Ticker

6/recent/ticker-posts

Ballagazar Uwa: Tsakure A Kan Wasu Daga Cikin Dabi’un Iyaye Mata Masu Ra’ayin Ko-In-Kula

WANDA AKA GABATAR A KWALEJIN KOYON LARABCI DA ADDININ MUSULUNCI TA SHABAB DAKE UNGUWAR DOSA KADUNA. RANAR JUMA’A 1 GA FEBRAIRU 2013.

BALLAGAZAR UWA: TSAKURE A KAN WASU DAGA CIKIN ƊABI’UN IYAYE MATA MASU RA’AYIN KO-IN-KULA

DAGA

MU’AZU SA’ADU KUDAN

SHIMFIƊA:

Ma’anar Ballagaza:

Na nufin mace mara kamun kai,da rashin kishin kai,da rashin natsuwa,kuma makwaɗaiciya. Haka kuma ana iya cewa mai ƙarancin wayau,mara tsafta,kucaka ko ƙazama. Ana iya kiranta da sauna ko sakarya,kosagalaɓa,ko samodara,amma dai suaanta na yanka shi ne “Ballagaza Bankaura.

Hoton Ballagaza:

Da zarar ka yi kaciɓis da Ballagaza kana iya ganeta,tun daga ɗaurin zani. Domin Bahaushe yace,sakaryar mace tun daga ɗaurin zani ake ganeta,saboda idan ta tashi ɗaurawa ta ɗaura da dama. Daga can ƙasa ta saki leɓen kishiya.

Kai ba kitso, ƙafa babu ƙunshi, Ga jirwaye a sha-raɓa da ƙwauri.

Kaushi da ƙauje sun ɓata ƙafar ƙazama,fuska kuwa babu mai ba koya (hoda) Babu su ja-gira a fuskar kucaka, Hannayenta ma babu wanki

Ba ta yanke farce bare tai suwaki,kaga haƙoranta sun zube babu fiƙa.

Idan a cikin gida ka hango ta duba,shi ɗaurin zanin ta ɗaura shi kandame (a ƙirji) ,Can a jima ya koma ture (iyaka cinya). Kai Allah wadai da siffar ƙazama.

Ma’anar Uwa:

Duk macen ta ɗauki ciki na haihuwa na tsawon watanni 7,ko 9,ko12,ta haifeshi. Wannan ita ce ake kira uwa ga abin da ta haifa,yana iya kasancewa jariri (na miji) kojaririya (‘ya mace).

Faɗaɗa Ma’anar Uwa:

Baya ga ma’anar uwa ta asali,sai Bahaushe kuma ya ɗauki Kalmar ya faɗaɗa ma’anarta. A inda yake amfani ita ga wasu abubuwa da dama,kamar haka:

 1. Uwar ɗaki (mutum ya samu wata mata wadda ta girmeshi ya rinƙa girmamata. Ita kuma tana lura da shi,ko kyautata masa da tausayi kamar yadda uwa kan yiwa ɗa).

 2. Uwar goyo (matar da ta riƙe ko goya mutum tun lokacin yayen daga shan nono,wasu kuma da ɗan girmansu. Wani riƙon kuma na tabanni ne,mace ta ɗauko yaro,ko a tsinta ta mai da shi ɗanta).

3. Uwargida (matar da mai gida ya fara aura kafin amarya).

GABATARWA.

Da sunan Allah Mai rahama Mai jinƙai, Mai kowa, Mai komai, Mai aikata abin da Ya so, ga wanda Ya so, a sadda Ya so, a yadda Ya so, ko ana so ba a so dole bayi su so. Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugaban halittu Annabi Muhammadu, da Alayensa da Sahabbansa.

Wannan muƙala zata ɗan taɓo, wasu daga cikin ɗabi’un iyaye mata waɗanda Bahaushe ke ƙyama ta kowace fuska. Idan aka dube su ta mahanga al’ada sun saɓawa al’adun Bahaushe. Haka kuma idan aka dube su ta mahanga addinin musulunci,nan ma sun saɓawa addinin. Domin sun yi ban-tafin makafi da shari’ar musulunci,saboda ɗabi’un sun yamma,ita kuma shari’a ta yi gabas. saboda haka babu inda suka haɗu. Idan kuma muka kalli waɗannan ɗabi’u a hankalce,sai muce sun saɓawa hankali. Wannan muƙala na nufin ta fito da wasu daga cikin ɗabi’un iyaye mata, tare da nuna irin nauyinsu da matsayinsu a mizanin al’adar Bahaushe. Bisa dalilin ƙyamarsu da ake yi,tare da gudun aikatasu ne ya sanya ake kallon mai yinsu shi ma ya zama abin ƙyama. Don haka duk macen da ta kasance tana aikata irin waɗannan ɗabi’un,ita ma ta zama abin ƙyama ke nan ga mijinta, da danginta,da abokan zama,kai da ma sauran al’umma baki ɗaya. In ban da ‘ya’yanta, ko su ma don ya zama dole.

Wannan shi ne dalilina ko hujjata da suka sanya na kira muƙalar da suna ‘’Ballagazar Uwa’’. Bayan haka wannan muƙala riga ce da babu wuya duk wadda ta saya ta huda ta sanya, to ita ce ballagazar Uwa. Domin haka zaɓI ya rage ga mai shiga rijiya,ko dai ki zama uwa ta ƙwarai,son kowa ƙin wanda ya rasa. Ko kuma ki zama ballagaza uwa ba a bin sha’awa ce ba.

1. Rashin kamun kai: Zan fara da halin ballagaza na fari,watau rashin kamun kai. Duk matar da ta zama mara kamun kai,ba ta da daraja a idon kowa. Kaɗan daga ɗabi’un mace mara kamun kai sun haɗa da : cin abinci akan hanya,ko a kasuwa,ko kuma a cikin taron jama’a. Haka kuma takan kasance mai yawan Magana tare da ɗaga murya. A kasuwa kuma ta yi ta yin surutu da maza babu gaira babu dalili. Misali wajen ‘yan tireda,da masu yari (ɗan kunni da sarƙa) da masu bulawus da sauransu. Wata saboda rashin kamun kai, har dariya tare da ba a zaka ji suna yi da wasu watsattsun maza wanda idan ba a yi sa’a ba, sai ɓarna ta auku.

Illolin Rashin Kamun Kai:

Zubar da mutumcin kai,da na ‘ya’ya,da na miji,wanda kan iya haifar da aukuwar ɓarna,misali kamar kwartanci,ko fyaɗe, ko magannun banza.

2. Rashin natsuwa: Ɗabi’a mai bin wannan ita ce rashin natsuwa, dukkan mace ana bukatar da ta kasance mai natsuwa a al’amuranta gaba ɗaya. Matuƙar a ka ce ta rasa natsuwa, to ta zama cikakkiyar ballagaza. Bisa hujjar cewa ana alaƙanta natsuwa da hankali ne,rashin ta kuma ana dangantashi da hauka. Duk abin da mace zata yi ana bukatar natsuwa tun daga Magana,ko tafiya,ko aikin girki,ko rainon yara ko miji da sauransu. Mace ta ƙwarai kan yi Magana da mijinta cikin natsuwa,babu hargowa. Haka kuma idan tana yin Magana da ‘ya’yanata takan yi masu a natse ba hayaniya,don su ma su koya.

Tafiya: Game da tafiya mace natsattsiya an so ta rinƙa yin tafiya cikin natsuwa ba faram-faram ko bagazan-bagazanba. Akwai tafiyar da mace zata rinƙa yi wadda ta dace,idan ta fito daga gida tafiyar natsuwa ake so. Idan kuwa a gida take to rinƙa yiwa mijinta yauƙI,tafiyar toron giwa (ƙasaita) don ta burge shi kuma ta ɗaure abin ta a gida. Domin idan ba ta yi ba,wata a waje ta yi masa ta ƙwace shi.

Aikin girki: Dangane da aikin girki kuwa, shi ma ana son natsuwa. Domin dole sai in akwai natsuwa ne za a samu abinci mai tsafta kuma mai daɗI, sannan kuma ayi shi akan kari (da wuri). Mace mai yin daren tuwo ba ta da kwar jini,akwai wata Karin Magana mai cewa: “mai daren tuwo kya ci da buzuzu”. Ya dace `mace ta iya girki,sannan kuma ta koyawa ‘ya’yanta,don kar su yi aure ba su iya ba, daga a baya a zo a ji kunya.

Rainon ‘ya’ya da na maigida: Dangane da rainon ‘ya’ya da na maigida,ana iya cewa sai mai natsuwa kan iya yinsa cikin ƙa’ida. Tabbas mace natsuwa ce ke iya tattalin ‘ya’yanta da mijin ta. Dole ne ta kiyaye ɗabi’un ‘ya’yanta masu kyau da marasa kyau. To haka shi ma mai gida ya kamata ta kula da kyautata masa, ta fuskar kwantar masa da hankali,lallashinsa a wajen Magana,shimfiɗa,da dukiyarsa, da mutuncinsa. Mace mai dabara kan ɗaure mijinta kyakkyawar ɗabi’a. Tun daga tsaftaceccen abinci mai daɗI, da kuma tsaftar jiki,da na muhalli. Kuma ta kasance mai daddaɗar Magana cikin murya tattausa,tare da shagwaɓa da narkewa.

Kyautata shimfiɗa: Kyautata shimfiɗa,a shimfiɗu kuma a shimfiɗar,ban da musu a shimfiɗa. Haka kuma,ki kula da abubuwa uku a game da shimfiɗa,kamar 1. kafi shayi (shimfiɗar bayan sallar asuba). 2. Yaushe gamo? (idan mai gida zai tafiya). 3. Yaushe rabo? (idan maigida ya dawo tafiya). Bahaushe yace: “igiyar ido tafi ƙiri ɗauri” ma’ana idan mace ta iya kallo,kuma ta yiwa mijinta to baya iya zuwa ko’ina (fari, ko ina zuwa?,ko ya da carbi).

3. Ɗabi’ar kwaɗayi: Bayan wannan kuma,sai ɗabi’ar kwaɗayi. Matuƙar a ka ce mace makwaiɗiya ce,to haƙaƙa tana cikin haɗari. Domin Bahaushe yace : “kwaɗayi mabuɗin wahala”ko “idan da kwaɗayi da wulakanci” ko “idan baki ya ci dole ido yai kunya”. Da sauran maganganu da dama masu nuna illar kwaɗayi a rayuwa. To don haka duk macen ked a kwaɗayi ballagaza ce,saboda tana iya faɗawa haɗarin kwartanci. Kwaɗayi ya ƙunshi son abin duniya (kuɗI da komatsan duniya) ,ko kuma son cin daɗI kamar nama,ko kifi,ko kayan ƙwalam da maƙulashe. Yawan son abin duniya ke sa mace karɓar kyauta,ko roƙo a inda bai dace ba. An sha samun matan da aka yiwa kyauta daga baya abin ya zama fitina. Ko kuma wasu matan a saboda tsire ko balangu ko kaza ko kuma atamfar anko, sai su bad a kansu. Wasu kuma a saboda kuɗI,ko a wurin talla,sais u bad a kansu a ballagazar arha.

4. Rashin kishin kai: A game da rashin kishin kai kuwa,ana iya cewa shi ma wani hali ne na ballagazar uwa. Duk inda a ka samu mace wadda ba ta san ƙimar da darajar janta ba. To wannan it ace Ballagaza. Da farko dai ba ta da kishin kanta,ba ta kishin miji,sannan ba ta kishin ‘yarta. Tura ‘ya talla rashin kishi ne,kuma yana yin ɓarna ba kaɗan ba.

Kishi a rashin kishi: kishin banza (kishin mai dadaro). A inda take ƙyamar mijinta ya ƙara aure, amma kuma yana da farka a waje. Ta ƙi zama da kishiya, amma ƙawar Alhaji ko Amimiyarsa ko abokiyar aiki za ta zo gidan,kuma ta karɓe ta hannu bibiyu. Duk ɓarnar da miji zai yi indai ba maganar kishiya to daidai ne.

Bisa la’akari da bayanan da suka gabata. Kai tsaye muna iya cewa,duk macen da ta kasance da ɗaya daga cikin waɗannan ɗabi’u da aka lissafa. To ta zama mara wayau,kuma ba ta da tsafta, kuma ta zama ƙazama. Ta zama Ballagaza komai ilminta,komai barikinta, tana yin ɗigirgire ko kan-tafi da rayuwarta.

