Article Citation: Hamza A. Ainu (2018). Salon Siffantawa a cikin Waƙoƙin Addu'a na Hausa. DEGEL: The Journal of the Faculty of Arts and Islamic Studies, Vol. 16. ISSN 0794-9316
SALON SIFFANTAWA A CIKIN WAƘOƘIN ADDU’A NA HAUSA
Na
Hamza
A. Ainu, PhD
Cibiyar
Nazarin Hausa
Usman Ɗanfodiyo University, Sokoto
Tsakure
Kamar
dai sauran takwarorinsu rubutattun waƙoƙin Hausa, su ma rubutattun waƙoƙin
addu’a na Hausa ana iya samun kusan kowane irin salon sarrafa harshe na waƙa a cikinsu. Daga cikin fitattun salailai da
aka fi samu cikin waƙoƙin Hausa akwai: Salon buɗa waƙa da rufe ta da amfani da
salon aron kalmomi da sarrafa nassoshin Alƙur’ani
mai girma da na Hadisan Manzon (S.A.W) akwai kuma amfani da sunayen Allah kai
tsaye ko fassarar ma’anarsu. Ga kuma salon siffantawa wanda yake ƙunshe da salailai daban-daban kamar na
zayyana da kinaya da kamance da jinsarwa da dai sauarnsu. Wannan takarda ƙudirinta ne ta fito da bayani kan yadda salon
siffantawa ya yi kaka-gida a cikin rubutattun waƙoƙin addu’a na Hausa.
Gabatarwa
Manazarta
kan rubutattun waƙoƙin Hausa sun yi ayyuka sosai ta fuskar
taskace su da bincike-bincike kan jigoginsu da salonsu da tsarinsu da
samuwarsu. Ayyuka irin na Hiskett (1975) da Ɗalhatu (1977) da Sa’id (1978/2002/ 2016) da Yahya,
(1987/1997/2001/2016) da Birniwa (1981/1987) da Tudu (2001) da Dunfawa (2002)
da Ainu (2007) da Usman (2008) da Omar, (2010), misali ne kaɗan daga waɗannan masana, kuma
gaba ɗayansu sun yi ittifaƙi cewa tasiri rubutattun waƙoƙin
Larabci shi ne tushe ga samuwar rubutattun waƙoƙin Hausa.
Ma’anar
Salo
Ƙamusun Hausa (2006:385),
ya bayyana ma’anar salo da cewa:
" Ya
yi ko sauyi ko lawni ko fice"
Amma
a fannin nazarin adabin Hausa zan taƙaita
bayani na ra’ayoyin wasu masana adabin Hausa biyu kacal, dangane da ma’anar
salo a taƙaice. A binciken da babban
malamin nan masanin Hausa Shaihin Malami Abdulƙadir Ɗangambo
ya gudanar game da salo (2007:37-42) ya ce:
"Za
a iya fassara salo kamar haka:
i. Salo wani abu ne da ya ƙunshi
zaɓi a cikin rubutu ko furuci
ii. Salo wani ƙari
ne na daraja a cikin rubutu ko furuci, wanda ba lalle ne a same shi cikin
kowane rubutu ba.
iii. Salo ya shafi kauce wa wata daidaicciyar ƙa’ida.
iv. Salo harshen wani mutum ne.
A
tasa gudummuwar game da bayyana ma’anar salon Shaihin malami Yahya, (2016:30)
ya ce ana iya a ce:
"Salo
yana nufin duk wata dabara ko hanya a cikin waƙa wadda mawaƙi
ya bi domin ya isar da saƙon
da yake son ya isar. Ita wannan dabara ko hanya tana yi wa waƙa kwalliya ta yadda saƙon waƙar
zai isa ga mai saurare ko karatun waƙa"
A
waɗannan taƙaitattun
bayanai na masana adabin Hausa. Za a iya fahimtar cewa lalle salo babban ginshiƙi ne da yake tallabe da waƙa a lokacin da ake tsara ta da aiwatar da ita
har ma ga nazarinta da mai sauraron ta. Idan aka keɓe nazarin salon siffantawa, wannan salon yana a matsayin gishiri a
cikin ƙulla waƙa. Mai yiwuwa ne wannan ne ya sa Shaihin
malami Ɗangambo ya raba salon
siffantawa har zuwa kashi biyu.
1. Gajeriyar siffantawa
2. Doguwar siffantawa
Wannan
ya bayyana irin muhimmancin salon siffantawa wanda Shaihin malami ya sifanta
shi da cewa:
"Siffantawa,
kamar kamantawa, kwatantawa ce, sai dai ita kwatance ne na kai tsaye,
akan ɗauki darajar wani abu ko halayyarsu a ɗora wa wani kai tsaye, wato a ce, "kaza" ko kaza kaza
ne. shi ne "kaza" (Ɗangambo
1987:43-44)"
Shi
ma a nasa ƙarin hasken game da
siffantawa Shaihin malami A.B. Yahya ya kamanta wannan salo da wata irin 'baza'
ce wadda da wuya mawaƙi
zai iya shirya waƙa ba tare da amfani da
nau’o’inta ba. Ga dai sharhi da Shaihin malami ya yi a taƙaice:
"Dubi
abin da Bahaushe ke nufi da 'baza' a cikin kalaminsa. 'Da bazaar wane yake
rawa; to kamar haka ne salon siffantawa yake ga mawaƙa. shi ne bazarsu. Duk wata bugewwa, duk wata
iyawa ta isar da saƙo a cikin waƙa, duk wata fasaha a cikin waƙa, ta fi kamala idan salon siffantawa ya taka
rawa a cikin waƙa (Yahya, 2016:80)".
Waɗannan ra’ayoyin masana wata manuniya ce wanda ta wadatar ga mai
nazarin waƙa ya san matsayin salon
siffantawa a cikin waƙoƙin Hausa a gaba ɗaya da kuma rubutattunsu a keɓance.
Salon
Siffantawa
Salon
siffantawa muhimmi ne kuma babba a cikin nazarin waƙa, wanda ya ƙunshi nau’o’in salo daban-daban.
Da
yake na lura waƙoƙin addu’a sun ƙunshi nau’o’in siffantawa daban-daban zan fi
ba da ƙarfi ga ma’ana wadda ta
ayyana salon da cewa faffaɗan salo ne, saboda in
tattara hankali da bayani wuri guda. Nau’o’in salon siffantawa da ake iya samu
a cikin waƙoƙin addu’a suna da yawa. Daga ciki akwai
zayyana da alamtawa da kinaya da kamance da kuma jinsarwa.
Salon
Zayyana
Salon
zayyana, a faɗar Yahya (1997, 2001 da 2002) shi ne
wanda Ɗangambo (1981), ya kira da
sunan doguwar siffantawa. Wannan salon na nufin mawaƙi ya yi amfani da kalmomi don bayyana wani
abu, har ya kasance hoton wannan abin da yake bayani ya zo a zuciyar mai
sauraro, ya ga kamar ga abin nan yana ganin yadda ya faru. Wannan salo kan zo
cikin baiti ko baitoci da dama. Irin wannan salo za mu iya fahimtarsa kai tsaye
a cikin waƙoƙin addu’a, saboda irin mamayar da ya yi a
cikin waƙoƙin. Misali:
Ga ni yau ban da wurin zama bale kwanci na kai can,
In na ga inwa
nis so shigat ta in ga ƙaya ɗai an nan,
In na biɗo mai takasi a iske kura ta ɗai an
nan,
Ban da abokin zama gabas ga tasha ni an nan,
Ga ni shawagi ɗai nikai waɗansu
sunai min tsawa.
Dubi
kuma wadannan baitocin da ke tafe:
Na ji tsoron
zangon da nic ciyo da ƙafata
ni ɗai,
Ban da mai min jagora ka sani Allah sai kai ɗai,
Ga shi
duk ɗan guzurin da ag garan daji ya ɓassai,
Wani abu wanda ag garan shi ko na saisai,
Ga ni daji nike Rahimi tsare ni ga hyaɗen
kaiwa.
Ga
shi salkata ba ruwa cikinta ƙishi
ya kam min,
Ba gida kusa ba
rijiya bale wani mai ɗebo min,
Babu sauran ƙarfi
gare ni don gajiya ta kam min,
Babu inwa kusa ba wurin shiga yunwa ta zo min,
Rabbu sauƙaƙe
sauran wuyar da ag gaba yo min baiwa.
Ga duwatsu manya ga godabe an ce sai na bi,
Hawansu zan yi
ko dole tunda nan hanyan nan tab bi,
Can samansu
akwai sarƙaƙi zama na tcinkai gumbi,
Can ƙasan nan kuma gangaren akwai wani babban
gulbi,
Wagga hanya sai
sannu ban da damar yin gaugawa
(Umaru Sanda/Alƙali Haliru Wurno: Allah Maishin Bawa).
Waɗannan baitoci da suka gabata ko ba faɗi ba, zuciyar maikaratu ko mai sauraron wannan waƙar ta ƙiƙiro masa yanayi da
matsanaciyar wahalar da waɗannan mawaƙi yake ciki ta hanyar amfani da salon zayyana.
Haka kuma akwai
wata waƙa mai irin wannan salo
wadda ke cewa:
Masu kokuwa
duka sun shirya,
Ga shi har
fagen yi an shaya,
Ga ni ban da karfo ko laya,
Ga shi ko ina
son kayaswa.
Wasu
sun yi gayya can su ko,
Sun yi taulahi
an amsa ko,
Ni fa ga ni nan cirko-cirko,
Agajinka ɗai nika dubowa.
Ga su wane can wai sun kimtsa,
‘Yan
farofaganda sun watsa,
Duk cikin ƙasashe sun kutsa,
Wai
batunsu ɗai suka gyarawa
(Ummaru
Wazirin Gwandu: “Zaɓaɓɓiya).
Waɗannan baitoci da suka gabata suna zayyana muna yadda tura ta kai
bango ga yaƙin neman zaɓen kujerar ɗan majalisar dattawa ta
Ikko, a shekara ta 1954, wadda wannan mawaƙin
ke son a zaɓe shi wakilin Gwandu da Yawuri a cikin jihar
Kebbi yanzu. Haka kuma baitocin sun ba da hoton bayanin irin raunin da
wannan ɗan takara yake da shi a cikin sauran ‘yan
takarar wannan kujera mai muhammanci. Ba ya da wata dabara ko madogara sai
Allah (SWT). Don haka ne yake roƙonsa
da ya aiko masa da taimakonsa don ya sami nasarar wannan zaɓe.
Haka
kuma, akwai wata waƙa tasa wadda ya tsara don
addu’a mai ɗauke da irin wannan salo
na zayyana, ga ta:
In nai zamana
gida can ya bi ni,
In na hito sai
ya taso shi ja ni,
In na ƙiya sai shi dai ɗunguje
ni,
In na yi har
kwance wai don shi bar ni,
Sai in ga dai
ya yi ganwo shi ɗauka.
Ya sa kwaɗan duniya ya haƙe ni,
Ya ko tsare
ko’ina ya hwake ni,
Ya zaburo yai farat ya riƙe ni,
Ya ko matsa ya hana min sukuni,
Ƙula-uzu Billahi shaiɗanu
minka
(Ummaru Wazirin Gwandu: “Waƙar Addu’a).
Baitocin da suka gabata suna zayyana muna
irin matsalar da mawaƙin ya shiga ta yaƙi da shaiɗan, duk wata hanya da ya bi don ya guje wa makircinsa sai shaiɗan
ya ɓullo masa wata hanya ta daban. Wannan ja-in-ja da ya shiga da shaiɗan ya
tsoratar da mawaƙin don haka ne ya ga ba
wata mafita sai dai ya kai ƙararsa ga Ubangiji Allah.
Salon Alamtawa
A
wannan salon na siffantawa ana amfani ne da wani sashi na wani abu domin wannan
sashen ya tsaya a matsayin dukan abin. Ko kuma amfani da kalma mai wata ma’ana
ta daban ko bayan ma’anarta ta yau da kullum (Yahya 2006 :113). Wannan salo na
daga cikin muhimman salailan da suka fi fice a cikin waƙoƙin
addu’a. Misali dubi wannan baiti:
Allah
iyakokinka inda na ƙetare,
Zunuban da nai Rahamanu kai min gafara,
Ba wanda zai min gafara bayan ka.
(Alhaji Lawan mai Turare: “Waƙar komawa Ga Allah).
Salon alamtawa a nan shi ne a ɗango
na farko wurin da ya siffanta zunuban da ya aikata da ƙetare iyaka. Kamar dai wanda ya ƙetare
wata iyaka wadda aka shata masa, wato ya ƙarya doka. Haka kuma a cikin wannan waƙar mawaƙin
ya sake yin amfani da salon alamtawa a inda yake cewa:
Neman kadarko
wanda zan bi na tsallake,
Don kodayaushe
tausayin kaina nake,
Ɓarnar da nai da yawa cikin
gonarka.
A ɗango na ƙarshe
ne ya yi amfani da salon alamata, a inda ya siffanta laifunka da ya yi da
zunubbansa tamkar ɓarna a cikin gona.
Shi
ma wannan mawaƙi ya yi amfani da salo
irin na alamtawa a cikin wannan baiti da ke tafe:
Yanke ya dai
bai don hakanga yas shirya tun farko,
Ya yi ganiyyi
Al-mudabbirun yak ko yo kasko,
Babu mai
amshewa ga wanda duk yab ba tun farko,
Komi jinkirin
rabo zai zaka in dai kai ƙarko,
Ajizi luro da
wanda yan nufe ka da yin har barwa.
(Ummaru sanda
Sarkin Bauran Dange/Alƙali
Haliru Wurno: “Allah Ma’ishin Bawa)
Idan
aka dubi ɗango na biyu na wnanan baiti za a ga
mawallafin ya yi amfani da salon alamtawa, a wurin da ya nuna Ubangiji Allah
shi ne wanda ya halicci ganiyyi wato, mai arziki da kasko, wato talaka. Kalmar kasko a nan ita ce alamci da aka yi amfani da ita ga siffanta talaka.
Haka kuma akwai wata waƙar mai jigo shigen wannan wadda mawaƙin ya
yi amfani da salon alamtawa kamar haka.
Ya sarkin da yab ba Alu zaɓen
tafiya ƙasar kufa,
Ya sarkin da
yabba uban Isa nasara wurin yumfa,
Korena a sa
mashi ganye in ga ya tofa,
Abin ga da nib
biɗa sashi zo hannuna in ga na dafa,
Ka sa mishi aƙiba
ya Ilahi/Arshi bibarkacin salla.
(Garba Gwandu: “Dogara Ga Allah Ya Fi Zuwa
Fadanci).
A ɗango na uku ne ya yi amfani da salon
alamtawa, a wurin da ya siffanta kansa da koren itace busashe saboda rashin
samun ruwa. Haka kuma yana roƙon samun ni’ima da
wadata, wadda ya siffanta da ganyen itace lif-lif.
Salon Kinaya
Wannan wani nau’i ne na salon siffantawa
wanda Abdulƙadir Ɗangambo (1981), ya kira shi da sunan gajeruwar siffantawa. Yahya
(1997/2000/2002), ya kira shi da sunan salon kinaya. Wannan salo a fagen
nazarin waƙa na nufin mawaƙi ya kira wani abu da sunan wani abu daban. Yin haka zai sa mai sauraro
ya ɗauki ma’anar wannan abin ko siffarsa tamkar wancan abin. Shi ma wannan
salon ana samunsa a cikin waƙoƙin addu’a, mislai dubi wannan baitin.
Ga garinmu ban kwana daji,
Ga ka ban biɗar wani budoji,
Tun da na sani
kai am munji,
Malja’inka nan
nika dagewa.
(Ummaru
Wazirin Gwandu: “Zaɓaɓɓiya).
A
wannan baiti mawaƙin ya yi amfani da salon
kinaya har sau huɗu. Ya ce Ubangiji Allah
shi ne birni kuma shi ne abin dogara. Sannan mawaƙin ya ce Wanda ba Allah ba, shi ne daji, haka kuma shi ne budoji,
wato boka. A nan mawaƙin
na nufin Allah shi ne ke da kowace irin wadata wadda ɗan adam yake biɗa, haka kuma shi ne
madogra. Wanda ba shi ba shi ne daji wanda ba komi a cikinsa sai wahalhalu da
rashin tsarewa daga halaka.
Wani misali mai shigen wannan salo shi ne,
Musawwiru gaffarun waƙahharu na kirai,
Jiyamini wahabbun ka ɗamre
afolaki,
Mumitun kashe maƙiyi kashin duniya shi zam,
Ana yi shina
kallo shi zan baya auraki.
(Haliru
Wurno: “Neman Tsari Daga Maƙiyi).
A
cikin waɗannan baitoci guda biyu, mawaƙin
ya yi amfani da salon kinaya. A nan ya siffanta maƙiyinsa da nau’in jaki mai suna afolaki da
kuma wani nau’in mai suna auraki. Ya nuna cewa siffofin maƙiyansa da ayyukansa duka ɗaya suke da siffofin jakai. Ga wani misali,
Malikul-mulki
ka jirkito su duk su tsaya baya na,
Ya Hafizun ka
san haƙiƙa kai ɗai ne shinge na.
Gun ƙawiyyun nil laɓe ina
mai cin donana,
Kai ne dangali garan kuma kai ne ƙumcina
Babu mai fasa shinginga nau tsaya ka
jiya kai wawa.
(Ummaru Sanda/Alkali Haliru: “Alah
Ma’ishin Bawa).
A baitin da ya gabata kalmomin da na ja wa layi a ƙasansu, su ne waɗanda aka yi amfani da su ga salon kinaya.
Salon Kamance
Wannan babban salo na siffantawa ya kasu
kashi uku; na daidaito, na fifiko sannan da na kasawa.
Kamancen Daidaito
Wannan shi ne kamance na salo; yakan kwatanta
abin da ka riga ka sani ko wani abu wanda waƙa ke magana a kai da wani abu daban. To idan ya kawo ma hoton abin ko
halinsa ko sifarsa a gabanka sai ya ce, to, yadda ka san wannan abin haka abin
da wannan waƙa ke bayani a kai duk ɗaya
suke ta wannan fuska. Yanzu ga misalin yadda salon yakan fito a cikin waƙoƙin
addu’a. Duba wannan baiti:
Na san ban da
mai ba ni sai Jabbaru ina da shi kullum,
Kullum na biɗai shi ka ban, kuma ba ni fashi bale zalum,
Na kuma lura
shi ɗai ka bai kuma ba shi hana ba har kullum,
Na kuma farfaɗo hankalina ya koma kamar kullum,
Raina yai
fari ƙal kamar nono ban ko ji
zahi ba.
(Ummaru
wazirin Gwandu/Alhajin Mazuga: “Ginar Dutsi)
A ɗango na huɗu da na biayr na wannan
baiti da ya gabata mawaƙin
ya yi amfani da kalmomin mizani; “kamar” da “kamar”, waɗannan su ne suka bayyana cewa wannan salo ne na kamancen daidaito.
A nan ya kamanta farin cikinsa da na launi irin na nono daidai suke, haka kuma
shi ma hankalinsa da ada yake tashe, a yanzu kam ya kasance a natse kamar ba
wata damuwa da ta taɓa samunsu. Har ila yau, a
cikin wannan waƙar mawaƙin ya sake yin amfani da salon kamancen
daidaito kamar haka:
Komi taliki bai da ƙarya ta ga wanda as sarki,
Mai abu ga shi to, mib bi ƙinƙaho, mai tamkacin jaki.
A
nan ma ya kamanta ɗan Adam, wato mutum da
jaki kanka suke ga mallakar wani abu ko ma wajen biyan bukata. Kalmar “tamkaci”
ita ce mizanin mu.
Haka
kuma a wata waƙar ta addu’a an yi amfani
da salon kamace irin na daidaito, kamar haka:
Sanin haka ya
sa tutut gare ka nike ƙarata,
Tsare ni ga
manya ka tsar da ni kumyar tsarata,
Aduwaina Ƙadirun
nufarsu da yin sauna ta,
Zama sun mame ni yau da gobe suna kabra ta,
Ka maishe su tibis garan su koma tamkar ɓawa.
(Ummaru Sanda S/Bauran Dange/Alƙali Haliru Wurno: “Allah Ma’ishin Bawa”).
A wannan baiti da ya gabata mawaƙin na yin addu’a zuwa ga Allah da ya ƙarya masa ƙarfin maƙiyansa su koma tamkar yadda ƙarfin ɓawan
itace yake. Amfnai da kalmar mizani ta “tamka” ita ce ta nuna wannan salo ne
kasance daidaito ne.
Mawaƙin
wannan waƙa da ta gabata ya sake amfani da irin wannan
salo, a wurin da yake cewa:
Kiyayyan nan wadda taz zaman mini tamkar taru,
Aduwwan nawa masu yo mini tohin Baru,
Kiren ƙarya kodayaushe masu kaɗa min turu,
Tsare ni ga
sharrinsu in zamo musu tamkar guru,
Su taka su kare su bar ni ban raki don kowa.
Wannan baiti da ya gabata a ɗango
na farko da na huɗu ne, mawaƙin ya yi amfani da kalma
mizani mai nuna salon kamance irin na daidaito, a inda ya ce “tamkar”.
Haka kuma akwai irin wannan misali a
cikin wata waƙa ta addu’a mai shigen
wannan jigon, a wurin da mawaƙi ke cewa:
Hafizu ka ɗaure la’imi in ya so yi min sharri,
Sharrin duk da
yas so shi ƙulla bayyane ko cikin
sirri,
Banye ƙulle-ƙullenshi
mai san min suwa tamkacin hairi,
Koda ya rubtua
a kece hissai ma cikin tsari,
Ka daƙushe ƙoƙarin duk da yay yi na
sharri Jalla don salla.
(Garba Gwandu: “Dogara Ga Allah Ya Fi Zuwa Fadanci).
A ɗango na uku na wannan baiti mawaƙin ya yi amfnai da salon daidaito, wurin da yake cewa: “tamkacin” hairi. A
nan ya roƙi Ubangiji Allah ya musanya masa da alhairi a
duk lokacin da maƙiya suka ƙulla masa sharri. A ƙarshe ga wani misali:
Addau dini su zam kamar ba’a yo su ba,
A rasad da su su zamo kama da gubari.
