Ticker

6/recent/ticker-posts

Addu'o'in Karfafa Imani Da Karin Tsoron Allah

TAMBAYA

Assalamu alaikum Dan Allah a koya mana addu’ar ƙarfafa imani da ƙarin tsoron Allah da kusantar Allah

ADDU'O'IN ƘARFAFA IMANI DA KARIN TSORON ALLAH

AMSA:‼️

Wa'alaikumun salamu warahamatullah

Gaskiya na ji dadin Wannan tambayan domin yakamata yan'uwa musani cewa mafi girman ni'ima bayan shiriya ita ce ƙarfafan imani da taƙawa. Imani shi ne hasken zuciya, kuma duk lokacin da imani ya ƙaru, kusancin bawa ga Allah yana ƙaruwa, zuciya tana samun nutsuwa, kuma biyaya yia tana zama mai sauƙi. Saboda haka, Manzon Allah (SAW) duk da cewa shi ne mafificin halitta, ya kasance yana yawaita roƙon Allah Ya tabbatar da zuciyarsa akan addini. Wannan yana nuna mana cewa kowane Musulmi yana buƙatar yawaita addu'ar neman ƙarfafa imani, tsoron Allah da dawwama a kan shiriya.

Ga wasu kadan daga cikin addu'o'in da suka zo a Al-Ƙur'ani da Sunnah waɗanda ake roƙon Allah dasu domin ƙarfafa imani, ƙara tsoronSa da kusantarSa:

 اللَّهُمَّ يَا مُقَلِّبَ الْقُلُوبِ ثَبِّتْ قَلْبِي عَلَى دِينِكَ

Allahumma yā Muƙallibal-ƙulūb, thabbit ƙalbī 'alā dīnik.

Ya Allah, Mai jujjuya zukata, Ka tabbatar da zuciyata a kan addininka.

> اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ الْهُدَى وَالتُّقَى وَالْعَفَافَ وَالْغِنَى

Allahumma innī as'alukal-hudā wat-tuƙā wal-'afāfa wal-ghinā.

Ya Allah, ina roƙonKa shiriya, taƙawa, kame kai da wadatar zuci.

> رَبَّنَا لَا تُزِغْ قُلُوبَنَا بَعْدَ إِذْ هَدَيْتَنَا وَهَبْ لَنَا مِن لَّدُنكَ رَحْمَةً ۚ إِنَّكَ أَنتَ الْوَهَّابُ

Rabbanā lā tuzigh ƙulūbanā ba'da idh hadaytanā wa hab lanā min ladunka ramah, innaka Antal-Wahhāb.

Ya Ubangijinmu, kada Ka karkatar da zukatanmu bayan Ka shiryar damu, Ka bamu rahama daga gareKa. Lalle Kai ne Mai yawan baiwa. Wadannan addu'o'in yakamata mu yawaita shi acikin addu'o'inmu da mukeyi na yau da kullun domin karfafa imani da karin tsoron Allah,

Ya Allah, Ka ƙara mana imani mai ƙarfi, Ka cika zukatanmu da tsoronKa, Ka sanya mu cikin bayinKa na gari, Ka bamu sonKa da son duk abinda yake kusantar damu zuwa gareKa, Ka tabbatar damu a kan gaskiya har ƙarshen rayuwarmu, Kasa ƙarshen maganarmu ya zama Lā ilāha illallāh, Muhammadur Rasūlullāh (SAW)🤲

Wallahu ta'ala aalam

✍️MT ABDULLAHI

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments