Article Citation: Mu'azu Sa'adu Muhammad (2018). Ḏabi'un Dabbobi a Mahangar Bahaushe. DEGEL: The Journal of the Faculty of Arts and Islamic Studies, Vol. 16. ISSN 0794-9316
ƊABI’UN DABBOBI A
MAHANGAR BAHAUSHE
Na
Mu’azu Sa’adu Muhammad
Department
of Languages
Sule
Lamiɗo University, Kafin Hausa, Jigawa State
Tsakure
Wannan nazari zai kawo wasu bayanai, dangane
da rayuwar dabbobi a tunanin Bahaushe. Binciken kuma zai nuna yadda wannan
tunanin ya sanya Bahaushe ke alaƙanta wasu ɗabi’u,
ko halayen da aka san ɗan Adam da su, zuwa ga dabbobi. Kamar wayo, da haƙuri, da ƙarfi, da wauta, da ɓarna,
da kwaɗayi, da tsoro, da sauransu. Nazarin zai dubi wannan tunanin ne, ta mahangar
al’ada. Bayan haka, Nazarin zai dubi irin yadda hikimar Bahaushe ta bayyana a
fili ta hanyar kafa hujjoji da wasu dabbobi a matsayin misalai, tare da karesu
da wasu tubalan adabin baka. Ta hanyar fito halaye ko ɗabi’u waɗanda dabbobin sukan yi. Kamar cin abinci, da shan ruwa, da
kwanciya, da tafiya, da kuka, sai a ƙarshe
kuma naɗewa.
Gabatarwa
A
wannan muƙala za ta ƙunshi wasu bayanai, a kan irin yadda Bahaushe
ke kallo, ko ɗaukar dabbobi a tunaninsa.
Dangantakar da ke tsakaninsu ne ta haifar da Bahaushe ke alaƙanta wasu ɗabi’u,
ko halayen da a ka san ɗan Adam su zuwa ga
dabbobi. Kamar wayo, da ilmi, da haƙuri,
da ƙarfi, da ɓarna, da mugunta, da kwaɗayi, da tsoro, da faɗa, da sauransu. Za a dubi wannan tunanin ne, ta mahanga al’ada.
Tare da yin amfani da wasu rassan adabin bakan Bahaushe (Karin Magana, da waƙar baka, da tatsuniya, da take da kirari, da
al’mara da sauransu), saboda ƙara
samun hujjoji a kan nazarin.
Maƙasudin wannan nazari, shi ne ƙara fito da matsayin dabbobi a rayuwar
Bahaushe. Bayan haka, nazarin zai dubi irin yadda Bahaushe yake ɗaukar wasu ɗabi’u, waɗanda mutane ne kaɗai a ka sani da su. Duk da
haka sai ya jingina su ga wasu dabbobi na gida, ko na daji.
Fashin
baƙi
A
taken wannan nazari, akwai wasu muhimman kalmomi da suke bukatar sharhi ga mai
karatu. Wannan fasali zai yi ƙoƙarin fashin baƙin waɗannan kalmomi domin bayar
da haske.
Ma’anar ɗabi’a
Abubuwan da a ka san mutum yana yi yau da
kullum. [1] Ayyukan da mutum ya
doge yana yi yau da kullum ya zama masa jiki.[2] Hali ne
dake ƙunshe da alheri, ko
sharri. [3] Bisa la’akari da bayanai da suka gabata na masana,
muna iya cewa: kalmar ɗabi’a, wani abu ne, mai alaƙa, ko dangantaka, ko nasaba, da halayya, ko aiki,
a kan harkokin da suka shafi rayuwa ta yau da kullum. Wannan kuwa ya haɗa ne tun daga mutane, da dabbobi da tsuntsaye, a wani lokaci har da ƙwari, da tsirrai.
Ma’anar dabbobi
Kalmar dabbobi jam’i ce ta kalmar dabba,
wannan kalma baƙuwa ce, an aro ta ne
daga harshen Larabci. Ga abin da Ƙamusun
Larabci “Tajul urus”ke cewa:kamar tururuwa da sauran hallitun ƙasa mai tafiya a kan ƙasa,mai wayo da maras
wayo. Mai wayo su ne kamar mutum, maras wayo kuma su ne sauran halittu, akan
ce, “addabatun kullu man yadubbu alal ardi,” ma’ana duk wani abu
mai rai, wanda ke jan ciki ko yake tafiya a kan doron ƙasa, wanda ya haɗa har da mutum. Kuma, a cikin Alƙur’ani suratul Hud aya ta 6, Allah Ya tabbatar da wannan fassarar Kalmar,
inda yake cewa:“Wama min dabatin fil ardi illa alallahi risƙaha…. Kuma
babu wata dabba a cikin ƙasa
face ga Allah arziƙinta yake,...”
A
nan, ana nufin dukkan wani abu mai rai da ke yawo a doron ƙasa, ya haɗa da dabbobi masu ƙafa huɗu har da mutane da
tsuntsaye. Hausawa kuwa, sai suka ware mutane daban, su
kuwa masu ƙafa huɗu su
ne dabbobi. Dangane da kalmar asali da Hausawa ke kiran dabba, kafin wannan aro
kuwa, shi ne ‘bisa’, jam’i bisashe ga dabbobin gida. Na daji ana ce masu ‘namun
daji’, na ruwa kuwa ana cewa ‘naman ruwa’.