(Mallam
Mahe Ƙaura-Namoda: “Waƙar Addua’a).
Duka
dai waɗannan misalai da suka gabata, kalmomin mizani ne suka yi muna
jagora ga fito da wannan salo na kamancen daidaito. Kalmomin kuwa sune “kamar”,
da “tamkacin”, “tamkar”, “kama”, da “awa” da sauransu.
Kamancen
Fifiko
Wannan
kuwa salo ne da mawaƙi ke amfnai da shi a inda
yake nuni da cewa wani abu na farko da ya kawo maka misalinsa ya fi wani abu
wanda ka riga ka sani. A cikin waƙoƙin addu’a mawaƙa kan yi amfani da wannan salo a cikin waƙoƙinsu.
Misali:
Shirin tafiya
aljanna ‘yan uwa,
Ya fi hawan
daba wajen ƙawa,
Dawaki an
shirya su sai hawa,
Ba tsoho ciki
babu tsohuwa,
Sun zan samari
masu kyan ƙawa.
(Muhammadu
Umar Kwaren-Gamba: “Waƙar
Roƙon Ruwa).
A cikin wannan baiti a ɗango
na biyu ne mawaƙin ya yi amfani da salon
kamancen fifiko ta amfani da kalmar mizani ta “fi”. Shi dai a nan yana bayani
cewa shirin da za a yi na tafiya a shiga aljanna bayan an ƙare hisabi, a ranar lahira ya fi ƙawatarwa a bisa ga yadda ake shirin hawan daba a nan duniya.
Haka ma mawaƙin ya ci gaba da yin amfani da irin wannan salon a cikin waƙarsa kamar haka:
Sai a kira mu a ƙara ce muna,
Yan mata na ciki an aje muna,
Nonna tsaitsaye sun fi tuluna,
Da shinfiɗɗu lantsan abin muna,
Ba’a ‘yan matan ba su ƙwaruwa.
Ga
kuma wani wurin da yake cewa:
Babu
abin da ka tada hankali,
Ciki muke kullum mai ta shagali,
Ga hasken shina
ta ƙyaƙyali,
Hasken ya fi
gaban na cocali,
Irin hasken har
bai misaltuwa.
A
cikin waɗannan baitoci guda biyu da suka gabata mawaƙin ya sake amfani da wannan salo na fifiko
a ɗangon da ya kamanta nonnan ‘yan matan aljanna da cewa sun fi
tululunan da muka riga muka sani waɗanda muke zuba ruwa a nan
duniya. Na biyun kuma mawallafin ya bayyana hasken waɗancan ‘yan mata na aljanna da cewa ya fi na fitilar hannu ta
cocilan. Kalmar “fi” da mawaƙin ya yi amfani da ita ita ce jagora da gane cewa wannan salo ne irin na
“fifiko”.
A wata waƙar mai kama da wannan ta addu’a mawallafinta ya yi amfani da irin wanann
salo kamar haka:
Ya fi bom ya fi
bindiga sharri,
Mai bugu shi yi
iza shi yi shuri,
Shago farta
gare shi da mari,
Har da rura garai da kirari,
Jalla tun ba mu taka ba kiyaye min shi.
(Ummaru wazirin Gwandu: “Waƙar Addu’ar Yunwar Shago”).
A wannan baiti da ya gabata tun a cikin ɗango
na farko mawaƙin ya kawo muna salon
fifiko ta amfnai da “fi” har sau biyu. Ya kamanta bugun wani ɗan dambe wai shi shago da cewa ya fi na tashin bom da ma na ita
kanta bindiga ɓarna. A nan yana
kwatanta ɓarnar waɗannan makamai ba ta kai ga
ta wannan yunwa ɓarna ba, ga rayukan ɗan Adam. Haka kuma baitin ya kamanta bugun da shago yake yi ga
abokan karawarsa, shi kuwa ya fi wannan yunwa ɓarna.
Kamancen
Kasawa
Kamar
dai wada taken sunan wannan salo ya nuna cewa na kasawa ne, a nan mawaƙi kan kwatanta abubuwa biyu, sai ya ce ɗaya bai kai ga ɗayan ba. Misali a wata waƙa wadda muka yi amfnai da ita ɗazu ga yadda mawaƙin
ya yi amfani da salon kasawa:
Ya Allah
ka ƙaro daɗin tsirarka ga Ahma komi duk,
Duk roƙon da yay yo gare ka karimi rirriɓa mai duk,
Don shi kaf fi
so kay yi kab ba shi hairinka duk duk duk,
Allahumma
sallim salaman bisa fiyayye duk,
Ahma wanda
annabawanka ba su kai kama tai ba.
