Ticker

6/recent/ticker-posts

Ma'anar Sunan Binta

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum Malam ni sunana Binta. Wanda mahaifina ya sanya mun Amma sai na ji wasu malamai suna cewa ba suna ba ne. Shin malan yaya abun yake?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Sunan BINTA na nufin «Diya» ko «Yarinya» a harshen Hausa, kuma ya samo asali ne daga kalmar Larabci «BINT» (بنت) da ke nufin ɗiya ko 'ya.

Hausawa suna yin inkiyar sunan ne ga 'ya'yansu masu suna 'FATIMAH" wato FATIMA BINTU RASUL (Fatima 'yar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam). To daga nan ne sai hausawan suke yin wani kirari ga duk masu suna Fatimah, suna cewa "Fadima Binta". To daga nan kuma sai sukan kirata da suna "BINTA".

Sunan "BINTA" a asali ba sunan da aka tsara ya zama cikakken suna ba ne. Wato ba sunan yanka ba ne mai zaman kansa a harshen Larabci, amma ya zama suna mai zaman kansa a al'adance musamman a wurin Hausawa. Saboda sun saba da sunan, har suna sanya wa 'yayansu kai tsaye a matsayin cikakken suna mai zaman kansa, kuma babu laifi a sanya shi tunda yana da kyakykyawan ma'ana a harshen Larabci da al'ada. Ba a sami wani hani ko haramci daga malaman Musulunci game da sanya wa yara wannan suna ba, domin yana nufin 'ya ko kuma yana da nasaba da sunayen gidan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam).

Ana iya chanza miki sunan BINTA zuwa FATIMAH. Ya halatta a chanza wa mutum suna ko kuma shi da kansa ya chanza sunan idan ya zamanto akwai wata matsala tare da sunan. Kamar yadda Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi chanjin suna ga wasu daga cikin sahabbansa masu yawa, bayan sun musulunta. Kuma kamar yadda Sayyiduna Umar (ra) ya taɓa chanza wa matarsa sunanta daga "AASIYAH" (عاصية) zuwa JAMILAH.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments