𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahamatullahi wabarkatuhu Barka da safiya da fatan an tashi lafiya ina da tambaya mine ne hukuncin macen da mijin ta ya mutu, Kuma a ranar da ya rasu shi ne kwanan idda ta ya ƙare ko za ta ƙara ne? Allah ƙara lafiya da imani na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikum salam
warahamatullahi wabarkatuhu
Idan mijinta ya rasu
alhalin tana cikin iddar saki mai dawowa (saki raj'iyyi) kuma rasuwar ta zo ne
kafin iddar ta cika ko a daidai ranar da ake gab da cikar ta, to za ta sauya
zuwa iddar mutuwa (wata huɗu da kwana goma) kuma tana da gajiyar gado a tare da shi.
Idan miji ya saki
matarsa saki ɗaya ko biyu kuma tana
cikin idda, a shari'ance ita ma'aikaciyar aure ce, kuma miji na da ikon mayar
da ita. Idan ya rasu a wannan lokacin (koda kuwa ranar ƙarshe ce ta iddar), ta
koma iddar mutuwa.
Idan har iddarta ta
cika kuma ta gama lakacin da ake buƙata kafin numfashin
mijin ya yanke, to auren ya riga ya mutu gaba ɗaya, kuma ba ta da iddar mutuwa ko
gado.
Idan mijinta ya mutu
tana da ciki, haihuwarta a ranar ko bayan rasuwarsa na nufin ta gama iddarta ke
nan. Ba ta buƙatar cika watanni huɗu da kwanaki goma (iddar takaba) tunda ciki
ya riga ya sauka. Haihuwa shi ne abin da ke kawo ƙarshen iddar mace mai
ciki, kamar yadda aya ta 4 a cikin Suratu Aṭ-Ṭalāƙ ta nuna:
وَالّٰٓـىٴِۡ يَٮِٕسۡنَ مِنَ الۡمَحِيۡضِ مِنۡ نِّسَآٮِٕكُمۡ
اِنِ ارۡتَبۡتُمۡ فَعِدَّتُهُنَّ ثَلٰثَةُ اَشۡهُرٍ وَّالّٰٓـىٴِۡ لَمۡ يَحِضۡنَ ؕ
وَاُولَاتُ الۡاَحۡمَالِ اَجَلُهُنَّ اَنۡ يَّضَعۡنَ حَمۡلَهُنَّ ؕ وَمَنۡ
يَّـتَّـقِ اللّٰهَ يَجۡعَلْ لَّهٗ مِنۡ اَمۡرِهٖ یُسْرًا
Kuma waɗanda suka yanke ɗammani daga haila
daga matanku, idan kun yi shakka, to, iddarsu wata uku ce da waɗanda ba su yi haila
ba. Kuma ma'abũta cikinna ajalinsu, (shi ne) cewa su haifi cikinnansu. Kuma
wanda ya bi Allah da taƙawa, (Allah) zai sanya masa wani sauƙi daga al'amarinsa.
(Surah: At-Talaaƙ, Ayat: 4).
Saboda haka idan
mijinki ya rasu alhalin kina cikin wata tsohuwar idda ta saki kuma lokacin bai
gama cika ba ko da a karshen ranar ne, wajibi ne ki soke iddar sakin ki koma ga
iddar mutuwa (takaba) ta tsawon wata huɗu da kwana goma (4 months and 10 days). Kuma
Wajibi ne ki yi wannan takaba a cikin gidan da kuka saba zama da shi ko wanda
ya rasu ya barki a ciki.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.