Bisa dogaro da bayanai da suka gabata, muna
iya cewa, Wannan kalma ta dabbobi, wasu halittu ne waɗanda
Allah Ya halitta su, suke rayuwa a doron ƙasa. Waɗannan halittun sun karkasu iri daban-daban, akwai masu ƙafafu huɗu, da masu biyu. Akwai dabbobin gida da suke rayuwa a gida, da dabbobin
daji waɗanda ke rayuwa a daji, sannan kuma da wasu masu rayuwa a tudu, bayan haka,
da dabbobin ruwa. Daga cikin dabbobin nan, akwai masu yawo a doron ƙasa, akwai dabbobi masu rarrafe da masu jan ciki (maja-ciki). Dabbobi masu
haihuwa (watau masu fatun kunnuwa) da dabbobi ‘ya’yan ƙwai (masu ramin kunne) da sauransu.
Danganta wasu ɗabi’u
ga dabbobi
Wannan tunani na alaƙanta wasu ɗabi’u ga dabbobi wanda Bahaushe yake da shi. Ana iya cewa
ya gaje shi ne, tun iyaye da kakanni,shi ne kuma ya yi naso har zuwa wannan
zamaninmu na yau. Bayan haka, wannan tunani bai rasa nasaba da wani ƙwarin gwiwa da ya samu daga alƙur’ani mai girma. A inda
wata aya ta nuna cewa, dabbobi da tsuntsaye wasu al’umma ne. “Kuma babu
wata dabba a cikin ƙasa, kuma babu wani
tsuntsu wanda yake hira da fukafukinsa face al’umma ne misalanku”Suratul
An’am(sura ta 6:aya 38)[4]
Bahaushe ya nazarci ɗabi’un
wasu dabbobi, na gida da daji. Haka kuma ya karkasa su gwargwadon yadda suke
gudanar da rayuwarsu ko a gida ko a dawa. Bayan wannan kuma sai ya danganta su
da wasu ɗabi’un mutane. Wannan alaƙantawar
da Bahaushe ya yi bai tsaya ga faɗa da fatar baki ba kawai.
Abin ya wuce haka, don kuwa ya yi naso a dukkan matakan adabin Bahaushe, adabin
baka har zuwa rubutacce. Wani abin mamaki shi ne, da zarar aka ambaci wata
dabba ko tsuntsu, ta gida ko ta dawa, sannan aka faɗi ɗabi’ar ko halayen ɗan Adam da aka danganta ta da shi, sai ka ga babu wata jayayya don
kuwa a zahiri abin haka yake.
Dangantakar
mutum da dabbobi ne ya sanya aka san halaye da ɗabi’un kowace dabba.
Biri
a tunanin bahaushe
Wannan
nazari zai ɗauki biri a matsayin
zakaran gwajin dafi, don ya zama abin dogaro, ko kafa hujja. Game da irin
kallon da Bahaushe ke yi wa dabbobi. Tun da farko dai Bahaushe na kallon
ko ɗaukar biri a matsayin wata dabba wayayyiya kuma mai ɓarna da rashin yarda, sannan ga ruɗu. Kaɗan daga cikin ɗabi’u, ko halayen da biri
ya yi tarayya da mutum sun haɗa da: Haƙuri, da tsabta, da kwaikwayo, da wayo, da
ilmi, da sauransu.
Wannan
irin kallo da Bahaushe ke yi wa biri shi ne ya haifar da nason biri a cikin
sassan adabin Bahaushe da dama. Daga cikin waɗannan akwai karin
maganganu masu yawa: Biri ya yi kama da mutum. Biri awakin banza, ba a cin ku
ba a sayarwa. Shegen sama kura ta ga biri. Hannun biri ba ka zama kurum.
Wannan
irin kallo bai tsaya a kan biri kawai ba, ana iya cewa kowace dabba, ko tsuntsu
da yadda Bahaushe ke kallonta, ko kuma da yadda ya ɗauketa. Kamar dabbobi masu dagi da fiƙa ya ɗauke su a matsayin mugaye,
amma kuma sai ya haɗa su da jaruntaka. Haka
kuma a cikinsu ɗin kuma sai ya ware zaki
ya ƙara masa da ƙarfi, da kwar jini da mulki. Ita kuwa kura
sai ya danganta ta da kwaɗayi, da tsoro, da ban
tsoro, da ƙwari (ƙofi). Damusa kuwa, sai ya alaƙanta da faɗa da rashin haƙuri. Giwa kuma, sai aka alaƙanta ta da ƙarfi, da haƙuri, da sauransu. Alaƙantawar
da Bahaushe ya yi wa biri da wasu ɗabi’u, bai rasa nasaba da
wasu hujjoji da ya samu daga wasu surorin Alƙur’ani:
“Kuma lalle ne, haƙiƙa,
kun san waɗanda suka ƙetere haddi daga gare ku a cikin asabar sai Muka ce masu “Ku
kasance birai ƙasƙantattu” Suratul Baƙara(sura ta 2:aya 65)
“Sa’annan
a lokacin da suka yi girman kai daga barin abin da aka hana su daga gare shi.
Muka ce musu: “ Ku kasance birai ƙasantatttu.”..
Suratul A’araf(sura ta7:aya166) [5]
Waɗannan ayoyi sun sanya Bahaushe ya ƙara ɗaukar biri a matsayin wata
dabba mafi kusanci da mutum. Ta fuskar kamannu da kuma ɗabi’u. Haka nan, akwai wata almara da ta kusantar da biri zuwa ga
mutum
Biri
da ɗabi’u wayo
“Hankali,
ko kangado, ko wayo, ko fahimta, ko basira”[6]. “Gane, ko
fahimta, ko hasashe, da tunani a kan wasu abubuwa, ana danganta wannan ga mutum
ko dabba”.[7] Bisa lura da bayanan da masana suka yi kan wannan kalma, muna iya
cewa, wayo na nufin dabara, ko basira, tare da sanin makamar al’amura in suka
taso.
Biri
Kamar
wata Karin Magana da Bahaushe ke cewa : “biri ya yi kama da mutum” Allah
ya yi wa biri wayo, saboda wayon da biri ke da shi, ya wuce duk inda ake
tunani. Domin kuwa ko a wajen haihuwa irin abubuwan da suke aikatawa ya zarce
tunanin dabbobi. Kamar yadda yake yin goyon’ya’yansa da rainon su, tare da
yadda ‘yan uwa kan taru su taya mai jego murna, da raino, har da yi wa jariri
wasa kamar yadda mutane kan yi.
Bayan
wannan biri gwani ne wajen hawa sama, babu dabbar da ta fi shi iya sama. Zaka
ga biri a kan bishiya, komai rashin kaurin reshe biri na iya hawa, ga ganganci
a kan bishiya cikin ikon Allah bai faɗowa. A inda za su taru
suna kokuwa a kan reshe ɗaya, amma ba wanda zai faɗo. Idan har ma reshe ya karye ne, sai kaga sun yi tsalle sun koma
wani reshen na daban. Bahaushe na kiran wannan kokuwa da “ruƙumar biri,” ba shakka biri na taƙama da wannan baiwa da Allah ya yi masa ƙwarewa a sama, saboda haka ne za ka iske har
wani tsalle suke yi daga wannan bishiya zuwa waccan. Biri na iya amfani da
bishiyar bakin kogi, ya tsallake ba tare da ya taka ƙasa ba. Wannan
ne ya haifar da karin magana mai cewa:“ina ruwan biri da gada ?’’.
Haka kuma idan biri ya ga hadarin ruwa da damuna, sai ya nemi wata bishiya mai
duhu, ya ɓoye kar ruwa ya jiƙa shi. Bishiya kan zama
muhallinsa, domin anan yake kwana da sauran al’amuran rayuwarsa.
i. Cin abinci: Haka kuma, biri ya yi kama da mutum, a inda
ya saɓa wa sauran dabbobi ta hanyar cin abinci, saboda biri ne kawai
yake da ɗabi’a ta cin abinci iri biyu, kamar haka; cin
abincin gaggawa da kuma na natsuwa. Idan biri na cin abinci na gaggawa, shi ne
za a ga yana cika bakinsa yana yin kumurya,( yana ɓoyewa a kumatunsa biyu hagu da dama). Da zarar ya samu natsuwa sai
ya rinƙa ci wancan ɓoyo da ya yi a bakinsa. Shi kuwa cin abinci na natsuwa a tsanake
yake yi, yana taunawa yana haɗiyewa tsaf cikin tsanaki
har yana yanga. Biri kuma, ya yi kama da mutum ta fuskar sauyi ko zaɓar abinci, biri ne kawai daga cikin dabbobi ke da abinci iri biyu
kamar haka; yana cin tsirrai da ‘ya’yan itatuwa da ganyayyakinsu, kuma ya zo ya
ci nama. A nan biri ya haɗa abincin dabbobi nau’i
biyu, maciya nama da maciya tsirrai.
ii. Shan ruwa: Wayon biri ya ƙara fitowa sarari shi ne, yadda yake yi idan
ya je bakin kogi shan ruwa. Da farko dai shi ba ya tsayawa a bakin kogin ko ya
shiga cikinsa ya sha, a ‘a sai dai ya koma gefe ya ƙwaƙula
rami a yashi ruwa ya tsatso, sannan sai ya duƙa ya sha. Biri bai yarda ya je bakin kogi inda yake yin wanka kai
tsaye ya sha ba.
Dila
da ɗabi’unsa
Dila
malamin daji kamar yadda Bahaushe ke cewa, Allah ya yi wa dila wayo, saboda
kuwa wayon da dila ke da shi, ya wuce duk inda ake tunani. Dabaru ko wayo da
dila yake da su, suna da yawa, kamar irin yadda yake shan ruwa, da kwanciya, da
yadda yake yin kuka da sauransu.
i. Shan ruwa: Dila ne kawai ba ya shan ruwa da baki, sai
dai ya tsoma jela ya haye tudu ya tsotsa. Duk wannan a dalilin rashin yardar
ne, ya sanya ba ya shan ruwa da baki. Dila in ya zo kogi, ba ya shan ruwa da
baki kamar sauran dabbobi ‘yan uwansa. Wani Makaɗin Gambara Dogo Na Abu
Kano, a waƙarsa yake cewa:
Jagora:
Duk wanda yace ba mu ba,
: Cikin maza ko
mata,
:Na goye ko
yayayye,
:Ubansa shi
dila ne ,
:Bai shan ruwa
da baki,
:Sai dai ya tsoma jela,
:Ya haye tudu ya tsotsa.”
ii. Kwanciya: Ko irin yadda dila ke kwanciya
baccinsa, yana ƙara bayyana wayonsa.
Domin shi ba ya kwanciya a sarari, sai dai a sarƙaƙiya. Haka kuma, a tsakanin busasshen ganye
yake yi, shi ma alamar wayo ne ga dila. Imam(1937).
iii. Kuka: Irin yadda dila ke yin kuka abin lura
ne. Dila ba ya yin kuka a wuri ya tsaya, sai dai da ya yi a kudu sai ya koma
yamma. Ko ya yi a gabas ya koma arewa. Haka kuma saboda tsabar wayon dila ne ya
sanya ba a kama shi da tarko. Haka kuma in ya yi kuka sai a ce shewar dila, ko
a ce guɗar dila guɗar banza. Wai don kar mafarauta su mamayeshi. Kamar yadda Audu Mai Tandu
Garu, a waƙarsa, yake cewa:
Jagora:A gaida dila sarkin dabara,dila,
:A gaida dila wayo gareka,dila,
:Idan
ya fito duba ka gane,dila,
:Idan
ya fito sai ya yi guɗa,
:Ba
za ya tsaya ba, sai ya ruga,
:Idan
ya taho kogi,ka duba,
:Sai
ya tsaya gaɓa ya duba,
:Idan
ya tsaya kuma, sai ya waiga,
:Sannan ya ciro bindi ya tsoma,
:Sannan ya haye tsauni ya tsotse,
:A gaida dila sarkin dabara,dila,
Gindi:Mu a gida mun gode Allah.
Kurege
Shi ma yana da irin nasa wayon, don haka ne
ma ya saɓa wa sauran dabbobi masu shiga rami. Shi raminsa bai yin hanya ɗaya,
sai dai ya yi hanya da yawa, da ake kira ɓuga
ko ɓula. Waɗanda yake amfani da su don a gudu ya tsirar da ransa, idan aka biyo shi.
Haka ƙurar da yakan tayar wajen gudu duk dabara ce
ta kuɓuta. Kamar
yadda Salihu Jan kiɗi yake cewa:
Jagora:Fitar
kurege rami
:Ba
tserewa yai ba
:Wata ƙura na baya.
Alh.
Musa Ɗan ƙwairo Maradun a waƙarsa ta ‘Yan Doton Tsafe cewa ya yi:
Jagora: Narega mai
gida ɗai wawa
:Sai
yai ɓulo nai can daban
:In
an ragaɗa in ficewa ta.
Dabbobi
masu hanƙuri
Haƙuri, jurewa, daurewa, [8]Haƙuri[9] Bisa dogaro da bayanai daga masana da suka gabata, muna iya cewa: wata ɗabi’a ce wadda mutum zai jure, ko daure a kan wasu al’amura ko
kuma kawar da kai game wasu da a ka yi masa. Bahaushe na alaƙanta ɗabi’ar haƙuri ga wasu dabbobi da tsuntsaye. Musamman
irin su damo, da kasa, da giwa, da dorina, da kwaɗo.
Tsuntsaye kuma, akwai agawagwa, shamuwa.
i. Damo: Bisa al’ada Bahaushe ya nazarci wasu halaye na damo, tare da
kwatantasu
da na Ɗan adam. Sannan kuma ya gwama su da na sauran
dabbobi, don tantancewa. A inda ya fifita damo a kan sauran ‘yan
uwansa, ta fuskar haƙuri, kamar a maganganun
yau da kullum akan
ce, “ai wane damo ne sarkin haƙuri”, ko “malam ka yi na damo,”
ma’ana ka yi haƙuri.
Haka mawaƙan Hausa suna amfani da
damo a
salon
siffatawa. Misali Alhaji Mamman Shata a waƙar
Sarkin Daura
Muhammadu
Bashar inda yace:
Jagora: Baba damo jikan
Audu,
:yana
kallo aka cuce shi,
:yana
kallo aka ƙware shi,
:bai ce komai ba na mai fada
:Bashari ya bar su wurin Alalh sai sun
je,
Gindi:Lafiya zaki Mamman Baban Galadima Ɗan Musa.
ii. Kasa: Ita kuma ana alaƙanta haƙuri
a gareta, saboda yawan barci da take da shi. Wannan yasa ko ka yi mata wani abu
ba zata kula ka ba, saboda tana barci saɓanin sauran macizai ‘yan
uwanta.
iii. Daurina: Dangane da daurina ita
ma Bahaushe ya jingina mata haƙuri,
saboda
duk da yake tana da girman jiki wannan bai sanya ta zama ai
faɗa ba matuƙar
ba a taɓa ‘ya’yanta ba.
iv. Giwa:bukkar daji ita ma ana alƙanta ta da haƙuri. Duk da ƙarfi da take da shi ba ruwanta da kowa, sai
an taɓa ta, sannan take faɗa.
v. Kwaɗo: Ana alaƙanta
shi da haƙuri, don yana da wuya a
samu wani da ya zargi kwaɗo da cewa ya yi masa wani
abu na cutarwa, wannan dalili ne ma ya haifar da wata magana mai cewa:“ kwaɗo ɗan Audu ba ka cizon kowa ”
Kwaikwayo
Kwaikwaya,
ko yi kwaikwayon[10]. Kwaikwaya,
ko kwakwayi, ko kwaikwayonsa, ko kwaikwayo tasa.[11] Gwada,
ko kwatanta yadda wani ke yin wani abu, kamar tafiya, ko magana, ko wata ɗabi’a don ka burge mutane.[12]koyi da abin
da wani ya yi[13] Bisa lura da bayanai da suka gabata da masana suka bayar, muna
iya cewa, wannan kalma ta kwaikwayo, na nufin duk wani aiki, ko motsi, ko sauti wanda za’a yi don a
kwatanta, ko gwada yadda wani mutum ke yin nasa, ko kuma wata ɗabi’arsa. Wannan ɗabi’a ta kwaikwayo mutane
a ka sani da ita, amma Bahaushe ya faɗaɗata zuwa ga dabbobi da tsuntsaye.
Biri
Bahaushe na danganta ɗabi’ar
kwaikwayo ga biri, saboda ya sakankance cewa babu wata dabba da ta kai biri iya
kwaikwayo na dukkan abin da ya gani ana yi. Wannan dalili ne ma ya sa Bahaushe
ke yin wasa da biri ta hanyar koya masa wasu abubuwa da zai rinƙa burge mutane, ana ba da kuɗi. Haka kuma sanin wannan yasa maharba, suke
yaudarar biri a inda suke ciro kibiya daga cikin kwari, sai su yi kamar sun
caka kibiyar a cikinsu, wanda daga baya sai su ciro wata kibiyar su harbi
birin. Shi kuma sai wuf ya cafke ta, don ya rama nan take shi ma sai caka
kibiyar a cikinsa, wanda in ba’a yi sa’a ba nan take sai ya faɗi:
Ƙarfi
“Faskara,
gagara, gundura, gawurta, ƙasaita.[14] ƙarfi, iko,iyawa, gagara[15].Bahaushe na alaƙanta ɗabi’ar ƙarfi ne ga wasu dabbobi, kamar zaki, da
karkanda, da giwa, da damusa, da doki, da gadu, da sauransu.
Babu
shakka Bahaushe na jingina ɗabi’ar ƙarfi ga wasu dabbobi, ko da yake ya kasafa su
zuwa gida uku: Akwai dabbobi masu ƙarfi
mai amfani, akwai dabbobi masu ƙarfi
banza mara amfani, da dabbobi masu ci da ƙarfi.
Dabbobi
masu ƙarfi mai amfani su ne,
kamar zaki, da giwa, da karkanda, da doki. Waɗannan dabbobi suna yin
amfani da ƙarfinsu, don kare kansu da
kuma farauta, watau neman abinci. Bisa wannan dalili ne yasa ake jingina
masu ƙarfi da haƙuri wanda yake saɓanin sauran. Alhaji Musa Ɗan ƙwairo
a waƙar Sarkin Muri Alhaji
Umaru Abba,yace:
Jagora:
Karkandan mai namijin ƙarfi
:Kowak kabra da kai
:Gabansa ya buɗe.
Gindi: Zaki, ba ja ka gaba ba,
(Sarkin Muri Uban Galadima).
Dabbobi masu ƙarfin banza kuma su ne,
masu amfani da ƙarfinsu a wani aiki mara
fa’ida. Ana jingina wannan hali ne ga gadu, domin yakan samu fili ya yi ta huɗa
da ƙahonsa. Abin lura a nan shi ne, bayan gadu ya
gama huɗar haka nan zai bar wurin ba abin da zai shuka, ba kuma wani abinci yake
nema ba. Wannan ya sa Bahaushe ya haifar da karin magana yana cewa: “Gadu mai
aikin banza.” “Gadu ƙarfi banza”.
Alhaji Amadu Ɗanmatawalle Haɗeja a waƙarsa ta gyaɗa
inda yake cewa:
Jagora: Gaya masu mugundawa,
:Shi na kaftun banza,
:Shi
ba rake ba,ba rogo ba,
:Da ma su daina shukar dusa
:ko sun gama ba za ta tsira ba.
Dangane da dabbobi masu ci-da-ƙarfi sune masu amfani da ƙarfinsu wajen farauta
kawai, sannan ba su da haƙuri. Waɗannan
su ne irinsu damusa, da wasu dangin masu ƙumba(dagi) da haƙorin fiƙa.
Ɓarna
Lalata,
ko ta’adi, ko riɓar da faɗa tsakanin dangi, almubazzaranci. [16] Ɓata ko lalata, ko gusar da ingancin, ko
amfanin abu, ko gurɓata wani abu. [17] Bisa
lura ga bayanai da masana suka yi muna iya cewa, ɓarna na nufin, lalata, ko ɓata wani abu mai amfani,
bisa kuskure ko kuma da gangar watau ana sane don mugunta.
i. Akuya: Bahaushe
ya nazarci wannan hali na ɓarna ga akuya, wannan
yasa har ya yi mata kirari da cewa: Taɓa ƙofa mai asirin sata. Jar akuya
mai kai ga yara ɓarnar.
Haka kuma Bahaushe ya lura da yanayin ɓarnar
da akuya kan yi, sannan kuma ya rarraba
ta kamar haka: Idan akuya ta
tarar da dannin kara (shinge), wanda
aka yi shi a tsaye,Sai ta sanya
ƙahonta
ta huda don ta shiga. Haka kuma,idan dannin a kwance a ka yi
shi,sai ta yi rimi (miƙe ƙafafun gabanta sama), a inda ta kan tsaya bisa
ƙafafunta
na baya, saboda ta yi ɓarna.,ta danna ƙafafunta na gaba don ta
shiga ta yi ɓarna.
Akwai misali a wani rubutaccen zube da aka samu
jirwayen ɓarnar
akuya a ciki, kamar haka:
ii. Biri ya yi
kama da mutum a wannan fuskar, saboda biri ne kawai aka
sani da ɓarna
ta ban haushi, da mamaki, da rainin wayo. Bahaushe ya
nazarci wannan halin biri, sai ya yi
masa kirari da cewa; biri mai ɓarnar
a faɗa, sannan ya lura da yanayin ɓarnar da biri kan yi, idan ya shiga
wurare daban-daban. Kamar Musa Ɗan ƙwairo
a waƙar Sarkin Daura,
yake
cewa;
Jagora:A zuba ɓarna jan biri ,
Bai ɗara bika ba ,
Tsula na nan ɗan ƙaraminsu,
To shi ma yana da karya gero.
Gindi :Babban jigo na Yari,
(Uban Shamaki tura haushi.)
A
waƙar Ali ‘Yan Doton Tsafe
Alhaji Musa Ɗan ƙwairo , yake cewa;
Jagora:
Wani ƊanSarki tsohon biri ne,
:Shi bai zama bai yi ɓarna
ba.
Gindi: Gagarau mai jiran daga,
Ali
na Magaji ci fansa.
Mugunta
Mugunta,sharri, [18] mugunta, sharri[19]. Bisa ga lura ga bayanai da masana suka yi muna iya cewa: Mugunta na nufin
aikata wani aiki don cutar da wani, ko yi masa sharri, ko yarfe. Bahaushe kan
danganta mugunta ga jaki, da ɓauna, saboda lura da wasu ɗabi’u
ko halaye da suke yi.
i. Jaki: Bahaushe
kan dangata mugunta ga jaki, saboda lura da wasu ɗabi’u
ko halaye da yake yi. Musamman idan ya so ya kayar da mutum, haka kawai sai ya
fara yin tutsu da harbi ko kawo cizo. A wani lokaci kuma sai ya goga mai
shi a jikin bango ko danni, ko kuma ya kutsa cikin wata sarkakiya ko wani
sunkuru ko ƙaya. Duka wannan Bahaushe yana
zargin jaki da cewa mugunta ce da nufi ya ke yi.
Bahaushe na zargin jaki da cewa, saboda
mugunta ne. Idan
jaki ya kayar da ubangidansa, sai ya ce
da ƙasa ta matsa, don uban
gidansa ya ji zafi. Wanda
yake saɓanin doki ne, idan doki ya
kayar da ubangidansa, sai ya ce da ƙasa ta matso sama don kar
mai
shi ya ji zafi. Sannan kuma ba zai taka shi ba, kuma ba zai
gudu gida ya bar shi ba.
ii. Ɓauna: Akan
dangata mugunta ga ɓauna, saboda lura da ɗabi’u
take da su. Musamman idan ta kyalla ido ta ga mutum, haka kawai sai ta fara
yin furjin yawu, da harbi, ko kawo cizo. A wani lokaci
kuma, ba ta yin haka sai maharbi ya harbe ta. Musamman idan ta ji kibiya
mai ta shiga jikinta ta dinga banke duk wani abu mai rai ko mara rai. Haka kuma
tana iya kutsawa cikin wata sarƙaƙiya ko wani sunƙuru ko ƙaya,
matuƙar ta ga wani motsi. Duka
wannan Bahaushe yana zargin ɓauna da cewa mugunta ce da
nufi ta ke yi. A wani lokaci kuma ko da saman bishiya maharbi ya hau to bai
tsira ba domin tana iya zuwa ƙarƙashin bishiyar ta kwanta ko kuma ta rinƙa fesa masa yawun bakinta wanda yake da ƙaiƙayin
gaske, in tsaya sosa jikinsa sai faɗo ƙasa, ita kuma ta kashe shi.
Kwaɗayi
Kwaɗai, ko kwaɗaita, ko ƙaunatar wani abu da yawa, [20] Bisa fahintar bayanan
Masana suka yi muna iya cewa, kwaɗayi na nufin yin sha'awa,
ko ƙawa na cin wani nau'in
abinci wanda ba kullum akan same sa ba. Misali, kamar abinci mai daɗi ko zaƙi kamar nama ko zuma ko
rake da sauransu. Bahaushe ya ba da wata ma'anar ga kwaɗayi, a nan yana nufin dabba ko tsuntsu mai son cin nama. Wannan ne ma yasa ake cewa kura tana da kwaɗayi.
Idan kura ta ga wata ƙaramar dabba ko mutum to
ta ga abinci, shi ya sa ake cewa kura uwar kwaɗayi.
Bahaushe
na alaƙanta ɗabi’ar kwaɗayi ga wasu dabbobi.
Musamman kura, da muzuru. Bisa wannan tsari Bahaushe ya jingina kwaɗayi ga kura fiye da duk wata dabba ta gida ko ta daji. Duk da yake
an san cewa nama ne abincin dabbobi masu dagi da fiƙa. To amma babu wanda ake kusanta shi da kwaɗayi ko ƙulafuci
kamar kura. Bisa wannan dalili ne ma ya haifar da wasu sunaye, ko kirari da aka
yiwa kura, masu bayyana ɗabi’ar kwaɗayi, da haɗama, da babakere kamar
haka: karyar dawa, ko gurgu daguyau, ko kya-ci-da-gashi.
Akwai
karin maganganu da suka shafi kwaɗayin kura: Ribar ƙafa wai kura ta taka kwaɗo. Abu namu kura da kallabin kitse. Sa a baka ya fi a rataya. Ba
girin-girin ba kai ka yi mai kura ta tsinci kalangu. Masu abu da rana suke ci,
kura ta ga saniya tana lashe ɗanta.
Tatsuniya
Ko
a tatsuniya a matsayin makwaɗaiciya kura kan fito.
Kamar tatsuniyar gizo da namun daji, a nan ma an nuna cewa:
“wai
namun daji ne suka yo ƙaura
za su sake wurin zama. Kowace dabba akwai irin kayan da ta ɗauka,
ita kura sai ta ɗauki tandu man shanu. To ashe ɗaukar
tandun mai da kura ta yi, wai wayo ta yi, don ta sha mai ne. Domin a ƙarshe ta kauce ta shiga daji da nufin zata tsuguna, ashe dai duk dabara ne
don ta sha mai”.
Waƙoƙin baka
Mawaƙan
baka su ma sun yi amfani da salon siffatawa, wajen tabbatar da kwaɗayin
kura a waƙoƙinsu
daban-daban. Misali: A wata waƙa
Alhaji Musa Ɗan ƙwairo a waƙar Sani Bello kuwa sai yace:
Jagora: Kura mai baƙin kwaɗai
:Ta shiga tarko
saboda ɗan rago,
:Saboda kwaɗanki kura,
:Ga ‘yan yara na ta jifanki,
:Da kuwwa suna ta suwwarki.
Gindi:
Sani Bello shiryayye ka ke
ka wuce a faɗa ma.
Mazuru
Shi
ma gwani ne kuma ya yi fice a fagen kwaɗayi, ko a maganganun yau
da kullum da akan ce: Mazuru cinye kaji. Tuban muzuru, amma ga kaza a baki.
Alhaji Sani Aliyu Ɗandawo
a waƙar Sarkin Yawuri Mamman
Tukur Mai martaba, cewa ya yi:
Jagora:Babban
mazuru can haka,
Sai tunbiɗar kaji yakai,
Shi bashi jin tsoron haƙo.
Sarkin
TukurBaaban Hassan
Gindi: Mamman Tukur Mai martaba,
Tsoro
Tsoro shi ne fitar hankali gare shi, da shiga
cikin wani hali na firgita da ɗimauta, da rikicewar tunani, da hankali. Idan
tsoro ya kai matuƙa, akan mutu farat ɗaya.[21] Bahaushe na alaƙanta tsoro ga wasu
dabbobi irin su kura, da barewa, da sauransu.
i. Kura: Bisa ga yadda Bahaushe ke danganta ɗabi’ar
tsoro ga kura, musamman farar kura. Ana iya cewa shi ne ya haifar da wata karin
magana mai cewa: “tsoro kamar farar kura” ko kuma “kura
ga tsoro ga ban tsoro. Bahaushe na yin amfani da wannan dalilin na
tsoro da kura ke da shi, ya ƙwaci kansa idan kura ta
rutsa shi a daji. A inda akan buga ganga, ko dai wani abu wanda zai firgita ta.
ii. Barewa: Ana alaƙanta
tsoro a gareta. Wannan a bayyane yake, saboda barewa na da matuƙar rashin yarda ko kuma ace ba ta amincewa
kowa ba. A tunanin wasu mutane suna jingina wannan da tsoro babban dalilin da
yasa ke nan barewa ba ta sakewa a duk inda take, ko da kiwo take yi da zarar ta
ji wani sauti, ko motsi, sai ta fita da gudu, hatta gudu da sbarewa ke da shi
wasu na jinginashi da tsoro.
Faɗa
Wasu
dabbobi kuwa ana iya cewa faɗa ɗabi’ar su ce, saboda su irin waɗannan dabbobi da tsuntsaye
ba ruwansu, ko da dalili ko babu, su a cikin faɗa ko shirinsa suke.
Misali; Bahaushe na danganta dage da faɗa, saboda har kirari yake
yi masa, yana cewa; “dage na Halima faɗa ranarka” ko “Ayagi mai
faɗa ko daga kwance a taɓa”.
Haka
damusa mata faɗa a inda har kirari ake mata kamar haka:
“damisa kin ƙi kallo biyu’’ko ‘’damusa
ba ki son kallon raini’’ko’’damusa ƙi
sabo’’.
Kyarkeci
ana alaƙantashi da faɗa har kirari ake masa; “kyarkeci mai wawar kora’’.
Kammalawa
A
wannan Muƙala mun ga wasu bayanai, a
kan irin yadda Bahaushe ke kallo ko matsayin da yake ɗaukar dabbobi a tunaninsa. Wannan irin matsayi ne har ya haifar da
Bahaushe ke alaƙanta wasu ɗabi’u ko halayen ɗan Adam ga dabbobi da
tsuntsaye. Kamar wayo, da ilmi, da ƙarfi,
da kwaikwayo, da ɓarna, da wauta, kwaɗayi, da faɗa da sauransu. An dubi
wannan tunanin ne, ta mahanga al’adar. Wannan mahanga ta al’ada watau wasu
hujjoji da aka samu ta fuskar duba wasu rassa na adabinsa (Karin Magana, da waƙar baka, tatsuniya, da take da kirari, da
almara da sauransu ).
Babu
shakka, an fito da wasu abubuwa a wannan muƙala an gano wasu abubuwa kamar irin shaƙuwar da ke tsakanin Bahaushe da dabbobi tun
daga na gida, har zuwa ga na daji. Haka kuma, an ƙara fito da bambancin da ke tsakanin dabbobin
su kansu, musamman ta fuskar ɗabi’a.
Manazarta
Abraham, R.C. (1947) Dictionary of the Hausa Language. London:
Hodder & Stoughton.
Bilbis M.M (2000) Makadaiciyar hanya tarihi shafi na 69.
Bunza A.M.(2006) Gadon feɗe Al’ada. Lagos: Tiwel
Ƙamusun Hausa (2006) Jami’ar Bayero Kano.
Bargery, G. P.
(1993) Hausa-English Dictionary and English-Hausa Vocabulary Ahmadu
Bello University Press Zaria.
Skinner
N(1999) Ƙamus na Turanci da Hausa..59 Northern Nigeria Publication Company, Zaria
Ingawa,
M da Wasu (1972) Ka yi ta karatu Northern Nigeria
Publication Company,
Gummi, A (1979) Alƙur’ani Mai girma tarjamar zuwa Hausa.
Ɗangambo, A. (1980) “Rabe-Raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga
Rayuwar Hausawa”, Triumph Kano.
Ɗangambo,
A. (2007)Ɗaurayar gadon feɗe waƙa sashin koyar harshen Hausa.Bayero University Kano.
Gusau, S.M. (1996) Makaɗan da Mawaƙan Hausa. Kaduna: Fisbas Media
Gusau, S.M. (1988)Waƙoƙin Makaɗan Fada:Sigoginsu Da
Yanayinsu musamman a Ƙasar
sakkwato”. Ph.D. Hausa. Bayero University Kano
Happold D.C(1973) Large Mammals of West Africa. London: Longman
Imam,
A. (1937) “Magana Jari ce” littafi na 1. Zaria: Northern Nigerian
Publication Company
Jack.W.B.(1998) Principles of Animals Communications. New York: U
Publications
Wushishi, B.J. (1998) Adabin Baka sigoginsa a Hikimominsa. M.A.
Hausa Bayero University Kano.
Yahaya, A.B.(2001)Salo asirin Waƙa, Sashen Harsunan
Nijeriya,
Usmanu Ɗanfodiyo
University Sokoto
[1] Dubi Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Vocabulary na Bargery, G. P. (1993) shf441
[2] Abdulfatah M.(2004)Alfasaha Fi
Fiƙhul Lugga Dar Al-kutub Al-limiyah Berout Lebanon
[3] Ibrahim M.(1972) Mu’ujamul Wasiɗi
1p252. Maktubatul Islamiyya Caairo Egypt
[4] Dubi Tarjamar Ƙur’ani zuwaa Harshen
Hausa na Gummi A.(1979)
[5] Abubakar Gummi (1979) Alƙur’ani Mai
girma tarjamar zuwa Hausa
[6] Skinner (1999)
Ƙamus na Turanci da Hausa. Northern Nigeria
Publication Company, Zaria.p 91
[7] Hornby.A.S(2006) Oxford Advanced
Learner’s Dictionary University Press NewYorkp776
[8] Dubi Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Vocabulary na Bargery, G. P. (1993) Ahmadu Bello
University Zaria. Shf
439
[9] Skinner N(1999) Ƙamus na Turanci da
Hausa. Northern Nigeria Publication Company, Zaria.p 124
[10]skinner (1999) Ƙamus
na Turanci da Hausa. Northern Nigeria Publication Company, Zaria.
[11] Dubi Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Vocabulary na Bargery, G. P. (1993) Ahmadu Bello University Zaria.
[12] Hornby.A.S(2006)
Oxford Advanced Learner’s Dictionary University Press NewYork.
[13] Ƙamusun Hausa na
Jami’ar Bayero Kano (2006)
[14] Dubi Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Vocabulary na Bargery, G. P. (1993) Ahmadu Bello University
Zaria. Shf 1215
[15]Skinner N(1999) Ƙamus na Turanci da Hausa. Northern
Nigeria Publication Company, Zaria.p 132
[16]Dubi Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Vocabulary na Bargery, G. P. (1993) Ahmadu Bello University
Zaria. Shf 89
[17] Encater Dictionary
[18] Dubi Hausa-English
Dictionary and English-Hausa Vocabulary na Bargery, G. P. (1993) Ahmadu Bello University
Zaria. Shf1175
[19] Skinner N(1999) Ƙamus na Turanci da
Hausa. Northern Nigeria Publication Company, Zaria.59
[20] Ƙamusun Hausa na
Jami’ar Bayero Kano (2006)
[21] Dubi Littafin Gadon feɗe Al’ada na
Bunza A.M.2006

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.