(Ummaru
Wazirin Gwandu/Alhajin Mazuga: “Ginar Dutsi).
A
baitin da ya gabata a ɗango na ƙarshe ne mawaƙin ya yi amfnai da salon kamancen kasawa. A nan ya bayyana cewa
dukan Annabawa darajojinsu ba su kai na Annabi Muhammadu (SAW) ba. Kalmomin “ba su kai” su ne mizanin kamancen kasawa a wannan baiti.
Salon Jinsarwa
Salon jinsarwa a ra’ayin Yahya (2001) ko
mutumtarwa (A. Ɗangambo 1981), shi kuwa
wata dabara ce ta amfani da harshe a inda ake ɗora
wa wani jinsi halayya ko daraja ko aikin wani jinsi daban da ba na shi ba.
Saboda haka ne masana sun kasa wannan salo kashi uku: Mutumtarwa da dabbantarwa
da abuntarwa.
Mutuntarwa
Wata halayya ko daraja ta mutum da aka ɗora
wa abin da ba mutum ba, ita ce ake kira salon jinsarwa na Mutumtarwa. Ana samun wannan salo da
yawa a cikin waƙoƙin Hausa da na addu’a, misali:
Jiya gaskiya
yau ɗamre takkwana kurkuku,
Ana bata kashi
anka sa mat awartaki.
(Alƙali Haliru Wurno: Waƙar Neman Tsari Daga Maƙiyi).
A
wannan baiti mawaƙin ya yi amfani da salon
jinsarwa na Mutumtarwa da ya ce an ɗaure gaskiya har ma an
saka ta a kurkuku. A zahirin gaskiya mutum ne ake kai kurkuku a ɗaure shi. A nan ya bai wa gaskiya daraja irin ta mutane da yake ya
ce ita ma an daure ta a kurkuku. Haka ma wannan misali yake a wannan baitin:
Kowacce shina
yi ku bar shi shi yo mun gane ƙarshenta,
Kunya za shi yi
ba shi yin komi ai tun da ƙarya
ta,
Mai jagora duk don ayo fitina shi an na tammnarta,
Ci nai za ta yi har ta nemo ƙari ba shi ƙwassheta,
Ya jama’ar
Musulmi mu bar sharri shi yaf fi don salla.
(Garba Gwandu: “Dogara Ga Allah Ya Fi Zuwa Fadanci).
A ɗango na uku zuwa na huɗu nan
ne mawallafin wannan waƙa ya yi amfani da salon
Mutumtarwa a inda ya ce duk wanda ya yi jagorancin ta da fitina shi ne za ta
ci. A nan ya baiwa fitina darajar cin abinci wanda za ta ci har ta nema ƙari saboda ba ta ƙoshi ba. Ga al’ada mutum
ne ko dabba ke cin abinci har ma ya nemo ƙari idan bai ƙoshi ba, amma ga shi
mawaƙin ya ce fitina ita ma tana cin abinci.
Dabbantarwa
Mawaƙi
kan ɗauki hali ko yanayi ko daraja ko ɗabi’oi
ko aikin da dabba ce kaɗai aka sani da shi sai ya ɗora
wannan abu a kan wani mutum. Misali dubi abin da wannan mawaƙi ke cewa:
Ruwa na sunka so su dume min kai ban ga ganga ba,
Har na fara cewa Habu na Habu ban kama kowa ba,
Na yo yad dabara da duk nika yi ban gane komi ba,
Don na fafaka
ban ji duk wani reshe za shi hissan ba.
(Garba Gwandu: “Dogara Ga Allah Ya Fi Zuwa Fadanci).
A ɗango na (4) huɗu na
wannan baiti a sama mawaƙin ya dabbantar da kansa
inda ya ce ya faffaka. A zahiri tsuntsu ne aka san yana da diffike har ya yi
amfani da su ya tashi sama ya faffaka. Amma sai ga shi ya baiwa kansa daraja da
halayyar tsuntsaye. Wani misali kuma shi ne:
In yau Allah
yaz zubo ruwa,
Sai ka ga dum
mun tada kunnuwa
Maza har mata
masu haihuwa
Bale dabba dum
masu shan ruwa,
Sai murna Allahu yai ruwa.
(Malam Muhammadu Umar Kwaran-Gwamba: Waƙar Roƙon Ruwa).
A ɗango na biyu na wannan baiti da ya gabata
mawaƙi ya dabbantar da ‘yan adam (mutane) wurin da
ya nuna cewa sun tada kunnuwa. Wannan ɗabi’a
ce ta dabbobi da suke tayar da kunnuwa a lokacin da suka ga abinci tafe. A ƙarshe ga kuma wannan misali:
Shago farta
gare shi da mari,
Har da rura garai da kirari.