 Bisa wannan dalili ya zama wajibi ga dukkan namiji ya ɗauki matakin riga-kafi. Babban riga-kafin kuwa shi ne,zaɓarwa ‘ya’yansa uwa ta gari tun kafin yin aure. Dole ne ya yi taka tsantsan,ya yi kaffa-kaffa wajen neman matar da zai aura.

ZAƁARWA 'YA'YA UWA TA GARI.

Wajibi ne ga dukkan mahaluki mai hankali da yayi niyyar yin aure, to ya yi ƙoƙarin zaɓarwa 'ya'yansa uwa ta gari, ma'ana mai tarbiyya da son addini. Kar ya bi son zucEiya ya auro mace don kyau, watau kyakkyawa, ko 'yar wane, watau mai nasaba (mai kuɗi, sarauta, muƙami). Wannan magana ta yi dai-dai da wani bayani da Manzon Allah (S. A. W) ya yi cewa ku auri mace ma'abuciyar Addini. Domin yace in ka yi aure don kyau, to lallai kyau kan ƙare in ta tsufa, ko nasaba don mulki na iya ƙarewa, amma shi Addini ba ya ƙarewa.

Bayan haka, zaɓarwa 'ya'ya uwa ta gari kamar hutar da kai ne, domin in ka haifi yara da mace ta ƙwarai, to kamar ita ce makarantar su don zasu koyi komai na ƙwarai daga wurinta. Saboda masu hikima sun ce uwa ita ce makarantar farko ga yaro. Haka kuma in mutum ya kuskure ya auri Ballagazar mace mara tarbiya, to ya kashe kansa da kansa, kuma yaransa sun shiga uku. Babban dalili shi ne, ita ba ta da tarbiya, ba ilimi balle addini, to a nan ina makarantar farko take? Sai dai su koyi zagi da miyagun halaye.

MATSAYIN UWA:

Matsayin uwa ga ɗan da ta haifa ba ƙarami ba ne, saboda kuwa wannan matsayi, Allah (S. W. T) Mahaliccinmu ne ya ba ta shi. Wani abin lura shi ne, tun daga ranar da miji ya kwanta da matarsa suka sadu, Allah (S. W. T) Ke nuna ikonsa watau in aka samu shigar ciki. Tun daga wannan rana ta dinga gwagwarmaya da wannan ciki tun yana ɗigon maniyyi kwana arba'in (40) , ya koma gudan jini kwana arba'in (40) , ya koma gudan tsoka kwana arba'in (40) , sannan ya zama ɗan tayi ke nan, daga nan har halittunsa su haɗu, duk wannan al'amari na faruwa ne, a cikin jakar mahaifa a cikin uwa.

 Wannan rayuwa da jariri kan yi a cikin duhun jakar mahaifa a cikin uwa ya gudana ne kamar haka: -

 1. Da farko dai yana samun abincinsa ne ta hanyar cibiyarsa da take haɗe da wasu hanyoyin jini, a wannan hali ne duk irin abincin da uwar da ta ci, to shi ma tayin (ɗan jinjiri) zai samu ta hanyar cibiyarsa da jijiyoyin jini kan ɗauko.

2. Na biyu shi ne jini na yawo ne watau zagaya jikin ɗan Adam ne tare da taimakon aikin zuciya, ma'ana bugun zuciya, shi wannan bugawa da zuciya take yi kan aika da jini a dukkan sassan jiki gaba ɗaya, wanda kuwa ya haɗa har da ciki inda ɗan tayin jariri yake kwance ko ɗan tare da mahaifa.

 Wannan kaiwa da komowa da jini ke yi, tare da taimakon bugawa da zuciya kan yi, yana gudana ne har tsawon lokacin da jariri ya ɗauka ya saba kuma bai san wani bugun zuciya na daban ba, sai wannan watau na uwarsa.

 Babban dalilin da yasa yaro kan gane mahaifiyarsa bayan an haife shi. Akwai wani bayani da wani malami ya yi kamar haka: -

 “Jariri yakan gane ko bambance bugun zuciyar uwarsa da na wata mace daban, wannan ya haifar da zarar jariri na kuka alhali yana hannun wata da ba uwarsa ba, matuƙar uwarsa ta karɓeshi ta kifa shi a ƙirjin ta zai ji bugun zuciyar ta wanda ya riga ya saba, to da ya ji sai ya yi shiru.

 DANGANTAKAR YARO DA IYAYE DA GADO

 Akwai wata dangantaka a tsakanin yaro da iyaye, baya ga haihuwa da raino da tarbiyarsa. Wannan dangantaka kuwa ita ce ta fuskar gadon wasu halayensu ko ɗabi'un su, ko cututtuka. Ana gadon wasu halaye ko ɗabi'un iyaye, wannan kuwa ba Bahaushe kaɗai ba har da masu ilimin kimiyya (scientist, Behavioral Sciences) , sun tabbatar da wannan. Sukan kira shi da turanci “heredity”. A al'adar Bahaushe ana hasashen cewa lallai yaro kan gaji jin kunya, haƙuri, natsuwa, basira daga iyaye, haka kuma yaro kan gaji rashin kunya, da saurin fushi, da faɗa,da hargagi da daƙiƙanci. Ban da wannan kuma a kan gaji sata, kyauta, rowa da sauransu.

 Bayan wannan kuma akwai wasu cututtuka da akan gada daga iyaye musamman uwa. kamar hauka, amosani, jini (sicler) , kuturta, hawan jini, ciwon suga da sauransu. Yaro kan gaji wasu cututtuka daga iyayensa, a wani lokaci ma har daga kakanni ko dai daga wani a zuriya.

 Baya ga wannan kuma sai wani gado da yake ba sabun ba, Duk da yake ana samunsa, kamar wajen inda jika na wajen 'ya mace kan gaji kaka na wajen uwa, kamar sarauta ko jagoranci, roƙo, ilimi. Domin a kan samu wani yaron da kan nuna alamar jagoranci ta fuskar yadda yara ke binsa ko a wajen wasa, wasu ya kan ɗore har girma, inda za ka bincika sai ka iske akwai wani kakansa wanda ya taɓa yin jagoranci ko sarauta.

 Haka kuma yaro kan gaji roƙo ta wajen kakansa akan samu wasu suna zama maroƙa ko mawaƙa. To, amma da za a bincika sai a iske ya gaji roƙo ta wajen kakansa ɓangaren uwa.

 Dangane da ilimi kuwa, akwai wasu da yawa zaka iske sun zama malama, amma da za a bincika, sai a iske iyayensu basu yi ba, amma kakansu na wajen uwa ya yi.

 Bugu da ƙari, wasu daga cikin Hausawa na yin aure ne ta hanyar binciken zuriyar da mata ta fito, shi ya sa ma ake cewa: “mai son miya ya auri tsohuwa” mai son shimfiɗa ya auri budurwa” “mai son ɗan ƙwarai ya auri isassa” kowa ya auri sakarai yana da takaici”. Sau da yawa a kan samu saɓani tsakanin iyaye da 'ya'yansu a lokacin aure, saboda su iyaye suna da tarihi na zuriyar, ko sun san asalin iyayen yarinyar, shi kuwa bai sani ba. To a ƙarshe dai abin da iyayen ke gudu, shi ne, irin wancan gado. To, amma kuma in kyakkyawan hali ne, sai ka ga har ƙoƙarin haɗa aure ake da zuriyar su wane. A irin wannan hali ne Bahaushe kan ce: “ai wane ya sha a mama ko ya tsotsa a mama”. Ma’ana ya gaji uwarsa. Akwai karin maganganu da dama da suka tabbatar da wannan tunani kamar haka: -

i. Harbi ga ɗan jaki gado.

ii. Barewa tai gudu ɗan yai rarrafe?.

iii. Haifi ka ga kamarka.

iv. Duk faɗin gida magajinsa ɗaya.

v. Mai son ɗan ƙwarai ya auri isassa.

Shi kuwa Malam Aliyu Namangi Zariya a wata rubutacciyar waƙa mai suna waƙar ƙazama cewa ya yi: -

WAƘAR ƘAZAMA

1- Ya Allah Rabbana taimake mu,

Mu gargaɗI ‘ya uwa ga auren ƙazama.

2- Auren tsohuwa hasara ga yaro,

Gwammaci tsohuwa da auren ƙazama.

3- In ba ka son tan e ba kau tambaye ni,

In Allah Ya yarda ka san ƙazama.

4- Mummunan halin ƙazama na fari,

Ba ta face miji na sai da dama.

5- Mai son cin tuwonta sai ya ci gashi,

Susan kai hagu na tofi da dama.

