Article Citation: Binta Musa Hassan (2019). Haihuwa a Al'umar Hausawa: Nazari Daga Tatsuniyoyi. DEGEL: The Journal of the Faculty of Arts and Islamic Studies, Vol. 17, No. 1. ISSN 0794-9316
HAIHUWA A AL’UMAR HAUSAWA: NAZARI DAGA TATSUNIYOYI
By
Binta Musa Hassan
Sashen Koyar da Harshen Hausa
Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi,
Kumbotso, Kano
bintamusahassan@gmail.com
Tsakure
Wannan takarda mai taken haihuwa
a al’umar Hausawa: nazari daga tatsuniyoyi.Ta
yi waiwaye ne a kan matsayi da fa’idojin haihuwa da kuma wasu al’adun haihuwa
daga tatsuniyoyin Hausa. Manufar wannan bincike ne, ƙyallaro ir-iren hidimomin
da Hausawa ske yi a duk lokacin da aka sami haihuwa. Za a kalli tatsuniyoyi na
Hausa a yi bitarsu da duk waɗansu
ayyuka masu nasaba da hakan domin daidaituwar matani. Tabbas haihuwa na da
muhimmin matsayi a rayuwar Hausa, wanda ya sa ta sami gurbi a ɗaya daga cikin adabin baka
na Bahaushe, wato tatsuniya. An gano cewa akwai al’adu masu tarin yawa da suka
shafi haihuwa a cikin tatsuniyoyi da suka haɗa da wa dai kyauta ce daga Ubangiji kuma tana ƙara wa
duk mutumin da Allah ya albarkace shi da ita kima da daraja. Duk wanda Allah Ya
ba shi ɗa, an
gama masa komai na duniya. Musamman idan ya yi wa ‘ya’yan kyakkyawar tarbiyya,
hakan ka iya zama sanadiyar shigarsa aljanna. Hausawa kuwa
mutane ne masu son haihuwa da son tara ‘ya’ya da yawa. Wasu lokutan waɗanda Allah bai ba wa haihuwa
ba, kan samu kansu cikin takaici da damuwa. Har sukan kasa yin haƙuri, sukan
yi ta yin ƙoƙari iri-iri
don ganin su ma Allah Ya ba su nasu ‘ya’yan. Takardar ta kuma yi bayani a kan
alamomin samun juna biyu. Sannan aka kalli wasu daga cikin hanyoyin da Hausawa
kan bi wajen kula da da kuma renon ‘ya’ayansu, kamar irin su goyon ciki da
wankan jego da reno da sauransu.
Gabatarwa
Al’ada tsarin
rayuwa ne da mutune suka saba yi a cikin rayuwarsu ta duniya, ta ƙunshi harkokin da suka yi ko suke yi da waɗanda suka faru
gare su na alheri da akasin haka da dukkan buƙatunsu na zaman duniya. Ciki kuwa har da fasaharsu da ƙere-ƙere da tarbiyya da horo da hani da
sauran wasu halaye da ɗabi’un kirki ko akasinsu, waɗanda ɗan Adam ke yi,
kuma al’umma ta aminta da su. Al’ada ta haɗa da nasarorin da
jama’a suka samu a shekara da shekaru domin ganin sun mallaki abubuwan da ke
kewaye da su domin biyan buƙatunsu na rayuwa.
Al’ada muhimmiyar aba ce kuma ja gaba a tafiyar harkokin yau da kullum na
rayuwar al’umma, domin ita ce rayuwar al’umma baki ɗaya, tun daga
haihuwa zuwa mutuwa. Tana kuma taimakawa matuƙa wajen warware matsalolin rayuwa da kuma samar wa al’umma ingantaccen
tsari da tsaro.
Adabi kuwa, wata hanya ce da al’umma ke
amfani da ita don bayyana al’adunta. Wato dai, ta nazarin adabin wata al’umma, mutum zai
iya samun tarihin rayuwar al’ummar. Ya gane irin ɗabi’un jama’arta da basirarsu da
yadda tunaninsu ke gudana da irin tsarin rayuwarsu, a fannonin mulki da
tattalin arziki da zamantakewa da tarbiyya da duka ɓangarorin
rayuwa tun daga haihuwa zuwa mutuwa. Adabi madubi ne da ake amfani da shi domin
a haskaka, a kuma tantance yadda al’umma ke aiwatar da al’amuranta na hikima da
fasaha a gargajiyance kamar, waƙe-waƙe da azancin
magana da wasanni da labaru da tatsuniyoyi da sauransu.
Al’ummar Hausawa suna da nau’o’in adabin baka, waɗanda suka haɗa da waƙa da zube da wasan kwaikwayo da kuma zantuttukan azanci da hikima.
Tatsuniya wadda wannan takarda za ta yi nazari a kai, ɗaya ce daga
cikin ‘ya’yan zube a adabin baka na Hausa.
