Jagora:
Hwarkon zaman Shehu cikin Gimbina
Jagora /Y/amshi :
Sai Magabci da Alkalawa,
Dag ga Alkalawa Gwandu,
Dag ga Gwandu sai Sihwawa,
Dag ga Sihwawa sai Sakkwato,
Yau rabon Usumanu da duniya,
Shekarash shi ɗari da sittin hadda biyab
bisa an masu lange,
Ta inda an kabi an dawo nan,
Abinga Allah ya mai kai dashi,
Sarauniya ta yarda a bayas,
Sardauna an miƙa maka
su dut,
Turawa saura bankwana,
Mai abin ya amshi abinai,
Turawa sai dai bankwana,
Mai abin ya amshi abinai,
Ga darajja Amadu Bello,
Da arziki na mazan jiya kayyi
Jagora :
Zak kuwat Turawa nan tudu
Jagora /Y/Amshi :
Shekara hamsin da tara,
Wurin da sun ka biyo Bidda,
Gwanga yayi hwaɗa da nasara,
Shekaras su biyab bisa daga,
Sai Kahin Ɗan Yamusa,
Magaji yayi hwaɗa da nasara,
Kwantagora garin Ibrahim,
Gwanga yayi hwaɗa da nasara,
Dag ga Zaria sai birnin Kano,
Koramaz Zorori wurin hwaɗa,
San Kano ya tarbi
nasara,
Sai Giginya an rafkewa,
Sakkwato sun yi hwaɗa da nasara,
A jama Giwa shi aƙ ƙarya,
Yara sai da rashin albarka,
Ga darajja Amadu Bello,
Da arziki na mazan jiya kayyi.
Wasu batutuwa ne☝️☝️☝️da
Makaɗa Salihu Alasan
Jankidi Rawayya wato Sarkin Taushin mai alfarma Sarkin Musulmi Alh. Sir
Abubakar III ɗan
Modibbo Usman ɗan
Sarkin Musulmi Mu'azu ɗan
Amirul muminina Muhammadu Bello ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo ya taskace wani sashe na Tarihin farkon kafuwar
Daular Usmaniyya a farkon ƙarni na 19 da yadda Turawan mulkin mallaka na Ingila suka
kassara ta a farkon ƙarni na 20, da yadda suka sake dawo da mulkin yankin Daular a
hannun jikan jagoran assassata da sunan "Yancin kai na Nijeriya" a
shekarar 1960 wato Sir Ahmadu Bello GCON KBE Sardaunan Sakkwato Firimiyan Jihar
Arewa na farko kuma na ƙarshe ɗan
Sarkin Raɓah Ibrahimu ɗan Sarkin Musulmi Abubakar
II /Mai Raɓah ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu
Bello ɗan Mujaddadi
Shehu Usman Danfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi wanda shi ne babban jagoran
Jam'iyyar NPC da ta fara kafa mulki a lokacin da su Turawan suka baiwa Tarayyar
Nijeriya Yancin kanta, a cikin waƙar da yayi masa (shi Sardauna Sir Ahmadu
Bello) mai amshi "Ga darajja Amadu Bello da arziki na mazan jiya
kayyi".
Makaɗa Salihu Alasan Jankidi Rawayya ya bayyana
wasu daga cikin wuraren da Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo ya zauna kafin da
bayan kafuwar Daula. Gimbina gari ne da Mujahidi Abdulsalam ɗan Ibrahim ya kafa bayan
tasowarsa daga ƙasar Gobir shiyoyin shekarar 1797(tsohon garin yana a cikin ƙasar
Gwadabawa ta Jihar Sakkwato ta yau) wanda a lokacin zaman Mujaddadi Shehu Usman
Danfodiyo a wurin ya kawo rashin jituwa tsakaninsu da masu mulkin Daular Gobir
har ma ana ganin shi ne musabbabin ɓarkewar
yaƙi
a tsakaninsu a shekarar 1803/1804.
Makaɗa Salihu Alasan Jankidi Rawayya ya nuna cewa
Mujaddadi ya zauna a wani wuri da ake kira Magabci ( a cikin yankin Dagawa ta ƙasar
Yabo a Jihar Sakkwato ta yau) daga nan ya ce Shehu Usmanu Danfodiyo ya zauna a
Alkalawa wato hedikwatar Daular Gobir da Sarkin Gobir Ibrahim Babari ya assasa
bayan Gobirawa sun mamaye Daular Zamfara a shiyoyin 1764/67, bayan faɗuwar wannan gari ga hannun
masu jihadin jaddada addinin musulunci na Daular Usmaniyya shiyoyin shekarar
1808.
