𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam, ina da kitso a kaina kuma gashin yana da yawa, ga shi an daure shi sosai. Shin idan na yi Janaba (bayan saduwa), dole sai na kwance kitson nan duka kafin in yi wanka, ko kuwa zan iya wanka a haka?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
A'a, ba dole ba ne ki
kwance kitsonki domin wankan Janaba. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam)
ya saukaka wa mata a wannan ɓangaren saboda wahalar da ke cikin yawan kwancewa da
daurewa. Abin da ake bukata kawai shi ne ki tabbatar ruwa ya shiga har Gindin
Gashin (fatarkai), sannan ki kwarara ruwa a saman kitson.
Ummu Salamah (Allah
Ya kara mata yarda) ta tambayi Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) game
da wannan matsalar, ta ce: "Ya Manzon Allah! (Sallallahu Alaihi Wasallam)
Ni mace ce mai yawan gashi kuma ina yin kitso (ina daure shi). Shin zan dinga
kwance shi idan zan yi wankan Janaba?"
Sai Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce mata:
(لاَ،
إِنَّمَا يَكْفِيكِ أَنْ تَحْثِي عَلَى رَأْسِكِ ثَلاَثَ حَثَيَاتٍ ثُمَّ
تُفِيضِينَ عَلَيْكِ الْمَاءَ فَتَطْهُرِينَ)
"A'a (kada ki
kwance). Ya wadatar a gareki ki kwarara ruwa a kan ki sau uku (tare da tura
ruwan a gindin gashin ya yin da kike wankan janaba), sannan ki zuba ruwa a
dukkan jikinki, shikenan kin yi tsarki." (Sahih Muslim: 330).
IMAM AN-NAWAWI
(Rahimahullah) Yana cewa:
"Wannan hadisin
na Ummu Salamah hujja ne karara cewa ba wajibi ba ne mace ta kwance kitsonta
domin wankan Janaba... Matukar ruwa ya samu damar shiga har zuwa gindin gashin
(fatarkai) da kuma saman kitson." (Duba: Sharh Sahih Muslim)
SHEIKH IBN UTHAYMIN
(Rahimahullah) Yana cewa: "A wankan Janaba, ba a shar'anta wa mace ta
kwance gashinta ba, saboda yawan maimaituwar Janaba (saduwa tana yawan faruwa),
don haka aka saukaka mata. Amma a Wankan Haila (Gama Al'ada), wasu malaman sun ce
ya fi kyau ta kwance saboda Haila sau ɗaya take zuwa a wata, kuma ana son tsarkin ya
fi karfi." (Duba: Majmu' Fatawa Ibn Uthaymin)
Tunda ba sai kin
kwance ba, ga yadda ake yi: Ki debo ruwa a tafin hannunki, ki zuba a kan. Ki yi
amfani da yatsunki ki Tura Ruwan sosai har sai kin ji fatar kanki ta jike (wato
gindin gashin ya samu ruwa). Ki sake zuba ruwa a saman kitson gaba ɗaya (ba sai kin
warware shi don wanke cikinsa ba, matukar ruwa ya bi ta samansa da gindinsa).
Sai ki wanke sauran jikinki.
'Yar uwa, wannan
sauki ne daga Allah. Kada wahalar kitso ta sa ki dinga gujewa mijinki, ko kuma
ki yi wanka shaho-shaho (babu tura ruwa a gindi). Dole ne ruwa ya taɓa fatar kai, amma
kitso ba sai an kwance shi ba.
Allah Ya sa mu dace.
(Ku tura wa 'yan uwa
mata don su samu sauki a ibadarsu).
WALLAHU A'ALAM
Abdullahi S. Boza ✍️
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Za ku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.