Tatsuniya wata hanya ce ta dabara, wadda mata,
musamman tsofaffi da sababbin amare suke sarrafa harshe tare da ƙuƙƙula wasu maganganu na basira cikin
azanci domin isar da wani saƙo ko cimma wani buri (Muhammad,
2003: 8). Tatsuniya, tana da amfani domin a lokacin da, da ilimi da karatu ba
su samu ba a ƙasar Hausa da ita ake koyar da
tarbiyya ga yara. Tatsuniyoyi da labarai, su ne makaranta ta ‘ya‘yan Hausawa,
inda suke koyon tarbiyya ko halayen kirki da hani da miyagun halaye da kuma
dabarun zaman duniya, kamar dabarun kare kai, samun abinci da sauransu (Ɗangambo, 1984:16).
Akan iya
fahimtar tunanin al’umma da al’adunsu ta hanyar tatsuniyoyinsu. Domin a cikinta
akwai tarin abubuwa waɗanda suka shafi rayuwar al’umma. Sannan akan iya sauya tunanin al’umma
dangane da yadda ake buƙata ta zama ta fuskar adabi da
tarihi ta hanyar tatsuniyoyinsu. Don haka wannan takarda ta sa tatsuniya a gaba domin duba
hoton al’adun haihuwa a cikinta.
Haihuwa
Balarabe (1980) ya
ce, haihuwa ita ce dandamalin kusantuwar al’umma a matsayinta na dunƙulalliyar jama’a mai al’adu iri ɗaya. Bayan tsarin
aure ya tabbata, haihuwa c eke bayar da tafarkin yin tarbiyya inda ake koya wa
mazowa baya yanayin rayuwar jama’arsu su tashi da ita.
Shi kuwa Abdullahi (2008) sai ya ce,
haihuwa karuwa ce ta hanyar fitowar wani abu mai rai daga jikin wata halitta
jinsin mace wanda ya ɓoyu a wani wuri na musamman na wani ƙayyadadden lokaci sakamakon saduwar jinsin mace da
namiji.
Haihuwa tana daga
cikin tsarin matakan rayuwa guda uku, aure da haihuwa da mutuwa. Haihuwa ita ce
gaba da aure kuma baya ga mutuwa. Haihuwa ita ce mafi girman hanyar yaɗa zuriya da
yawaitar da jama’a. Kuma ta haihuwa ne al’umma kan bunƙasa ta fifita tsakanin al’umomi.
Fa’idojin Haihuwa Daga Tatsuniya
“Haihuwa maganin
mutuwa, ba don ke ba da iri ya ƙare”. Wannan na daga cikin kirarin da
Hausawa ke yi wa haihuwa. Haihuwa hanya ce muhimmiya wajen yaɗa zuri’a da
yawaita jama’a. Ta hanyar haihuwa ne kaɗai ake samun zuri’a, a samu magada.
Hausawa sukan ce, “Kyawun gida da magaji”. Ta hanyar haihuwa ce al’umma ke bunƙasa, a yawaita a duniya. Yawan jama’a kuwa a cikin al’umma abin alfahari
ne ga tattalin arziki da kuma siyasa, musamman ga Hausawa waɗanda suke da
tsarin iyali ‘mai yaɗo.’ Samuwar yara a cikin iyali martaba ne ga maigida da sauran mutanen
gida, domin taimakawar yaran ga harkokin gida, musamman wajen aikin noma da
sauran aikace-aikace da aike-aike daga wannan wuri zuwa wancan. Har Hausawa
sukan ce: “Haihuwa mai rana ko kana gudu haifi ka yar, wata rana sai ka
waiwaya”. Haihuwa kan yi ranarta a duk lokacin da mutum ya mori ɗansa ko ‘yarsa.
Misali samun taimako tatsuniyar Ɗan-ƙashin-gwiwa, ta yi nuni da haka:
Samun Taimako
“Wata rana an
yi wata mace mai yawan roƙon haihuwa. Ran nan sai wani ɗan ƙurji ya fito mata a kan gwiwarta. Sai ta ce, “Allah ka ba ni ɗa ko da na ƙashin gwiwa ne ma mana”. Shi ke nan, take sai ta ɓincine ƙurjin nan na kan gwiwarta. Sai kuwa ta ga ɗa ya fito suɓul. Sai ta yi
murna. Bayan ta gama murna, sai ta ce; “To, yau kuma ina zan sami itacen
wanka?” Sai Ɗan-ƙashin-gwiwa ya ce, “iya ba ga ni ba”. Sai kuwa ya je ya yiwo mata ita ce
mai yawa, ya kawo mata. Ta kuma cewa, “ko ina zan sami abincin da zan ci?” Sai
ya ce, “iya ba gani ba. Sai ya je gidan namun dawa ya ɗebo mata alkama da
shinkafa da dai hatsi iri-iri ya kawo mata” (Yahaya, 1972:38).
A nan haihuwa ta
yi wa Iyar Ɗan-ƙashin-gwiwa rana, domin ga shi daga haihuwarsa har ta more shi, ya samo
mata itacen wanka da abinci.
