Jagora:
Ran nan kwanan da kayyi Yauri tun
Yelwa has Sakkwato
Y/Amshi :
Dud inda mun kazo mun iske dubun
mutane,
Murna sukai ka taho
Bajini na Sarkin kudu
Gwamnan jahas Sakkwato,
Shehu Kangiwa mai niyyar riƙon gaskiya
Jagora :
Kowa addu’a ɗai yakai
Y/Amshi :
Allah ya taimakeka riƙon
duniya Alhaji,
Yayi ma tsari swahe dut
Jagora :
Wada kas samu duniya,
Allah baka lahira
Y/Amshi :
Ya zamo lahira tahi nan,
Bajini na Sarkin kudu
Gwamnan jahas Sakkwato,
Shehu Kangiwa mai niyyar riƙon
gaskiya
Jagora :
Baba kowa Allah yab ba mutane,
Komi akai yayi mai
Y/Amshi:
Ka ƙara hamdala don komi akai yayi ma,
Bajini na Sarkin kudu
Gwamnan jahas Sakkwato,
Shehu Kangiwa mai niyyar riƙon
gaskiya.
☝️☝️Suna cikin kalmomin Makaɗa Alh. Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri dake cikin waƙar da ya rerawa marigayi mai girma Alhaji Shehu Mohammed
Kangiwa Turakin Kabi, Gwamnan farar hula na farko a Tsohuwar Jihar Sakkwato
(Sakkwato da Kabi da Zanhwara, SOKEZA na yau) daga 1/10/1979 zuwa wafatinsa
ranar 17/11/1981, a waƙar da yayi masa mai turke "Gwamnan jihar Sakkwato, Shehu
Kangiwa mai niyyar riƙon gaskiya, bajini na Sarkin Kudu a farko farkon shekarar
1980.
Haƙiƙa waɗannan
kalmomi sun dace da wanda aka yiwa su saboda mutum ne na mutane mai ƙwazo
da jajircewa da karimci da kwatanta gaskiya da adalci kamar yadda rayuwarsa
kafin da bayan zamansa gwamna ta bayyana.
Ɗan Malam Muhammad Maijimada(Malam Inuwa) ɗan Malam Yakubu ɗan Malam Muhammad Mansur Muƙaddas,
an haifi Alh. Shehu Mohammed Kangiwa a garin Kangiwa hedikwatar Ƙaramar
Hukumar Mulkin Arewa a Masarautar Argungu, Jihar Kebbi ta yau a ranar
13/11/1939.
Mahaifinsa Malam Muhammad
Maijimada (Mal. Inuwa) mutumen garin Godiya ne dake Ƙaramar Hukumar Mulkin
Gwarzo, Jihar Kano. Ya ziyarci Sakkwato a lokacin mulkin mai alfarma Sarkin
Musulmi Malam Hassan ɗan
Mu'azu inda ya zarce zuwa Jega daga nan kuma ya zo Kangiwa ya kafa makarantarsa
ta Allo.
A Kangiwa ne ya auri mahaifiyar
Alh. Shehu Mohammed Kangiwa, wato Hajiya Fatima yar Malam Ahmadu wani malamin
addinin musulunci da ya taho Kangiwa
daga Ƙofar
Yanɗaka Katsina.
Mahaifin Alh. Shehu Mohammed
Kangiwa ya rasu a shekarar 1941 wannan shi ne dalilin tashinsa a hannun
yayansa, Alh. Adamu Ɗanbaba mahaifin marigayi Ambasada Sani Kangiwa.
Yayi makarantar Allo da
mahaifinsa ya bari, a tsakanin 1946 zuwa
1967, Alh. Shehu Mohammed Kangiwa yayi karatunsa na zamani na Firamare da
Elimentary da Midil da Jami'a a Kangiwa da Argungu da Sakkwato da ABU Zaria da
Lincoln Inn ta Ingila inda ya kammala digiri a fannin shari'a (Law).
Ya riƙe muƙamin
Sakatare na musamman na marigayi mai girma Firaministan Nijeriya, Alh. Sir
Abubakar Tafawa Ɓalewa, ya kuma yi aiki a hukumar jiragen ƙasa ta
Nijeriya da Kwalejin fasaha da ƙere-ƙere ta Kaduna(Kaduna Polytechnic) kafin
daga bisani ya zama babban sakatare a gwamnatin tsohuwar jihar Sakkwato inda
daga nan ne gwamnatin mulkin soja ta Nijeriya a ƙarƙashin jagorancin Janar Olusegun Obasanjo
ta naɗa shi a matsayin
Kwamishinan kula da ma'adinai da lantarki na Tarayyar Nijeriya a shekarar 1978.
Marigayi mai martaba Sarkin Kabin
Argungu, Alhaji Muhammadu Mera ya naɗa
shi Turakin Kabi (Turakin Argungu) a shekarar 1977.
Saboda kiraye - kirayen al'ummar
tsohuwar jihar Sakkwato a shekarar 1978/79, Alh. Shehu Mohammed Kangiwa ya
tsunduma a fagen siyasa, aka tsayar dashi takarar kujerar gwamna tare da
marigayi magajin garin Gusau, Dr. Garba Nadama a matsayin mataimaki a ƙarƙashin
tutar Jam'iyyar NPN, an zaɓe
su a watan Yuli na shekarar 1979 aka rantsar dasu ranar 1/10/1979.
Sun fara sanin juna shi da Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri tun suna yan matasansu a garin Argungu domin anan Argungu ne aka haifi
Alhaji Sani Aliyu Ɗandawo a shekarar 1943, suna zaune a Argungu har zuwa shekarar
1959 lokacin da mahaifin Sani Aliyu Ɗandawo wato Aliyu Ɗandawo Shuni ya tashi
daga Argungu ya koma Yauri.
Wannan tare bata yanke ba har ya
zuwa wafatin Alh. Shehu Mohammed Kangiwa a ranar 17/11 /1981 a Kaduna sanadiyar
hatsari/haɗari da ya
samu akan doki da yake ƙwallon dawaki akai.
Taren ta amfane su domin kuwa
Makaɗa Alh Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri ya zama hamshaƙin ɗan
kwangila kuma ɗan
kasuwa baya ga kiɗa da
waƙa
sanadiyar Alhaji Shehu Mohammed Kangiwa. Shi kuma Gwamna Alh. Shehu Mohammed
Kangiwa sunansa yayi amo ta hanyar yayata shi da Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo Yauri yayi a waƙoƙin da
ya yi masa. Allah SWT ya jaddada masu rahama su da sauran dukan magabatanmu ya
sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani Alfarmar Fiyayyen Halitta
Rasulallahi Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya rabbal alamin.
A wannan hoto marigayi mai girma
Gwamna Alh. Shehu Mohammed Kangiwa ne (a tsakiya) tare da mataimakinsa marigayi
Dr. Garba Namada na farko daga gefen hagu da kuma marigayi Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo
Yauri na farko daga gefen dama.
Daga Alƙalamin:
Hon.
Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin Birnin Magaji) Jihar Zamfara,
Nijeriya.
23/07/2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.