6- Hanci majina idanunta kwantsa,

Dattsa ya daɗa wa bakin ta girma.

7- Sai ka ga tai jagal da suma da dauɗa,

Ga bauli a kwance tashin ta fama.

8- Ba mai son kitso bat a kasa aski,

Taba ya dafe haƙoran ƙazama.

9- Gude ba ƙoƙari baga kasa girki,

Ga haɗama a zuci ƙoshin ta fama.

10- Ran girkinki ba a ƙoshi da jiɓi,

Shi naman miji ki cinye shi a tsama.

11- In ta ga ka fito kamar za ka azure,

Sai sababi ya tashin don ɓata girma.

12- Kaji, bar neman fita ina tsame nama,

Yau dai kai rabon a zage ka kaima.

13- Tun da ka sai kitse ya narke a girki,

In aka zo rabo rabawarsa fama.

14- Wanda ka bashi ƙanƙana sai y arena,

Kowa so shike shi karɓa da girma.

15- Ran nan ma ka sai ƙashi na ci zagi,

Gun ƙwarin gidanka mai ya da girma.

16- In tace da ni ƙazama in rama,

Wanda ya san kumatu ya san ƙazama.

17- In tace ina ci ne in rama,

Domin ga tasalla ƙoshin ta fama.

18- Kwana goma jeer haifanta goma,

Ba taran miji ga haifan ƙazama.

19- Ita ko bante ta ƙetare sai ta haihu,

In ka san kuɗI su ƙare a suna.

20- Ya Alah daɗa wa matanmu tsabta,

Ka da Allah ka ba mu mata ƙazama.

21- Tun da mijin ƙazamiya zai ji kunya,

Can aljanah babu mata ƙazama.

HAƊARIN TALLA GA ‘YA MACE

Haɗari na nufin mummunan sakamako da zai iya biyo bayan aikata wani aiki. Ko wane mugun matsayi da za a iya faɗawa a dalilin aikata wani aiki bayan ko ana cikin yinsa.

Talla kuma na nufin a ɗauki abin sayarwa don a zagaya ko kuma a zauna ana yin bayani abin da ake sayarwa saboda a jawo hankalin mai buƙata saboda ya saya.

Dangane da haɗarin talla ga ‘ya mace, ana iya cewa abubuwan da yarinya ke iya gamuwa ko faɗawa cikinsu ba tare da ta so ba, ko ba ta so ba. Babban haɗarin talla ga ‘ya mace shi ne faɗawa fasiƙanci, watau zina. A wasu lokutta ko da yarinya kamammiya ce wata u ta na da tarbiya to da zarar ta fara talla, sai abokan tallar watau ƙawayenta sun gurɓata mata tarbiya ta hanyoyi daban daban. Ko kuma mazaje da sukan kira ta don sayen abin sayarwa, wasu ba da zuciya ɗaya suke saye ba. Akwai masu kiranta kamar za su saya sai su fara yi mata zancen banza, tun tana ƙyama sai ka ga yau da kullum ta fara sabawa har saiske tana kokuwa da maza ba kunya ba tsoron Allah.

Bayan wannan, yarinya kan koyi rashin kunya a inda za ta koyi miyagun maganganu, ciye-ciye a titi, kokaye-kokaye, zage-zage da sauransu.

Waɗannan bayanai da suka gabata ba a ɓoye suke ba, a sarari suke domin kuma ‘yan matan da suka yi cikin shege a wuraren talla ba za su ƙirgu ba. Wasu yaran kuma sun ɓace gaba ɗaya har abada an rasa su.

Bugu da ƙari, shi dai tallan nan a wasu a kan yi shi ne don a yi wa yarinya kayan ɗaki watau danki, wanda wani lokaci kwalliya ba ta biyan kuɗin sabulu. Domin ribar da ake samu a wurin talla ba ta taka kara ta karya ba. In aka tattara jarin watau uwar kuɗin da ita ribar sai a iske basu kwaranye abin da ake buƙata, kamar tallan goro, gyaɗa, ƙosai, tuwo da sauransu.