Ya ci gaba da cewa Mujaddadi
Shehu Usman Danfodiyo ya zauna Gwandu (garin ƙanensa Malam Abdullahi Ɗanfodiyo)
dake Ƙaramar
Hukumar Mulkin Gwandun Jihar Kebbi ta yau, daga nan kuma sai Sifawa dake cikin Ƙaramar
Hukumar Mulkin Boɗinga
ta Jihar Sakkwato ta yanzu kafin daga bisani ya dawo da zama a cikin birnin
Sakkwato cibiyar Daular Usmaniyya inda ya yi wafati a shekarar 1817, Allah SWT
ya jaddada masa rahama, amin.
A cikin waɗannan batutuwa da ya ambata kamar yadda muka
kawo su a sama☝️, Makaɗin
ya bayyana yadda Turawan mulkin mallaka na Ingila suka shigo wannan yanki ta
kogin Binuwai suka zo Ida ( ta Jihar Kogi, yankin Nijeriya ta Arewa ta tsakiya)
zuwa Bida ta Jihar Neja a shiyoyin 1897, har shigowarsu Keffi da Kwantagora da
Zaria da Kano da Sakkwato da kuma irin gwabzawar da Sarakuna da al'ummar waɗannan ƙasashe
suka yi dasu a tsakanin 1897 zuwa watan Maris na shekarar 1903 a lokacin da
suka ci Cibiyar Daular Usmaniyya wato Sakkwato a filin daga na Giginya.
Bayan Sarkin Musulmi Muhammadu
Attahiru I ya bar Sakkwato a watan Maris na shekarar 1903 tare da wasu daga
cikin jama'arsa riƙe da tutar jihadin jaddada addinin musulunci na Daular
Usmaniyya, Turawan sun bishi har sai da suka kashe shi a Ɓormi/Ɓurmi
ta Ƙasar
Funakaye dake cikin Jihar Gombe, Nijeriya a cikin watan Yuli na shekarar 1903
su ka ɗauke wannan
tuta suka yi gaba da ita.
Sai gashi a shiyoyin shekarun
1958/59/60 a lokacin da suke shirye - shiryen baiwa ƙasar Nijeriya Yancin kai
sun dawo da wannan tuta wanda Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello GCON KBE ya
jagorance su zuwa wajen yayansa/wansa mai alfarma Sarkin Musulmi Alh. Sir
Abubakar III suka miƙa masa ita(wannan tutar ta na nan a fadar mai alfarma Sarkin
Musulmi dake Sakkwato).
Wato "ta inda an kabi an dawo nan, an karɓe mulkin Daular Usmaniyya a yaƙin Giginya na Sakkwato a shekarar 1903 ta hannun kisan mai alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Attahiru I, gashi a shekarar 1960 an baiwa Nijeriya yancin kai ciki kuwa har da yankin da ya ƙumshi mafi yawancin ƙasashen/garuruwan Daular Usmaniyya kuma ta hannun gwamnatin da wannan gwarzon jikan ma'assasin Daular suka kafa, "Sarauniya ta yarda a bayar, Sardauna an miƙa maka su dut, Turawa saura bankwana, mai abin ya amshi abinai".
A matsayinsa na Firimiyan Jihar
Arewa tun daga Sakkwato har Adamawa shi ne shugaba, kenan Tutocin Shehu
Mujaddadi duka suna ƙarƙashin ikonsa, Allahu Akbar! Haƙiƙa Makaɗa
Sarkin Taushi Salihu ɗan
Alasan ɗan Tigari mai
abin kiɗa ya nuna ƙwarewa
da fasihanci da zalaƙa da hikima da basira wajen taskace wani sashe na kafuwar
Daular Usmaniyya da yadda aka ɗaiɗaitar da ita da kuma yadda
gaskiya tayi halinta aka dawo da lamurran ga masu su na asali.
A wannan hoto Marigayi mai girma
Firimiyan Jihar Arewa na farko kuma na ƙarshe
Alh. Sir Ahmadu Bello GCON KBE Sardaunan Sakkwato ne.
Allah SWT ya jiƙan
magabatanmu ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani Alfarmar Fiyayyen
Halitta Rasulallahi Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya rabbal alamin.
Daga Alƙalamin:
Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin
Birnin Magaji ) Jihar Zamfara, Nijeriya.
18/07/2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.