Tatsuniyar Wata Tsohuwa ta ƙara fito da fa’idar haihuwa, domin abin da ya faru ga ‘yar tsohuwa na
wahala a wajen ɗiban ruwa da tana da ɗa ko jika da shi zai samo mata ruwan
tana zaune, ya kawo mata, da ba ta sha wahalar da ta sha ba. Kamar yadda
tatsuniyar ta nuna:
“Ana nan cikin warkajamin ɗiban ruwa, sai ga
wata ‘yar tsohuwa tukuf da ita wai ita ma ta zo ɗiban ruwa. Akwai
wani abin tausayi game da wannan ‘yar tsohuwar. Watau tana da miji, amma tun da
Allah Ya halicce su, ba su taɓa haihuwa ba. Kullum sai roƙon Allah suke yi Ya ba su haihuwa tun kafin su kwanta
dama, amma ba su samu ba” (Yahaya, 1977:4).
A tatsuniyar an
nuna ita dai wannan tsohuwa tun safe ta zo ɗiban ruwan nan,
amma har magariba, kai maƙato maƙato har sai da gari ya waye ba ta samu ruwa ko da na sha
ba. Shi kuma ruwan saboda wuyarsa da ƙoƙon ƙwara ake ɗiban sa.
Adon Rayuwa
Bayan haka kuma,
haihuwa adon rayuwa ce mai bai wa mutum damar jin ya ci ribar zamansa na
duniya. Domin tana cusa
wa ɗan Adam farin ciki a rayuwa da kuma gamsuwa. Wannan dalili ne ma ya sa
Hausawa kan ce, ‘wanda ya shuri arewa, amma ya bar ‘ya’ya rasuwa ya yi, ba
mutuwa ba’. Wato ya bar na baya, waɗanda za a dinga gani ana tunawa da
shi, kuma waɗanda za su riƙa yi masa addu’a. Sannan tana kafa
tushen zumunta da ƙarfafa wanda ke tsakani da kuma
kyautata soyayya da ƙarfafa danƙon aure tsakanin ma’aurata. Domin da an yi aure, babban burin ma’aurata
da duk masoyansu shi ne samun ƙaruwa, wato zuri’a, ‘ya’ya nasu na
kansu. Saboda haka ne akan yi addu’a da cewa; ‘Allah Ya kawo ƙazantar ɗaki, amma ba ta rashin shara ba.’
Farin Ciki
Haihuwa tana sa
farin ciki da jin daɗin a rayuwa, rashinta kuma akwai sosa rai da takaici. Saboda wannan
dalili ya sa wasu matan sukan roƙi Allah cewa,
ko da bayan Ya ba su zai karɓi abinSa, to a ba su, a ce dai su ma
sun taɓa haihuwa. Tatsuniyar Reru ta
nuna:
“A wani gari mai nisan gaske, an yi
wata mace wadda ta ɗauki lokaci mai tsawo ba ta sami haihuwa ba. Wata rana suna hira tare da
wasu abokanta mata masu haihuwa suna cewa, “haihuwa tana faranta rai, lokacin
da aka haifi ɗa namiji ko ɗiya mace. Kuma rai yana ɓaci lokacin da aka rasa abin da aka
haifa. Sai wannan mata da ba ta taɓa haihuwa ba ta ce, “ ita kam ko
wanda Allah za Ya ba ta ya koma ya karɓa tana so”. (Koko, 2009: 120).
A tunanin
Hausawa ‘ya’ya maza sun fi ‘ya’ya mata, don haka idan mace ta cika haihuwar
‘ya’ya mata, ba ta haifi namiji ba, shi ma an gudu ne, ba a tsira ba. Akwai
wani karin magana da ake cewa, ‘gwamma da ku da rashinku’. Wannan yana nuni da yadda Hausawa ba su
cika son a haifa masu ‘ya’ya mata ba. Domin har kullum Hausawa, musamman maza
na ganin ɗa namiji shi ne magaji, ita kuwa ‘ya mace ‘yar gidan wani ce, domin duk daɗewar ‘ya’ya mata a
gidan iyayensu, wata rana za a aurar da su. Wasu kuwa ba sa son ‘ya’ya mata ne
saboda irin tsarabe-tsaraben da ke tattare da su, tun suna yara, har zuwa
lokacin aurensu, irin kuɗaɗen da za a riƙa kashe masu na kayan ƙyale-ƙyale a lokacin da suka zama ‘yammata da na kayan ɗaki a lokacin
aurensu. Sannan wasu na ganin ‘ya mace na iya jawo masu abin kunya, idan ba mai
kamun kai ba ce. A tatsuniyar Wata ‘Yar Sarki an nuna yadda kullum Sarki
yake ta roƙon Allah Ya ba shi ɗa namiji, amma ba
ya cewa mace:
‘An yi wani Sarki mai jama’a da yawa da kuma arziƙi. Shi dai Allah bai taɓa ba shi haihuwa
ba. Kullum yana ta roƙon Allah ya ba shi ɗa namiji. Idan ya
je masallaci bayan an ƙare salla, sai ya ba malamai kuɗi su taya shi roƙon Allah don samun ƙaruwa’ (Ɓaɓura,1986:83).
Ganin haka sai su
ma matan suka fi son haihuwar ‘ya’ya maza maimakon mata, don ko sa sami ƙarin so daga wajen mazajensu. Kuma idan mijin mai muƙamin sarauta ne, tana tunanin nan gaba ɗanta zai gaji
sarauta. Sannan kuma duk matar da ke haihuwar ‘ya’ya maza, ita ke da gida,
domin sai ta fi sauran matan samun karɓuwa a wajen maigida.
