Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Ba Ya Fita Zuwa Sallah A Masallaci Sai An Tayar Da Ikamah

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Ina matsayin maigidan da a kullum ba ya fita zuwa sallah a masallaci sai an tayar da iƙamah?

HUKUNCIN WANDA BA YA FITA ZUWA SALLAH A MASALLACI SAI AN TAYAR DA IƘAMAH

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

Hikimar kiran sallah ita ce a sanar da musulmin da suke nesa cewa lokacin sallah ya yi, don haka sai kowannensu ya tashi ya yi shirin zuwa masallaci, domin bayar da wannan farillar. Shiyasa a cikin kiran Ladan yake faɗin: Haya yia Alas Salaah da Haya yia Alal Falaah sau bibbiyu.

Amma ita iƙamah ana yin ta ne domin a sanar da waɗanda suka amsa waccan kirar ta farko har suka tabbata a cikin masallacin cewa, yanzu za a fara sallah. Shiyasa a cikinta ladan yake maimaita faɗin: Ƙad Ƙaamatis Salaah har sau biyu a cikinta.

Don haka, da zaran musulmi ya ji muryar ladan mai kiran sallah sai ya daina komai, ya shiga shirin amsa wa wannan kiran. Ya tashi ya kintsa ya taka cikin natsuwa zuwa masallaci. Ya shiga, ya samu wuri a sahun farko, ya tsaya ya yi gaisuwar masallaci da sauran nafilolin da aka so a Sunnah, sannan ya zauna ya jira Iƙamah.

Masu makara waɗanda ake tayar da iƙama alhali ba su a cikin masallaci suna da kaso a cikin maganar da Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya yi cewa:

« وَالَّذِى نَفْسِى بِيَدِهِ لَقَدْ هَمَمْتُ أَنْ آمُرَ بِحَطَبٍ يُحْتَطَبُ ، ثُمَّ آمُرَ بِالصَّلاَةِ فَيُؤَذَّنَ لَهَا ، ثُمَّ آمُرَ رَجُلاً فَيَؤُمَّ النَّاسَ ، ثُمَّ أُخَالِفَ إِلَى رِجَالٍ فَأُحَرِّقَ عَلَيْهِمْ بُيُوتَهُمْ ، وَالَّذِى نَفْسِى بِيَدِهِ لَوْ يَعْلَمُ أَحَدُكُمْ أَنَّهُ يَجِدُ عَرْقًا سَمِينًا أَوْ مَرْمَاتَيْنِ حَسَنَتَيْنِ لَشَهِدَ الْعِشَاءَ ».

Na rantse da Wanda raina yake a hanunsa, haƙiƙa! Na yi aniyar yin umurni da a tattaro kirare, sannnan in yi umurni da a kira sallah, sai kuma in umurci wani mutum ya yi limancin sallar, sai kuma in koma ga mutanen (da ba su zo masallacin ba), in kona gidajensu a kansu. Na rantse da wanda raina ke ga hanunsa, in da ɗayansu ya san zai samu ƙashi mai tsoka ko kofaton tunkiya masu kyau guda biyu da ya halarci sallar ishai. (Sahih Al-Bukhaariy: 7224).

Idan da ya zartar da wannan aniyar to da kuwa masu makara sun shiga cikin waɗanda zai samu a cikin gidajensu, kuma ya ƙoƙƙona su.

Maganin wannan shi ne mutum ya riƙa gaggawan yin shirin zuwa masallaci da zaran an fara kiran sallah, kafin sheɗan ya dawo ya fara nauyayar da shi da waswasi, kamar yadda Abu-Hurairah (Radiyal Laahu Anhu) ya riwaito daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) cewa:

« إِنَّ الشَّيْطَانَ إِذَا سَمِعَ النِّدَاءَ بِالصَّلاَةِ أَحَالَ لَهُ ضُرَاطٌ حَتَّى لاَ يَسْمَعَ صَوْتَهُ فَإِذَا سَكَتَ رَجَعَ فَوَسْوَسَ فَإِذَا سَمِعَ الإِقَامَةَ ذَهَبَ حَتَّى لاَ يَسْمَعَ صَوْتَهُ فَإِذَا سَكَتَ رَجَعَ فَوَسْوَسَ »

Idan sheɗan ya ji kiran sallah sai ya juya yana tusa har sai ya kai inda ba ya jin kiran sallar. Idan ladan ya yi shiru sai ya juyo ya fara sanya waswasi. Idan kuma ya ji iƙama sai ya sake tafiya har sai ya kai inda ba ya jin muryar, idan kuma ya yi shiru sai ya komo ya shiga sanya waswasi. (Sahih Al-Bukhaariy: 608; Sahih Muslim: 882).

A taƙaice dai: Abin da ya kamaci duk mai hankali shi ne, ya yi wa kansa faɗa, haka ma makusanta - kamar iyalinsa - su taimaka da tuna masa har ya riƙa halartan masallaci a kan lokaci.

Su ma ladan da liman su taimaka ta hanyar kashe ƙarar amsa-kuwwa (loudspeakers) a lokacin tayar da iƙamah da karatun sallah, tun da dai an sharanta su domin waɗanda su ke cikin masallaci ne. Su ma suna taimakawa wurin zuwa masallaci a makare. Domin galibi sai sun ji Iƙamar ce sannan suke tashi, maimakon daga sun ji kiran sallah.

Allaah ya ƙara mana fahimta.

Wal Laahu A’lam.

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments