An ciro daga littafin:
FASIHIYA BINTA LABARAN
Fati Nijar Da Waƙoƙinta
Na
Abu-Ubaida Sani
Halima Daura Kabir
Abdullahi Bashir
Manazarta
Sani, A-U., Kabir, H.D., & Bashir, A. (2024). Fasihiya Binta Labaran (Fati Nijar Da Waƙoƙinta). SAS Publishers. ISBN: 978-978-795-635-7. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19513195
IN KA JI WANE... ƊAUKAKAR HAJIYA FATI NIJAR A DUNIYAR WAƘA
2.0 Shimfiɗa
Kawo tarihi
tiryan-tiryan abu ne mai matuƙar wahala
musamman idan ba a riga an kundace shi yayin da abubuwan ke faruwa ba.
Wahalarsa na ƙaruwa yayin da ya
kasance ya shafi wanda ke da ɗawainiyoyin rayuwa masu tarin yawa tare da hulɗa da
mutane daban-daban kamar dai yadda lamarin yake ga Binta Labaran. Duk da haka,
wannan babi ya yi bakin ƙoƙari wajen kalato muhimman bayanai da suka shafi ɗaukakar
Hajiya Fati a duniyar waƙa.
2.1 Fara Waƙar Fati Nijar
Waƙa ita ce sana’a ta farko da Binta Labaran ta fara. Kafin
fara waƙarta, ba ta da wata sana’a takamaimai da take yi. A maimakon haka, ta duƙufa ne kawai kan karatun addini, musamman na Alƙur’ani mai
tsarki. Rungumar sana’ar waƙa da ta yi ya zo mata da babbar riba. Domin kuwa, tuni ta
biya Haji inda ta sauke farali. Haka kuma, ta biya wa iyayenta. Ko bayan nan,
wannan sana’a ta ba
ta damar mallakar gidaje da motoci kamar yadda Bashir, da wasu (2010 p.
8) suka bayyana.
Hajiya Fati ba ta
gaji waƙa ba. Ta taso ne kawai da baiwarta. Da yake kuwa ta
kasance hanyar cin abinci gare ta, sai ta faɗa cikinta
gadan-daban. A taƙaice ke nan, ta
fara waƙa cikin yanayin da Gusau (2008) ya bayyana da ɗabi’a, wato fara
waƙa ba tare da gado a wurin wani ko naƙalta ta hanyar bin ubangida ba.
2.2 Waƙoƙinta na Farko
A farko Fati
Nijar ba waƙoƙinta na kanta
take rerawa ba. Ta fara ne da rera waƙoƙin finafinai da akan buƙaci ta tsara. Ma’ana, akan
ba ta tsari da salon da ake buƙatar waƙoƙin su kasance,
daidai da labarin fim ɗin da waƙar za ta fito a
cikinsa. Waƙar da ta fara rerawa a wannan tsari tana da suna Al’amarin
Hassan Yana Bam Mamaki.
Daga baya Hajiya
Fati ta bunƙasa sana’ar ta hanyar rera waƙoƙinta masu cin
gashin kansu. Ire-iren waƙoƙin nan takan yi su ne bisa yadda take so sannan ta
tallata su. Na farko-farko a wannan tsari su ne:
a. Girma-Girma
b. ‘Yan Matan
Arewa
Ta buɗe waƙar Girma-Girma da bayanin kanta inda take cewa:
Na yi godiya a gare ku
masoyana,
Girma girma Allahu Shi ne
mai girma,
Mu riƙe amana
da kwaikwayon halin Manzon Allah.
Ehhh Binta Labaran Mulanƙabun kuma sunana,
Fati Nijar wasu jama’ar ke
ta kira na,
Na yi jinjina gare ku
dukka masoyana,
Na gaishe ku Abubakar Sani da yayana ALA.
A cikin waɗannan
baituka biyu, ana iya ganin nason tasirin karatunta na allo. Kuma ta bayyana
sunan da aka fi sanin ta da shi kafin laƙabinta ya
dusashe shi, wato Binta Labaran. Daga bisani kuma ta bayana laƙabin da ake yi mata na Fati Nijar. Wani abin da za a ƙara tsinta a cikin waƙar shi ne, tsohuwar tarayyar zamantakewa (ta fuskar sana’a) da take da shi da Aminu Ladan Abubakar (ALA) inda har
ta kira shi da yayanta.
Ko bayan wannan,
akwai waƙoƙinta na
farko-farko da ke nuni da nason karatun Muhammadiyya da zabiyar ta mu’amalantu da shi. Daga cikin ire-iren waƙoƙin akwai waƙar Ɗan Amina
Fiyayye. A cikin waƙar tana cewa:
Amshi: Ya Rasulullah, Ya Rasulullah,
Ɗan Amina fiyayye a gai da kai manzona.
Na kirayi maƙagi na ruhu da
fuskata,
Masanin sirrina ka amsan buƙatata,
Taimako zan nema gare ka Sarkin kyauta,
Ka zama ban basira in yabo gurin manzona.
Ƙaro dubu na salati gurin manzona,
Almustafa Muhammadu Ɗaha uban Nana,
Wannan da shi na riƙa madogarar
begena,
Ɗan Aminatu gaishe ka Musɗafa
manzona.
A cikin salatin Yaa Rabbi mai girma,
Roƙo nake ka haɗa har ahalin mai girma,
Tsatso ga Faɗima Binta Zahara ‘yar mai girma,
Kamar Hassan da Hussaini ‘ya’yan manzona.
A cikin sahabu Rasulu su ma ba zan yar ba,
Domin ko sun yi rawar gani gun sa ɗan babba,
Sun taimaka wa Rasulu a dalilin Rabba,
Jinjina nai maku manya-manyan masoyana.
A yanzu zan koma in yo yabon manzona,
Domin ko shi na riƙe ya zam abin
cetona,
Ya zamo sutura a gare ni ni da dangina,
Allah ya ƙaran ƙaunar Rasulu manzona.
Ya Rasulu Manzon tsira yabonka naƙ ƙaga,
Shugaban duniya riƙe da hannun dama,
In kai riƙo a gare ni
wallahi na girma,
Ɗaha ka dafa min Almukhtari manzona.
Wata hanyar samun
kuɗi daga waƙa ga Fati Nijar
ita ce talla. Wato kamar dai sauran fitattun mawaƙa, tana iya yin waƙa domin tallata
wata haja. Wata daɗaɗɗiyar waƙar talla da Binta
Labaran ta yi ita ce ta G. Cell. Ta yi wannan waƙar a kamfanin sadarwa na G. Cell a farko-farkon shigowar kamfanin (wajen
2001). A wani baitin waƙar tana cewa:
G Cell na kowa ne an yo shi don karkara da birane,
Ga sabuwar hanyar sadarwa karkara da gari,
Ga wacce ke tace iska mai sada albishiri,
G Cell yanzu yana a jiha uku mun yi alƙawari,
Sai mun haɗe da ƙasa domin G Cell na kowane ne.
2.3 Ɗaukaka Da Ficen Fati a Fagen Waƙa
Binta Labaran na
cikin rukunin mawaƙan zamani. Masana
ba su kai matsaya a kan takamaiman sunan da
ya dace a kira nau’in waƙoƙinsu ba. Wannan ya sa ake kiran su da sunaye daban-daban.
Daga ciki akwai:
a. Waƙoƙin zamani
b. Waƙoƙin baka na zamani
c. Ruwa biyu[1]
d. Jemagun waƙoƙi
e. Waƙoƙin situdiyo
Ko ma dai yaya
abin yake, waɗannan waƙoƙi sun cancanci a
kira su na zamani. Zamani ne ya zo da su. Kayan kiɗan situdiyo ararru ne daga baƙin al’ummu, musamman
Turawa. A taƙaice ke nan, ana
iya cewa Binta Labaran mawaƙiyar zamani ce. Waƙoƙinta kuwa, ana iya kiran su ‘waƙoƙin zamani.’
Fati ta yi suna
sosai a duniyar waƙa. Sunanta ya watsu
a lungunan ƙasar Hausa. Ta kuma kasance abin kwatance da kwaikwayo
tsakanin mata matasa da dama. Yadda take gudanar da ayyukan kiɗa da waƙa tare da sauran mawaƙa na nuni ga irin zaman lafiya da lumana da ke tsakaninsu. Wani babban
misali shi ne yadda suke waƙar haɗaka (ɗani) da
waɗansu mawaƙan na daban. Daga
cikin ire-iren waƙoƙin ɗani da ta yi akwai na siyasa da kuma na ta’aziyyar Ɗanmaraya Jos.
Tarin waƙoƙin da ta yi na ƙara nuni da bunƙasar
fasaharta a fagen waƙa. Ta kasance wadda
ake girmamawa a tsakanin mawaƙa.
2.4 Ƙalubale a Cikin Gwagwarmayar Rayuwar Fati
Kamar yadda aka
bayyana a ƙarƙashin 1.2.5 da ke
sama, Fati Nijar ta fara fuskantar ƙalubalen
rayuwa ne tun lokacin ƙuruciyarta. Ƙalubale na farko shi ne mayar da ita da aka yi sha-aike
kasancewar ba ta da ƙiuya. Daga nan
kuma sai ta fara fuskantar ƙalubalen hassada
da kishi sakamakon baiwar waƙa da Allah ya ba
ta.
Wani babin ƙalubale da Fati Nijar ta fuskanta shi ne gwagwarmayar
rayuwa a Nijeriya. Ya kasance sabon muhalli a gare ta. Da taimakon Ubangiji, ta
gina sabuwar rayuwa tare da yin sababbin abokan arziki da abokan aiki.
A ɓangare ɗaya kuwa, sanannen abu ne a ƙasar Hausa cewa dukkannin mawaƙa da masu harkar
finafinai na fuskantar ƙalubalen
tsangwama da zargi. Wannan ƙalubale ya fi
yawa ga mata. Ya haɗa da kuɗin goro da ake yi musu a matsayin masu fanɗare wa
koyarwar addini da al’ada.
Tarin ƙalubale da Fati Nijar ta fuskanta bai sa ta yi ƙasa a guiwa ba. Domin kuwa, ta ci gaba da fafutukar
tabbatar da mafarkinta. Sannu a hankali har ta yi fice, ta yi suna sosai a
tsakanin mawaƙa. Har ta kai da
cewa amon sunanta ya zagaya ƙasar Hausa da
zaurukan sada zumunta a kafafen intanet.
2.5 Naɗewa
Lallai “Idan ka
ji wane ba banza ba.” Binta Labaran ta biyo waɗansu matakan rayuwa da ke tattare da zaƙaƙuranci da fasaha. Ta
sha gwagwarmayar rayuwa inda har ta baro ƙasarta ta haihuwa ɗungurungun ta dawo Nijeriya da zama. Game da ƙalubalen rayuwa da
ta fuskanta kuwa, lallai za a iya cewa kwalliya ta biya kuɗin sabulu.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.