Wasu Al’adu da
Batutuwa Game da Haihuwa
A al’ummu,
fahimtar cewa mace ta sami juna-biyu kan danganta ne ga abubuwa da dama. Waɗannan alamu sun haɗa da; canzawar
kalar fata zuwa fara, da yawan zubar miyau, da sauransu. Al’adun haihuwa da aka
san Bahaushe das u sun haɗa da iccen biƙi da kayan yaji da na jiƙo da na dafa ruwa
da kuma na wanka.
Ba ma ga al’umma ba, ko ga mutum guda,
haihuwa aba ce babba. Tare dad a kasancewar ‘ya’ya wani irin adon rayuwa mai
bai wa mutum ƙarin farin ciki da annashuwa. Misali;
Son Haihuwa
Hausawa mutane ne
masu son haihuwa, kuma ba sa gajiya da ita komai yawan ‘ya’yan da suka samu,
har sai ta tsaya da kanta. An tsinkayi haka a cikin tatsuniyar Ɗan’auta da yayyensa Dodanni:
“Wata mace ce dai
ta haifi ɗanta mai kai goma. Da ta tashi sake haihuwa sai ta haifi mai kai tara. Ta
kuma sake haihuwa ta haifi mai kai takwas. Ta sake haihuwar mai kai bakwai. Ta
kuma haihuwar mai kai shida. Ta ƙara haihuwar mai
kai biyar. Sai ta haifi mai kai huɗu. Sannan ta haifi mai kai uku. Sai
kuma ta haifi mai kai biyu. Daga ƙarshe sai ta haifi
mai kai ɗaya” (Yahaya,1974:28).
Mace ɗaya tal ta haifi
‘ya’ya goma, a tsarin iyalin Hausawa na auren mata huɗu, wannan ya nuna
lallai Hausawa mutane ne masu son tara ‘ya’ya da yawa. Domin sukan sakar wa
matansu su yi ta haihuwa ba iyaka, har sai sanda Allah ya tsayar da ita. Ko da
za su haifi ‘ya’ya nawa, murna ake yi da farin ciki da yi masu ɗawainiya da kuma
barka da arziki.
A tatsuniyar Na-goma,
ma an kuma nuna: “Wata rana, an yi wani mutum wanda yake da ‘ya’ya
goma……”(Yahaya,1971:34).
Addu’a da Neman Magani
Saboda ƙaunar da Hausawa ke yi wa haihuwa, ya sa duk arziƙi ko sarauta ko muƙamin da mutum yake da shi, idan ba
shi da ‘ya’ya banza ne. Kuma irin waɗannan mutane sukan yi duk ƙoƙarin da za su iya don su sami haihuwa
domin su sami magada kuma su bar baya. Sukan bi hanyoyi da dama wajen ganin sun sami haihuwa.
Waɗansu sukan yi
addu’a ko su sa malamai su yi masu. A tatsuniyar Wata ‘Yar Sarki an nuna:
An yi wani Sarki mai jama’a da yawa da kuma
arziƙi. Shi dai Allah bai taɓa ba shi
haihuwa ba. Kullum yana ta roƙon Allah ya ba shi ɗa namiji. Idan
ya je masallaci bayan an ƙare salla, sai ya ba malamai kuɗi su taya shi
roƙon Allah don samun ƙaruwa’(Ɓaɓura,1986:83)
Wasu kuwa maganin haihuwa suke karɓa daga wajen
masu maganin gargajiya don ko sa dace da samun ‘ya’ya. Tatsuniyar Ɗan Sarki ya Zama Maciji ta nuna haka:
Wani mutum ne dai yana da matansa
uku, ya fi son biyu daga cikin matan nasa. Ɗaya ba ya son
ta sosai---. To shi dai wannan mutum ba shi da ɗa ko ‘ya ko ɗaya. Ya damu
saboda rashin ‘ya’ya. Ana nan, ranar nan, sai ya ji ana tallan maganin haihuwa.
Sai ya sayo wa matan nan guda biyu waɗanda yake so, ya ƙi sayo wa Bora (Yahaya, 1972:9
Ƙara Yin Aure Don Haihuwa
Wani lokaci kuwa wasu mazajen sukan ƙara aure ne don burin ko za su sami ƙaruwa, idan ya
zama mace ko matan da suke tare da su ba su haihu ba. Misali a tatsuniyar Wani
Sarki da Matansa an bayyana:
Wani Sarki ne
mai mata uku, amma Allah bai taɓa ba shi haihuwa ba. Ana nan, wata
rana sai ya nemi shawarar fadawansa a kan abin da ya kamata ya yi saboda wannan
rashin haihuwa. Sai suka ce ya kamata ya ƙara aure. Shi
kuwa ya ɗauki shawararsu, ya sa aka a budurwa kyakkyawa ya aure ta. Bayan‘yan
watanni sai Alllah Ya ba ta ciki”. Labari ya gama ko’ina, matar Sarki tana da
ciki (Usman, 2012: 10).
