TAMBAYA❓
Salam Malam dafatan
kana lafiya ya karatu, Allah ya karawa rayuwa Albarka
Tambaya?
Meye hukuncin yin sallar nafila bayan sallar Asuba ya halatta ko akasin hakan?
Bissalam
AMSA:‼️
Wa alaikumu salaam
warahmatullah,
An haramta yin sallar
nafila bayan an gama sallar Asuba, har sai rana ta fito sosai wato ta tashi
kimanin tsawon mashi daya, kusan minti 15 zuwa 20 bayan fitowarta. Wannan
hukunci ne da jumhur malamai Hanafiyya, Malikiyya, Shafi'iyya, da Hanbaliyya
suka yarda a kai, sabanin sallar da take da dalili na musamman kamar sallar da
aka bata (ƙada'i).
Hujjar wannan ita ce
hadisan da Manzon Allah ﷺ ya hana yin salla a wasu lokuta guda uku, daya daga cikinsu shi
ne bayan sallar Asuba har saj rana ta fito. Daga cikin hadisan akwai fadin
Manzon Allah ﷺ: "Babu salla bayan Asuba har sai rana ta fito, kuma babu
salla bayan La'asar har sai rana ta faɗi" (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito).
Haka kuma an ruwaito daga Umar Ibn Al-Khattab (RA) inda ya ce Manzon Allah ﷺ ya hana yin
salla bayan sallar Asuba har sai rana ta fito, da kuma bayan sallar La'asar har
sai rana ta faɗi.
Dalilin wannan hani,
a cewar malamai, shi ne domin toshe hanyar da za a rikita al'amarin bautar rana
da ake yi a wancan lokaci domin kafirai suna sujjada wa rana a lokacin
fitowarta da faduwarta, don haka Musulunci ya bambanta al'ummar Musulmi da
wannan hali ta hanyar hana salla a wancan lokacin na musamman.
Sai dai akwai wasu
'yan bambance-bambance a tsakanin malamai kan wasu salloli na musamman dana ke
so na yi bayani akai:
1: Idan wani ya bar
wata sallar farilla ya manta ko ya yi barci har lokacinta ya wuce, sa'an nan ya
tuna bayan Asuba, jumhur malamai sun ce zai iya yin ƙada'inta ramawa ko da
a wannan lokacin ne, domin akwai dalili na musamman wato uzuri.
2: Idan wanda bai yi
raka'atanil fajir raka'a biyu na kafin farilla ba kafin ya shiga masallaci, ya
halatta ya yi ta bayan sallar farilla, kamar yadda hadisin Ƙais bin Amr ya nuna,
inda Manzon Allah ﷺ ya gani ya yi raka'a biyu bayan Asuba, sai ya tambaye shi, ya
ce bai yi sunnar Asuba ba tukuna, Manzon Allah ﷺ bai hana shi ba.
Amma in banda
wadannan hallayen na musamman, yin nafila ba tare da wani dalili na musamman ba
a wannan lokacin bayan Asuba har zuwa fitowar rana haramun ne. Allah Ya kara
mana ilimi mai amfani.
Wallahu ta'ala aalam
✍️MT
ABDULLAHI
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.