Bayan haka, a sanadiyyar tallar nan yarinya kan yi asara goma da goma domin kuwa ta kan yi asarar karatun addini da na zamani (boko). Kai a bar ma maganar ilimi hatta tarbiyya da bgirki mai talla kan yi asararsu. Ta fuskar ibada nan ma a kan yi asararsa kamar sallar azahar, la’asar, magriba da isha’i, don kuwa an shagala da talla ba za a damu da an gaji ba a maganar ramuwar sallar. Talla kan yi illa ga wasu yaran ba a sani wani lokaci sai ciwo ya ci ƙarfinsu sannan ake ganewa, wasu kuma a wurin tallar suke ɗaukar cutar, wasu a wurin tallar suke gamuwa da iskoki (aljanu).

To Jama’a ina mafita?:

Tun da mun riga mun ji ɗabi’u da siffofin ballagazar uwa. ashe ya zama wajibi mu tambayi kanmu ni,da kai,da shi. Bisa abin da ya dace mai hankali ya yi,domin kar mu faɗa rami. Mun dai ji matsayin uwa ga ‘ya’yanta,tun daga wajen gado,da koya tarbiya da sauran al’amura na yau da kullum. Ke kuma mace wajibi ne ki kula tare da kiyaye waɗannan ɗabi’un, don ki kare kanki,da ‘ya’yanki,har da mijinki daga ɓata suna ko halaka.

 KAMMALAWA;

A ƙarshe wannan muƙala ta ɗan taɓo, wasu daga cikin ɗabi’un iyaye mata. Tabbas su ne waɗanda Bahaushe ke kyama ta kowace fuska. Idan aka dubesu ta mahanga al’ada,da addinin musulunci,da kuma a hankalce sun saɓawa al’adu,da addinin Bahaushe. Idan kuma muka kalli waɗannan ɗabi’u,sai muce sun saɓawa hankali. Wannan muƙala ta fito da wasu kaɗan daga cikin ɗabi’un ne, tare da nuna irin muninsu,da nauyinsu da matsayinsu a mizanin al’adar Bahaushe. Bisa dalilin ƙyamarsu da ake yi,tare da gudun aikatasu ne ya sanya ake kallon mai yinsu shi ma ya zama abin ƙyama. Don haka duk macen da ta kasance tana aikata irin waɗannan ɗabi’un,ita ma ta zama abin ƙyama ke nan ga mijinta, da danginta,da abokan zama,kai da ma sauran al’umma baki ɗaya. In ban da ‘ya’yanta, ko su ma don ya zama dole.

Mun riga mun ji irin illolin da waɗannan ɗabi’u suka yi,ko zasu yi mana, ta fuskoki marasa iyaka, kuma ta kusurwoyi daban daban. Domin haka,ina fatan wannan muƙala, ta zama kamar matashiya ce ga masu hankali daga cikinmu maza da mata. Allah Ya tsare mu Ya bamu ikon gyarawa amin. Assalamu alaikum.

 MANAZARTA

Ladan Y. (1980) Zaman Duniya iyawa ne. Northern Nigeria Publication

 Company Zaria.

Maryam S. L. (1993) Kishi kumallon mata Bushara Publication House, Gusau.

Madauci I. (1963) Al'adun Hausawa Northern Nigeria Publication Company, Zaria.

Sadiya G. Y. (2005) Talauci Hauka ne? Super Print Press.  Kano.

Saulawa I. (2000) Jagorar fahimtar tavin Hankali. Katsina

 Printing Presss.

Zindani A. A. (2000) Human Development Muslim World League Printing Press Makka. Saudi Arabia.

Yunus I. (2005) Wa'azi a Muhadara, Masallacin Jumu'a na

 Kinkinau,Kaduna.

Zainab M. K. (2008) Hira da ita a gidanta No. 1 Ƙofar Fada Kudan.

Stone & Cozon (1985) New Biology for Secondary School

Amina M. S (2009) Kallabi. Jaridar Leadership Hausa.

 21/5/2009.

Umma U. S. (2008) Don Iyali. Jaridar Nasara,20/10/2008.

Bello M. (2009) Kiwon lafiya. Jaridar gaskiya tafi Kwabo.

 26/3/2009.

Safiya J. (2006) Himma dai mata. Jaridar gaskiya ta fi Kwabo.

 20/4/2006.

Brown. l. J. (1975) The Evolution of Behavior,printed in the United State of America.

Choge B. (1990) Waƙar Sakarai ba ta da wayau. Ballagaza bankaura. 

Post a Comment

0 Comments