A wasu lokutan
kuwa, akan yi rashin dace, neman haihuwa kan jefa wasu cikin hallaka, musamman
mata kamar yadda ya faru ga kaza a tatsuniyar Kaza da Malam:
Wata kaza ce wadda ba ta taɓa haihuwa ba.
Kullum ba ta da wani aiki sai roƙon Allah Ya ba
ta haihuwa. Duk inda ta ji labarin wani malami ko boka sai ta yi can jiki na
rawa, amma har yanzu ba ta dace ba. Ana nan cikin wannan hali sai kaza ta ji
labarin wani shahararren malami wanda ya ƙware wajen ba
da magani kala-kala. Kaza ta ce, ban ga ta zama ba, nan take ta garzaya wajen malam. Nan dai
malam ya ce ma kaza ta je ta samo gishiri da magi da ruwa da kayan miya da duk
abin da ake haɗawa wajen dafa kaza. Bayan ta kawo masa ne, ya buge ta ta faɗa cikin wuta, ya
yi sauri ya yanka ya kai ma amaryarsa ya ce, ta haɗa masu farfesu.
(Koko, 2009:114).
A tatsuniyoyin da suka gabata, an nuna yadda Hausawa suka
ba wa haihuwa muhimmanci. Inda har waɗansu sukan yin addu’a ko su sa malamai
su yi masu don samun haihuwa. Wasu kuma maganin haihuwa suke karɓa daga wajen masu
bayar da magungunan gargajiya. Yayin da wasu mazajen sukan ga ƙara aure shi ne mafita, idan har matan da suke tare da su
ba su haihuwa.
Matsalar Haihuwa
Sanin kowa ne
Allah ne mai bayar da haihuwa ga wanda Ya so, Ya kuma hana wanda Ya so, ba
domin ya yi masa wani laifi ba. Sau da yawa malaman addini Musulunci kan faɗakar da waɗanda ba su haihu
ba cewa, hakan da Allah Ya yi masu shi ya fi dacewa da su, kuma cikin RahamarSa
akwai kyakkyawan tanadin da Ya yi masu a ranar gobe kiyama. Amma duk da haka, a
wasu lokutan Hausawa kan shiga halin damuwa da takaici, musamman idan tsufa ya
zo, ba su haihu ba.
Tatsuniyar Mai Mazare Uban Lawaya, ta nuna haka lokacin da yake ba wa ‘yar
tsohuwa labari;
Ni ne dai tun ina da mata, har na rabu
da su duk, har ga shi tsufa ya kusan kama ni Ubangiji Allah bai ba ni haihuwa
ba. Ni ko na ce, Allah Allah ka hore mini ko da ɗan ƙurji a guiwa mana wanda zan samu ɗa da shi, in ga ƙwai na a duniya...(Yahaya, 1974:55)
A mafi yawan
lokuta Hausawa sukan jingina al’amarin rashin haihuwa ga mace. Sukan yi ƙoƙarin jefa matar da ba ta haihu ba
cikin takaici da baƙin ciki. Ta hanyar tsangwamar ta da munanan
kalamai da kuma yi mata habaice-habaice da gori. Sannan irin waɗannan mata kan
fuskanci matsi daga wajen iyayen miji da ‘yan’uwansa da kishiyoyi, wani lokacin
ma har daga wajen maigidan da kuma jama’ar gari.
Tatsuniyar Juya ta Sami Gagare ta fito da irin
takaicin da matan da ba su haihu ba ke ɗanɗana, har a kan riƙa ya masu da magana da habaice-habai da kiransu da juya:
“Akwai wata mata da mijinta, ba su taɓa haihuwa ba. Sai
‘yan gaza-gani a garinsu suka shiga cewa ita juya ce ba mai haihuwa ba, irin waɗannan maganganu
kuwa sukan dame ta” (Usman, 2012:15).
Idan ita kaɗai ce matarsa,
akan matsa masa ya ƙara aure, wanda idan har kishiya ta zo
ta haihu, ai shi ke nan, sai matsi da tsanani da habaici da gori ya yi gaba. A
wasu lokutan kuma idan uwargida ta ga amarya ta zo daga baya za ta haihu, ita
kuwa ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba, sai ta ɗaga hankalinta.
Idan kuma su biyu ne, sai su haɗe wa amaryar kai, su matsa mata. Wani lokacin
ma har su yi ƙoƙarin zubar da
cikin ko kuma idan an haifi ɗan su yi ƙoƙarin nakasa shi ko kuma a nuna kishi da
baƙin ciki ƙiri-ƙiri a kan ɗan.
Tatsuniyar Ba-da-baki, tana ɗauke da wannan salo na muzguna wa matar
da ta sami juna biyu. Hakan ya fito
fili a lokacin da Ba-da-baki ke bayyana wa Sarki cewa:
“Ni ce dai Sarkin garin nan ya aure ni.
To da man yana
da matansa da ‘ya’ya. To da kishiyoyina suka ga ina da ciki sai suka sa mini
tsama. Suka dame ni. Sai na ce a raina tun da yake haka ne na daina yin magana
da kowa a gidan, sai na haihu na samu lafiya tukuna” (Yahaya, 1974:46).
Amma kuma sai
suka ci gaba da ƙulla mata makirci iri-iri ta hanyar
kashe dabbobin Sarki suna cewa ita ce, har ta kai ga sun kashe ɗan Sarki wanda
ya fi ji da shi. Duk suka ce ita
ce. Daga ƙarshe dai Sarki ya ce da fadawa su kai
ta bayan gari su kashe ta.
Tatsuniyar ‘Yammata Huɗu Masu abin Mamaki, ita ma ta nuna yadda matar Sarki ta
shiga ɗimuwa da takaici da baƙin ciki yayin da
amaryarsa ta durƙusa ta haifi ‘ya’yanta guda biyu da
mace da namiji. Ɗaya da cibiyar azurfa, ɗaya da ta zinari.
Amma da uwar ta tafi ɗauraya, sai kishiyar ta kama ‘ya’yan ta
watsa su ta bayan gida, cikin tafasa. Ta ɗebo ƙadangaru guda biyu ta zuba mata.
Sannan a
tatsuniyarWani Sarki da Matansa shi
ma an nuna yadda matan Sarki suka shiga baƙin ciki yayin da suka ji labarin amaryar Sarki ta sami juna biyu. Domin su
sun daɗe a gidan Sarki ba tare da ko ɗaya daga ciknsu ta sami ko da ɓatan wata ba. Suna
ganin cewa ta zo daga bayansu za ta gaje gida. Don haka, sai suka shiga neman
hanyar da za su bi su zubar da cikin, amma abu ya gagara, har lokacin haihuwa
ya zo. Lokacin da suka tabbatar da ta kusa haihuwa, sai suka je wurin Sarki suka
nemi izini su je shan iska da saran itace a jeji tare da bayinsu. Da fari Sarki
ya ce, ba za su je da amaryarsa mai juna biyu ba, amma da suka nace, sai ya bar
su suka tafi jeji da ita. A dajin naƙuda ta kama ta,
suka kai ta gindin bishiya, suka kwantar da ita, ta haihu. Da suka ga ta haifi
‘ya kyakkyawa, kuma ba ta cikin hayyacinta, sai suka ɗauki jaririyar
suka jefa a kan bishiya. Can da rana ta yi sanyi, sai su da bayinsu suka kama
hanyar gida, tare da mai jego. Suka gaya wa Sarki wai matarsa ta haifi wani ɗan itace ne, ba
mutum ta haifa ba (Usman, 2012:10).
Wasu kuwa ba su iya ɓoye zafin rashin
haihuwa, musamman ga ‘ya’yan kishiyoyinsu. Sukan nuna tsana da halin ko-in-kula ga ‘ya’yan.
Tatsuniyar Wasu Kishiyoyi Biyu,
tatsuniya ce da ta ƙunshi wasu kishiyoyi guda biyu ɗaya tana da ɗa ɗaya, ɗayar kuma ba ta
taɓa haihuwa ba, kuma ita ce uwargida. Dukkansu suna da randar ajiye ruwa.
Ran nan sai uwargida ta fita, sai yaron amarya ya kama kuka ruwa yake so. Ta duba randarta ashe babu ruwa, sai ta
je wajen randar uwargida ta ga ruwa, sai ta ɗiba ta ba yaronta
ya sha. Amma saboda zafin cewa, ita ba ta haihu ba, sai ta ƙeƙasa ƙasa ta ce, sai an biya ta ruwanta. Kuma ga shi ranar ba a zuwa ɗibar ruwa gulbin
garin. Ta ce kuma sai wannan ruwan take so don kawai ta ƙuntata mata. (Koko, 2009: 48).
Wani lokacin kuma
akan ɗauki ɗa a ba wa matar da ba ta haihuwa riƙo, a nan ma ba ta
tsira ba, domin za a riƙa cewa, za ta raba ɗa da mahaifiyarsa.
Ko kuma ma masu ɗan su karɓe abinsu rana tsaka. Tatsuniyar Dagaci
da Malaminsa ta fito da kyakkyawan misali:
“An yi wani dagaci a wani gari da
matarsa, to amma matar ba ta taɓa haihuwa ba. Ba tare da saninsa ba,
wata rana matar wani babban malami ta je wurin matar dagaci hira a gidansa.
Suna cikin hira sai matar dagacin ta fara ba matar malamin labarin tashin
hankalin da take ciki na rashin haihuwa. Kuma ga shi maigidanta, watau dagacin,
ya ce, yana son ya sami ‘ya’yan da za su zo su gaje shi. Kuma ya ba matar tasa
wasu ‘yan watanni, idan ba ta sami ciki ba zai kore ta, ya auro wata matar.
Wannan barazana ce fa ta sa matar dagaci ta fara kuka da baƙin ciki. Amma da matar malami ta ji yadda labarin yake,
sai ta ce, da matar dagaci, tana da ciki wata biyu, amma idan Allah Ya sauke ta
lafiya, za ta kawo wa matar dagaci abin da ta haifa, domin ta nuna wa
maigidanta cewa ta haihu. A ranar da matar malami ta haihu kuwa, kamar yadda
aka yi alƙawari sai ta ɗauki jaririnta ta
kai wa matar dagaci, ba tare da kowa ya sani ba. Matar dagaci ta ci gaba da
renon jaririn matar malam. Amma ana gobe suna sai matar malami ta dawo ta ce,
mijinta ya ce, shi ba zai ba da ɗansa ba, saboda haka a dawo masa da ɗansa. Haka dai
matar dagaci ta sha fama da roƙon matar malami da
ta rufa mata asiri, ga shi gari duk ya ɗauka cewa, ta haihu, amma ta ƙi yarda. Daga ƙarshe dai ta karɓi ɗanta ta tafi gida.
