara fito da wasu abubuwa
game da muhimmancin dare ta inda ya shafi tunanin Bahaushe, kamar taimakawa
mawaƙa a fagen waƙa, mafi yawan mawaƙa sun fi gudanar da waƙoƙinsu da dare, sannan dangane da malamai a fagen ilmi. Domin dare
yana ƙara kaifafa tunani tare da aiwatar da ibada cikin sauƙi. Bayan wannan kuma, nazarin ya ƙara nuna muhmmancin dare a fagen magani da na tattalin arziki a
rayuwar Bahaushe ta fuskar gudanar da wasu sana’o’insa. An kuma ƙara fito da irin girmamawar da ake yiwa dare a Bahaushiyar al’ada
musamman wajen bauta da bukukuwansa.
Manazarta
Abubakar
A. T. (2015) Ƙamusun Hausa . Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Bargery
(1937) Ƙamus Turanci zuwa Hausa Northern Nigerian Publication
Company,Zaria
BUK(2006) Ƙamusun Hausa .
Bunza AM
(2006) Gadon feɗe Al’ada. Tiwel Nigeria Limited Surulere, Lagos.
Imam A
(1955) Magana Jari ce. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria.
Imam A
(1937) Ruwan Bagaja. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria.
John T. U
(1937) Jiki Magayi. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria.
Ɓalewa A (1955) Shehu
Umar. Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Kano M da
wasu (1933) Dare dubu da ɗaya. Northern Nigerian
Publication Company,Zaria.
Ɗangambo (1980) Kitsen
Rogo. Kamfani Triumph Kano
Zango T.
(1959) Da’u Fataken Dare. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria
Ingawa A
(1970) Iliya Ɗan Maiƙarfi. Northern Nigerian
Publication Company,Zaria
Daura S A
(1970) Tauraruwar Hamada. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria.
Katsina
D. U (1980) Kulɓa na Ɓarna. Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Ladan Y.
(1980) Zaman Duniya Iyawa ne. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria.
Ɗangogo (1970) Tabarmar
Kunya. Northern Nigerian Publication Company,Zaria.
Katsina
M. S (1960) Uwar Gulma. Northern Nigerian Publication
Company,Zaria.
Yahaya Y.
I (1980) Tatsuniyoyi. Longman Press Ibadan
[1] Habibu
A. Sarki (2000) zuwan musulunci Afrika da shigowarsa Ƙasar
Hausa babu kamfani a kano.
[2]Sa’idu
Abubakar hira da shi a bakin Kasuwar Sati Kaduna 18/6/2012.
[3] Dubi Littafin Tatsuniyoyi. Yahaya
Y.I (1980) Longman Press Ibadan
[4] Filin Yara Manyan Gobe Radiyo Najeriya
Kaduna 20/5/1999.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.