𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh. Malam Khamis, da fatan kana cikin ƙoshin lafiya. Malam, muna ƙara godiya, Allah ya saka ma da mafificin alheri, ya biya ma dukkanin buƙatunka. Tambayata ita ce: Ya aka yi aka samu kiran salla? Mene ne falalar kiran salla da bin mai kiran salla? Kuma idan ana kiran salla a lokaci guda daga mabanbanta masallatai, sai na fara bin masallacin da na fara jin kiran sallarsa, ina farawa kuma sai na ji wani masallacin shi ma an fara kiran salla, ya zan yi ke nan? Zan yi shiru ne ko kowane zan bi? Kuma ya hallatta ana kiran salla in yi salla ko sai an gama kiran salla sannan zan yi kabbara? Kuma wace irin addu'a ingantacciya mutum zai iya yi bayan kiran salla? Allah ya saka da alheri, ya ƙara ma Malam lafiya da ilimi mai amfani.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa
rahmatullahi wa barakatuh.
Daga Ibnu Umar Allah
ya yarda da su ya ce: Musulmai sun kasance a lokacin da suka iso Madina, suna
taruwa su kintaci lokacin Sallah ba tare da an yi kira ta ba. Sai suka tattauna
wata rana a kan haka, sai wasunsu suka ce: Ku riki kararrawa kamar kararrawar
Nasara. Wasu kuma suka ce: A'a, sai dai kaho kamar kahon Yahudawa. Sai Umar ya
ce: Shin ba za ku tura wani mutum ya yi kira Sallah ba? Sai Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: «Ya Bilai, tashi ka kira sallah»
[4]. [4] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (604), da Muslim, a lamba ta
(377).
Akwai ruwayar data zo
cikin sunan na Abi Dauda 420, wadda ta nuna cewa Abdullahi Bn Zaid ibn Abdi
Rabbihi wata rana yana tsakanin bacci da falke sai wani yazo masa ya koya masa
kiran sallah, da gari ya waye yazo wajen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya baya yia masa, Ashe Umar bin khaddab ya dade da yin mafarki kiran
sallah kusan kwana ashirin amma bai gaya wa Manzon Allah (Sallallahu alaihi
Wasallam) ba sai ranar da Abdullahi ya gaya wa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam), sai manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) bai ce umar me yasa
baka gaya mun tun tunni ba. sai ya ce ya kai bilal tashi kaje ka kira sallah.
Wannan shi ne tarihin samuwar kiran sallah.
Imam Ibn Kudamah
Al-Makdisi ya ce: "Al'umma ta yi ijma'i akan cewa an shar'anta kiran
sallah domin salloli biyar". [5] al-Mugni: (1/ 293).
Kiran sallah yana da
babban matsayi da falala mai girma a Musulunci, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya ce: "Da mutane sun san babban alherin da ke cikin kiran
sallah da iƙamah, da sun yi kuri'a a kan wanda zai yi shi saboda
girman ladansa. (Bukhari da Muslim suka ruwaito).
A wani hadisi Daga
Abi-Hurairah Ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: “Da Mutane
Sun San Abinda Ke Cikin Kiran Sallah da Sahun Farko, Idan Akace Bazaka Samesu
ba Sai Anyi Ƙuri'a da Sun Yarda Ayi Ƙuri'ar”
(Bukhari da Muslim).
Allah na gafarta wa
mai kiran sallah gwargwadon tsawon muryarsa. Ba wani aljani ko wani mutum ko
wani dabba ko wani abu da zai ji muryar mai kiran sallah sai ya yi shaida
gareshi ranar Alƙiyama. Duk wanda ya yi sallah tare da jama'a a bayan
kiran sallah da iƙamah, mai kiran yana samun rabon ladan sallar dukkan su
ba tare da an rage na kowa ba. A ranar tashin kiyama, masu kiran sallah za su
fi kowa tsawon wuya (wato daraja da shugabanci zuwa rahama), domin su ne ke
kira zuwa ga bautar Allah.
Manzon Allah (tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: «Idan mai kiran sallah ya ce:
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, sai ɗayanku ya ce: ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, sannan ya ce:
ASH'HADU ALLA ILAHA ILLALLAHU, kuma shima ya ce: ASH'HADU ALLA ILAHA ILLALLAHU,
sannan ya ce: ASH'HADU ANNA MUHAMMADAN RASULULLAH, kuma shima ya ce: ASH'HADU
ANNA MUHAMMADAN RASULULLAH, sannan ya ce: HAYA YIA ALAS SALLAH, sai ya ce: LA
HAULA WALA ƘUWWATA ILLA BILLAH, sannan kuma ya ce: HAYA YIA ALAL
FALAH, sai ya ce: LA HAULA WALA ƘUWWATA ILLA BILLAH, sannan
ya ce: ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, kuma shima ya ce: ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR, sannan
ya ce: LA'ILAHA ILLALLAH, kuma shima ya ce: LA'ILAHA ILLA ALLAH, daga zuciyarsa,
zai shiga Aljanna» [37]. [36] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba
ta (611), da Muslim a lamba ta (383). [37] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta
(385).