Matar dagaci ta rasa yadda za ta yi” (Usman, 2012:32).
Wannan kaɗan ne daga cikin
baƙin ciki da takaicin da waɗanda ba su haihuwa
ba ke ɗanɗana. Domin wasu sai sun gama wahala da ‘ya’yan, sannan iyayensu za su ƙwace su.
Alamomin Samun
Juna-Biyu
Akwai
alamomi da Hausawa ke amfani da su wajen gane mace ta samu juna biyu da suka ƙunshi zubar da yawu, ko amai, ko tsaginagini wajen cin
abinci, ko canza kamanni. Amma mace da ta sami juna- biyu tana gane ta ɗauki ciki ne idan
ta yi ɓatan wata. Irin waɗannan al’adu sun fito a cikin
tatsuniyoyi da dama, kamar haka :
Tatsuniyar Dagaci da Malaminsa
ta fito da wannan babbar alama ta gane mace ta sami juna-biyu. Ga abin da
tatsuniyar take cewa :
‘Bayan’yan kwanaki sai matar Dagaci ta gaya wa Dagaci
cewa ta yi ɓatan wata. Da Dagaci ya ji wannan labari, sai ya shiga murna. Ya fara faɗawa fadawansa da
mutanen gari cewa matarsa tana da juna-biyu (Usman, 2012 : 30).
Sannan yayin da aka ce mace cikinta ya girma
Hausawa sukan ɗauke mata yin ayyukan wahala don kiyaye lafiyarta da ta abin da take ɗauke da shi, duk
dai a tatsuniyar an nuna:
‘Saboda cikin,
Dagaci ya ba da umarni a kai matarsa wani gyararren gida. Ya sa a riƙa yi mata duk abin da take so. Kuma ya ce kada ta taka ko
ƙofar gida don kada ta wahala a lokacin
da take renon ciki har ranar haihuwa’ (Usman, 2012: 31).
Kula da ‘Ya’ya
Hausawa tun
‘ya’yansu suna ciki suke ɗaukan matakan kulawa da su. Akwai wasu
zaunannun al’adu da suke yi, tun daga lokacin da aka ce mace ta ɗauki ciki, har
lokacin da za ta haihu. Irin waɗannan al’adu sun haɗa da goyon ciki da
wankan jego da shayar da nono da reno da sauransu. Duka waɗannan hanyoyi ne
na kula da abin da za a haifa da kuma ita uwar.
Bisa ga al’ada, mai ciki, akasari na
fari, takan je gidansu ta haihu a can wajen iyayenta har ma ta yi wankan jego a
can. Tsawon lokacin da akan ɗauka wajen goyon ciki yakan bambanta
daga wuri zuwa wuri.
Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi
wadda ta ƙunshi labarin wani Sarki da bai taɓa samun haihuwa ba
ta fito da wannan al’ada:
‘To shi Sarkin bai taɓa haihuwa ba, duk
sanda matansa suka ɗauki ciki, sai ya zube. Ran nan bayan
‘yan shekaru da auren Marainiya da Sarki ya tara matansa, bayan ya tabbatar
kowace tana da ciki. Ya ce da su kowacce ta tafi gidan iyayenta, kuma kada ta
dawo sai ta haihu (Usman, 2012:57).
Wankan jego al’ada ce da Hausawa suka ɗauka da muhimmanci
domin sun ɗauka cewa dole ne a yi wankan jego, in har mace ba ta yi ba takan ɗanyace. Wato takan
kumbura ta yi ta fama da rashin lafiya. Dangane da tsawon lokaci da akan ɗauka wajen yin
wankan kuwa, yakan bambanta daga wuri zuwa wuri. Sai dai, ba yakan gaza kwana
arba’in ba. A waɗannan kwanaki akan yi wanka safe da yamma.
Tatsuniyar
Ba-da-Baki ta nuna yadda ta yi wankan jego. Ga abin da tatsuniyar take cewa:
‘Sai ran nan ta haifi ɗanta namiji. Ta je
ta samo itacenta na wanka ta ɗora ruwan wanka a wuta. In ya tafasa ta
kwashe ta kai ban-ɗaki ta yi wanka (Yahaya, 1974:48).
Sannan idan mai jego ta yi arba’in,
wato ta gama wankan jego takan je gidan iyaye da ‘yan’uwa yawon arba’in. A
tatsuniyar Ɗandamariye ma Yagunamu da ta haihu ta yi arba’in,
sai ta je ta ga iyayenta domin su ma su ga abin da aka haifa (Koko, 2009: 88).
