TAMBAYA❓
Assalamualaikum warahmatullah malam Allah ya saka da alkhairi, Muna godia da yawa.malam tambayata ita ce meye hukunci tusar da take fitowa mata ta gabansu, bata dubura ba, tana Kara Amma bata wari, kuma idan kana da alwala, idan kaita, shin alwalarka tananan kota warfare? Allah ya saka da alkhairi
AMSA:‼️
Wa alaikumu salamu
warahamatullah,
Wannan iska da take
fita daga gaba tana warware alwala, ko da babu wari a cikinta kuma ko da ba
najasa bace, domin malamai sun tabbatar da cewa Annabi Muhammad ﷺ ya bayyana
cewa duk abin daya fito daga wurare biyu na jiki gaba da baya yana cikin abin
dake karya alwala, kuma wannan ya shafi maza da mata daidai domin abubuwan dake
karya alwala sun haɗa da fitar da iska
daga baya ko daga gaba, ko da kuwa iska ce kawai ba tare da najasa ta fita ba
Dalilin wannan ita ce
hadisin da aka ruwaito daga Manzon Allah ﷺ inda ya ce Allah baya karɓar salla in babu
tsarki wato alwala, kuma malamai sun bayyana cewa duk abin daya fito daga gaba
ko baya yana karya alwala, don haka idan aka fitar da iska daga gaba, dole ne a
sake alwala kafin yin salla ko wata ibada da ke bukatar alwala Wannan shi ne
ra'ayin malamai hudu na mazhabobi - Hanafiyya, Malikiyya, Shafi'iyya, da
Hanbaliyya - domin dukkansu sun yarda cewa fitar da kowane irin abu daga
al'aura, ko gaba ko baya, yana karya alwala.
Don haka, duk lokacin
da kin ji wannan tusan ya fito alhali kina da alwala, tilas ne ki sake yin
sabuwar alwala kafin ki yi salla. Amma idan wannan halin ya zama akai-akai, wato
kullum ko yawancin lokaci haka yake faruwa har baki samun lokacin tsarki mai
tsawo, to a wannan yana yin za ayi miki hukuncin mai uzuri kamar mai ciwon
yoyon fitsari istihada za ki yi alwala bayan shigar lokacin kowace salla, sannan
wannan alwalar tana wanka har zuwa fitowar lokacin sallar da take biye, kuma
fitowar iskar bayan kin riga kin yi alwala a wannan yana yin ba ta sake warware
miki alwalar ba, sai lokacin salla na gaba ya shigo. Allah Ya sanya mana sauki,
kuma Ya bamu lada bisa wahalar da muke sha wajen neman tsarki.
Wallahu ta'ala aalam
✍️MT
ABDULLAHI
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.