𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Don Allah ina da tambaya: yaya ake yin ramuwar sallolin farilla idan mutum bai san adadinsu ba? Wane tsari ya kamata a bi? Misali, shin mutum zai iya yin salloli biyar lokaci guda (ramuwa) yana ci gaba da yi har sai ya ji ya gamsu cewa ya biya abin da ke kansa? Ko kuwa sai ya riƙa yin kowace sallah a lokacin da ya tuna da ita daban-daban?
Haka kuma, shin ya
halatta mutum ya riƙa yin nafila alhali yana da bashin sallolin farilla a
kansa? Don Allah, a yi mana bayani Allah ya saka da alheri.”
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ramuwar sallolin da
ba a san adadinsa ba shi ne a yi ƙiyasin abin da ake
ganin ya wuce mutum, sannan a fara biya a hankali har sai an gama.
Ba lallai sai kin yi
salloli biyar a lokaci guda ba, amma ya halatta a yi hakan domin hanzarta biyan
bashin. Mafi sauƙi shi ne duk lokacin da kika yi sallar farilla ta yanzu,
sai ki biyo da ramuwar sallar da ta gabata a tare, kullum haka zaki dinga yi
har sai zuciyarki ta amince cewa kin gama biyan bashin.
Idan ba ki san
ainihin adadin ba, sai ki ƙiyasi (wato ki ɗauka misali shekaru
biyu+ ko ƙasa da haka) sannan ki fara biya. Allah Yana duban niyyar
bawa ne da ƙoƙarinsa na gyarawa.
A taƙaice dai, ki fara
biya a hankali tare da kowace sallar farilla ta yau da kullum, kuma ki sa rai
Allah zai karɓa tunda manufarki ita
ce tsarkake tarihin ibadarki.
Mafi yawan malamai
sun tafi akan cewa ya fi kyau mutumin da yake bin bashin farilla ya mayar da
hankali wurin biyan bashin da farko kafin ya shagaltu da nafila. Duk da hakan
ya halatta, amma kiyaye farilla shi ne fifiko a wurin Allah.
Anan nake so inyi
miki gargadi game da barin sallah ta wuceki da gangan, ko kuma yin sakaci wajen
ramasu. Wannan haramun ne domin kuwa yana daga cikin wasa da sallah. Kuma Allah
fada cewa:
فَوَيۡلٌ
لِّلۡمُصَلِّيۡنَۙ الَّذِيۡنَ هُمۡ عَنۡ صَلَاتِهِمۡ سَاهُوۡنَۙ
"tsananin azaba
ya tabbata ga masallata wadanda suke masu shagala daga sallarsu" (Surah:
Al-Maa'un, Ayat: 4-5).
Sa’ad Ibn Abi Wakkas
(RTA) ya ce: na tambayi Manzon Allah (Tsira da Amincin Allah su kara tabbata a
gareshi), a kan wadanda suke masu shagala daga sallarsu, ya ce shagala daga
sallah shi ne jinkirta lokaci, ma’ana kin yin sallah a kan lokacin har lokacin
sallar gaba ya shiga. An kirasu masallata sai dai kuma ga shi suna wulakanta
ta, tare da jinkirta ta daga lokacin ta, Allah ya yi musu alkawarin ‘WAILU’ shi
WAILU wata Tsananin Azaba ce, a wata fadar kuma an ce wani rami ne a cikin
wutar Jahannama da za a saka dukkan duwatsun duniya a cikin sa da sun narke
saboda tsananin zafin da yake cikinsa. To nan ne mazaunin masu wulakanta Sallah
ko jinkirta ta daga barin lokacinta, sai dai wanda ya tuba ya yi nadama a bisa
aikinsa na baya.
Allah ya fada cikin
Suratul Mudassir yana mai bayar da labarin ‘yan wuta cewa:
مَا
سَلَـكَكُمۡ فِىۡ سَقَرَ قَالُوۡا لَمۡ نَكُ مِنَ الۡمُصَلِّيۡنَۙ وَلَمۡ
نَكُ نُطۡعِمُ الۡمِسۡكِيۡنَۙ وَكُنَّا نَخُوۡضُ مَعَ الۡخَـآٮِٕضِيۡنَۙ وَ
كُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ الدِّيۡنِۙ حَتّٰٓى اَتٰٮنَا الۡيَقِيۡنُؕ فَمَا
تَنۡفَعُهُمۡ شَفَاعَةُ الشّٰفِعِيۡنَؕ
“me
ya shigar da ku cikin sakar? sai suka ce ‘ba mu kasance cikin masu sallah ba,
kuma ba mu zamo cikin masu ciyar da matalauta ba, kuma mun kasance muna kutsawa
tare da masu kutsawa, mun kasance muna karyata ranar sakamako har gaskiya (wato
mutuwa) ta zo mana, saboda haka, ceton mai ceton masu ceto ba zai amfane su ba!
(Suratul Mudassir aya ta 42-48).
Ubangiji mai girma da
daukaka yana cewa:
فَخَلَفَ
مِنۡۢ بَعۡدِهِمۡ خَلۡفٌ اَضَاعُوا الصَّلٰوةَ وَاتَّبَعُوا الشَّهَوٰتِ فَسَوۡفَ
يَلۡقَوۡنَ غَيًّا ۙ اِلَّا مَنۡ تَابَ وَاٰمَنَ وَعَمِلَ صَالِحًـا فَاُولٰٓٮِٕكَ
يَدۡخُلُوۡنَ الۡجَـنَّةَ وَلَا يُظۡلَمُوۡنَ شَيۡــًٔـا ۙ
"Sai wadansu yan
baya suka maye a bayansu suka tozarta sallah, kuma suka bi sha’awowinsu, to da
sannu za su haɗu da azaba, face
wanda ya tuba, kuma ya yi imani, kuma ya aikata aiki na kwarai to waɗannan za su shiga
aljanna kuma ba za a zaluncesu da komai ba." (Surah: Maryam, Ayat: 59-60).
Kiji tsoron Allah, ki
kiyaye dokokinSa. Sallah ita ce rukunin Musulunci na biyu bayan shahada, kuma
ita ce ke raba musulmi da kafiri. Ita ce mafi girman dukkan ibadodi kuma ita
za'a fara dubawa aikin ayyukanki aranar Alkiyamah. Idan tayi kyau kin tsira. Idan
kuma ta ɓaci (saboda rashin
yinta akan lokaci, ko rashin yinta da ilimi, ko rashin sanya tsoron Allah
cikinta) to mutum yayi asara mai girma. (Allah shi kiyayemu).
Wajibi ne mutumin da
ya tsinci kansa a wannan hali ya tuba zuwa ga Allah, ya kuma kiyaye lokutan
sallolinsa a kan yadda addini ya tsara.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Za ku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.