(Alhaji Ummaru Wazirin Gwandu: “Yunwar
Shago).
Abuntarwa
Wannan salo na nufin liƙa wa mutum hali ko ɗabi’a ko daraja ko kuma saka mutum cikin yanayi na wani
abu wanda ba dabba ba (misali dutse ko ruwa ko mota). Misalin wannan a waƙoƙin
addu’a shi ne:
Alƙahharu komi ka samu na ka san shi sarkina,
Kay yi nufin da
kat tabbata shi garan in falke in kwana,
In kuma na ji
tsoronka daidai na kai al Ilahina,
Amma na ji
tsoro ƙwarai na hirgita don
mahwalkina
Na katce ƙwarai walla na tsinke, rai bai yi daɗi ba.
(Alhaji Ummaru
Nasarawa Wazirin Gwandu/Alhajin Mazuga: “Ginar Dutsi).
Dango
na karshe mawaƙin ya liƙa wa kansa ɗabi’a irin ta igiya ko tsawo wanda shi ne ke katcewa ko tsinke wa
idan har ya ji tsauri. Sai ga shi mawallafin ya saka wa kansa wannan ɗabi’a don haka a nan ya yi amfani da wannan salon na abuntarwa.
Kammalawa
Wannan
takarda ta tattauna ne a kan wasu fitattun salailai da ake iya samu cikin waƙoƙin
addu’a na Hausa, musamman ma salon siffantawa wanda ya ƙunshi salailai da dama kamar salon zayyana da
alamtawa da kinaya da salon kamance da kashe-kashensa tare da misalan waƙoƙi
da suke tabbatar da kasancewar salon siffantawa salo ne da yake da bazaarsa ne
mawaƙa ke taka rawa.
A
nan za a taƙaita ga tattaunawa kan
salon siffantawa a cikin rubutattu waƙoƙin addu’a na Hausa, ba wai don waɗannan da aka kawo misalinsu ba su kaɗai ba
ne. Akwai ire-iren salailai da yawa da ba a taɓo ba. Don haka wannan
bincike wata matashiya ce ga masu nazari a kan rubutattun waƙoƙin
Hausa gaba ɗaya da kuma na addu’a a keɓance.
Manazarta
Ainu, H.A. (2007), " Rubutattun Waƙoƙin
Addu’a Na Hausa, Nazarin Jigoginsu Da Salailansu, Kundin Digirin Ph,D. Jami’ar
Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
CNHN (1977), Waƙa A Bakin Mai Ita I Zaria NNPC
CNHN (1977), Waƙa A Bakin Mai Ita II Zaria NNPC
C.N.H. (2007), Wa’azu Gonar Malam, Diwanin Waƙoƙin
Ummaru Nasarawa UDUS Press, Sakkwato
Ɗangambo,
A. (1980), “Hausa Wa’azi Verse From C.A. 1800-C.A. 1970 A Critical Study of
Form, Language and style:, kundin digiri Ph,D. London S.O.A.S.
Ɗangambo,
A. (1981), "Daurayar Gadon Feɗe Waƙa", Kano, Jami’ar Bayero
Ɗangambo,
A. (1984), "Rabe-raben Adabin Hausa Da Muhimmancinsa Ga Rayuwar Hausawa,
Kano Triumph.
Ɗangambo,
A. (2007), "Daurayar Gadon Feɗe Waƙa (Sabon Salo)", Amana Publishers
Limited New Kano Road, B.O. Box 1265, Zaria, Kaduna State, Nigeria.
Gusau, S.M. (1995), Dubarun Nazarin Adabin Hausa,
Kaduna FISBAS Media Services.
Ibrahim, M.A (1984), Aƙali
Halliru Wurno Da Waƙoƙinsa”, kundin digirin B.A. Sokoto, Jami’ar
Sakkwato.
Yahaya, I.Y. (1988), Hausa A Rubuce: Tarihin
Rubuce – Rubucen Cikin Hausa Zaria: NNPC.
Yahya, A.B. (1997), Jigon Nazarin Waƙa, Kaduna FISBAS Media
Services.
Yahya, A.B. (2001), "Dangantakar Waƙa Da Tarbiyyar ‘Ya’yan Hausawa", cikin
Harsunan Nijeriya, Na xix, CNHN, Jami’ar Bayero, Kano.
Yahya, A. B. (2016) Salo Asirin Waƙa (sabon bugu), Sokoto: Guaranty Printers.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.