A Bahaushiyar al’ada uwa ita take ba wa
jariri nononta, har sai ya kama abinci ya bari don kansa. Mata sukan shayar da
‘ya’yansu lokaci mai tsawo, domin wasu sukan kai har shekara uku kafin su yi
yaye.
Tatsuniyar Abotar Zaki da Mutum ta nuna mata
Hausawa su suke shayar da ‘ya’yansu nono: “ Idan ta sami abinci ta ci sai ta
dawo cikin kogon nan ta ba ɗanta nono ya sha”(Koko, 2009:39).
Tatsuniyar Wata
Tsohuwa da Aljana, shi ma an nuna yadda tsohuwa take shayar da ɗanta:
“Yanzu ga shi Sarkin garin ya ji
labarin haihuwarki, ya sa an zo an ɗauke miki ɗanki, amma ka
da ki ji kome. Ɗanki duk lokacin da y yi motsi zan ɗauko miki in
kawo shi gurinki ki ba shi mama” (Yahaya 1977: 6).
Sannan su dai matan suke kula da kuma renon ‘ya’ya tun
suna jarirai har zuwa girmansu. Tatsuniyar Kura
da Zomanya ta nuna:
“A can cikin wani ƙungurmin daji akwai wata zomanya mai ciki, wadda gidanta yake kusa da na
wata kura, ita ma mai juna biyu. Suna zaman lafiya da junansu irin na maƙwabta. Wata rana sai zomanya ta je wurin kura ta ce mata:
“Kin ga ni da ke mun kusa haihuwa, ya kamata mu nemi wurin da za mu rinƙa ɓoye ‘ya’yanmu”. Sai kura ta ce: “E,
gaskiya ne, to bari mu tona rami babba domin mu saka ‘ya’yanmu a ciki’ (Usman,
2012: 14).
Haka kuma a cikin
tatsuniyar ‘Yammata Huɗu Masu Abin Mamaki, nan ma an nuna yadda ɗaya daga cikin
‘yammatan da ta haifa wa Sarki ‘ya’ya biyu ta rene su: “Tana renon ‘ya’ya tana
renon ‘ya’ya har Allah Ya raya su”(Yahaya 1977: 33).
Wannan ya nuna
yadda mata ke reno da tattali da adana ‘ya’yansu.
Kammalawa
Haihuwa mai daɗi, ‘ya’ya ababen ƙauna da alfahari da tunƙaho. Waɗanda Allah Ya ba
wa Allah Ya raya masu, Ya yi masu albarka. Waɗanda kuma Allah
bai ba su ba, Allah Ya ba su, idan ba sun alheri ne a gare su. Idan kuwa akasin
haka ne, to, Allah Ya yi masu zaɓi ma fi alheri. Takardar ta yi tsokaci
ne a kan halayyar Hausawa ta son samun magada, tare da fito da hanyoyi daban-daban
da sukan bi wajen ganin sun sami magadan. Da kuma hanyoyin da sukan bi wajen
kulawa da kuma renon abin da Allah Ya ba su. Duk an yi waɗannan ne ta hanyar
nazarin tatsuniyoyin Hausa. Tabbas tatsuniyoyi madubi ne da suke haska rayuwar
al’umma gaba ɗaya.
Manazarta
Adamu, M. T. (2015). Haihuwa Da Suna a Bahaushiyar
Al’ada. Kano: Salma A’aruf Publishers.
Alhassan da Wasu (1982). Zaman Hausawa. Institute of
Education, ABU Zaria.
Ɓaɓura, S.A. (1986) “Narrator As Interpreter: Stability and Ɓariatoin in Hausa Tales”. Ph. D. Thesis. London: University of London.
Ɗangambo, A. (1984) Rabe-Raben
Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph Publishing
Company.
Ibrahim, M. S. (1982) “Dangantakar
Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa”. Kundin Digiri na
Biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya Kano: Jami’ar
Koko, H.S. (2009) Jagoran Nazarin Tatsuniya. Sakkwato: Mathi Production.
Madauci, I. da Wasu (1968) Hausa Customs. Zaria: N.N.P.C.
Muhammad, Y.M.
(2003). Adabin Baka. Zariya:ABU Press
Ltd.
Umar, M. B.
(1980). Al’adun Haihuwa a Ƙasar Hausa. Zaria: Hausa
Publications Center.
Umar, M.B. (1987) Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Garagjiya. Kano: Tofa
Commercial Press.
Usman, B. (2012) Taskar Tatsuniyoyi. Kano: Gidan Dabino
Publishers.
Yahaya, I.Y. (1971) Tatsuniyoyi da Wasanni na 1-4. Ibadan:
Oxford University Press.
Yahaya, I.Y. (1972) Tatsuniyoyi da Wasanni na 5-6. Ibadan:
Oxford University Press.
Yahaya, I.Y. (1972) “The Style and
Content of a Hausa Tale”. A cikin
Harsunan
Nijeriya Vol. II. Kano: Jami’ar Bayero.
Yahaya, I.Y. (1974) Labarun Gargajiya na 1. Ibadan: University
Press
Yahaya, I.Y. (1977) Labarun Gargajiya na 2. Ibadan:
Uniersity Press
The official website of the DEGEL Jounal is https://www.degeljournal.com

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.