𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum. Malan Dan Allah ya halatta macen da ta haihu kwana biyar Sai jinin ya ɗauke ya halatta tayi wanka tayi sallah ko bai halattaba?
HUKUNCIN JININ
HAIHUWA IDAN YA ƊAUKE KAFIN KWANA 40
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Idan jinin haihuwa
(biki) ya ɗauke bayan kwanaki
biyar, mace za ta yi wankan tsarki kuma ta cigaba da sallah da azumi kuma
Mijinta zai iya saduwa da ita.
A bisa koyarwar
addinin Musulunci ba sai ta jira ta cika kwanaki arba'in (40) ba za ta fara
sallah. Idan alamomin tsarki sun bayyana ko da kuwa a rana ta farko ne ko ta
biyar, wanka ya wajaba a kanta. Idan har jinin ya sake dawowa a cikin kwanaki
arba'in ɗin, a lokacin ne za
ta sake dainawa ta koma hukuncin mai jego.
Akwai kuskure da mata
da yawa ke yi, suna zaton cewa Nifasi dole sai an yi kwana 40. A'a, kwana 40
shi ne Iyaka mafi yawa (Maximum), ba iyaka mafi kankanta ba.
Idan jinin ya ɗauke ko da bayan
kwana biyar ne, ko sati biyu, matukar kin ga alamar tsarki (Bushewa ko Farin
Ruwa), to kin gama Nifasi. Wanka ya hau kanki, Sallah ta hau kanki, Azumi ya
hau kanki. Sai dai idan jinin ya sake dawowa kafin kwana 40 ɗin su cika, to sai ki
daina sallah (ki koma hukuncin Nifasi).
Ummu Salama (R.A) ta
ce: "Masu biki (Nifasi) sun kasance suna zama kwanaki 40 a zamanin Annabi
(Sallallahu Alaihi Wasallam)." (Sunan Abu Dawud & Tirmidhi)
Babban Malami Imam
Tirmidhi yana cewa bayan ya kawo hadisin: "Masana daga cikin Sahabbai da
Tabi'ai sun yi Ijma'i (Haduwa) akan cewa mai biki za ta bar sallah kwana 40 ne,
sai dai idan ta ga tsarki kafin nan, to za tayi wanka tayi sallah."
A takaice idan Jini
ya dauke kafin kwanakin 40 sai kiyi Wankan tsarki Sannan kiyi Sallah. Idan kuma
Jini ya wuce kwanaki 40 sai kiyi Wankan tsarki, kiyi Sallah (ko da jinin bai ɗauke ba, wannan ya
zama Istihada/Ciwo).
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Za ku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.