Kuma idan mai kiran
sallah ya ce a sallar Asuba: "ASSALATU KHAIRUN MINAN NAUM, " to shi
ma mai sauraro zai faɗi irinsa; saboda faɗin Annabi (Sallallahu
Alaihi Wasallam) "Idan kun ji mai kiran sallah, to ku faɗi irin abin da yake
faɗi. Sai kuma ku yi
mini salati, domin shi wanda ya yi mini salati guda Allah zai yi masa salati
goma. Sannan sai ku roƙa mini waseelah a wurin Allaah, domin ita wani matsayi ne
a cikin Aljannah, ba ta dacewa sai ga wani bawa guda daga cikin bayin Allah, kuma
ina fatar in zama ni ne wannan bawan. Duk wanda ya roƙa mini waseeilah to
lallai ceto ya tabbata gare shi" (Sahih Muslim: 875).
Bin kiran sallah, sunnah
ce mustahabbiya ga kowane musulmi babba ko yaro, namiji ko mace, mai tsarki ko
mara tsarki, kamar mai janaba, ko mai haila, ko mai nifasi. Har mai bayar da
darasi (wa'azi) ko mai zikiri ko mai karatun Alƙur’ani ma, duk an so
su dakatar da abin da suke yi a lokacin da aka fara kiran sallah. Sai a bayan
sun gama maimaitawa da yin addu’o’in da suka biyo bayan hakan, sannan sai su
cigaba.
Bayan kammala kiran
sallah, akwai matakai da addu'o'i na musamman da Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya koyar damu, mu karanta domin samun lada da cetonsa a ranar
kiyama.
أَشْهَدُ
أَنْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ، وَأَنَّ مُحَمَّدَاً
عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ، رَضِيتُ بِاللهِ رَبَّاً، وَبِمُحَمَّدٍ رَسُولَاً، وَبِالْإِسْلَامِ
دِينًا
"Na shaida babu
abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai, ba shi da abokin taraya yia. Kuma lalle
Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam) bawanSa ne kuma ManzonSa ne. Na yarda
Allah shi ne Ubangijina, kuma Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam) Manzo ne, kuma
Musulunci shi ne addinina."
Bayan haka, sai mutum
ya yi salati ga Annabi Muhammadu (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi):
اَللّهُمَّ
صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ
وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اَللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى
مُحَمَّدٍ، وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارِكْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ
إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ
Ya Allah! Ka yi
rahama (da yabo) ga Muhammad da kuma alherin gidan Muhammad, Kamar yadda Ka yi
rahama ga Ibrahim da kuma alherin gidan Ibrahim, Lalle Kai Abin Yabo ne, Mai
Girma. Ya Allah! Ka albarkaci Muhammad da kuma alherin gidan Muhammad, Kamar
yadda Ka albarkaci Ibrahim da kuma alherin gidan Ibrahim, Lalle Kai Abin Yabo
ne, Mai Girma.
Sai addu'a Neman
Wasilah:
اللَّهُمَّ
رَبَّ هَذِهِ الدَّعْوَةِ التَّامَّةِ، وَالصَّلَاةِ الْقَائِمَةِ، آتِ
مُحَمَّدَاً الْوَسِيلَةَ وَالْفَضِيلَةَ، وَابْعَثْهُ مَقَامَاً مَحْمُودَاً
الَّذِي وَعَدْتَهُ
"Ya Allah!
Ubangijin wannan kira cikakke (na kadaita Ka), da sallah da za a tsayar da ita.
Ka ba wa Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam) Wasila (matsayi na musamman a
Aljanna) da daukaka, kuma Ka tashe shi a matsayi abin yabo (na yin ceto) wanda
Ka yi masa alkawarinsa.
Annabi (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce: Duk wanda ya karanta wannan addu'ar cetonsa ya tabbata
a gare shi ranar kiyama.
Bayan ka kammala
wadannan zikirai, za ka iya rokon Allah duk abin da kake bukata na alherin
duniya da lahira. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya baya yiana cewa
addu'a tsakanin kiran sallah da iƙama ba a maida ita
(ana karbarta cikin sauri).
Idan ana Kiran sallah
a lokaci guda daga mabanbantan masallatai, ba sai ka dinga sauyawa daga wannan
zuwa wancan ba. Ka amsa kiran farko da ka fara bi har ya gama. Idan masallacin
da ya fara kiran sallar shi ne mafi kusa da gidanka, to shi ne ya fi cancanta
ka bi. Idan masallacin farko ya gama, kuma na biyun yana kiran sallah har yanzu,
za ka iya amsa sauran kiran sallar tasa idan kana so. Babu wajibci akan duka.
Amsa kiran sallah sunnah ce mai ƙarfi (ko mustahabbi),
saboda haka amsa kiran sallah guda ɗaya ya wadatar da kai.
Ba a yin sallah idan
aka fara kiran sallah sai dai a saurari kiran sallah a kuma amsa masa. Saboda
haka Kada ka shagala da wani abu da zai sa ka kasa amsa kiran sallah koda
karatun Alkur'ani ne. Kar ka kabbarta sallah a dai-dai lokacin da kiran sallah
ke gudana har sai an kammala. Amma idan akwai dalili, kamar kana tsoron lokacin
zai ƙure ko za ka rasa jam'i, ya halatta ka fara sallah tun
ana kiran sallah. Ba haramun ba ne, sai dai bin ladan kiran sallah ya fi.
Allah Ya karɓi ibadunki, Ya ƙara mana ilimi mai
amfani da aiki nagari.🤲
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.