Ticker

6/recent/ticker-posts

Jagorori Da Alkalan Gasar Rubutun Gajerun Labaran Hausa Ta Arc. Ahmad Musa Dangiwa Literary Foundation 2026

Taken gasar a wannan shekara shi ne: "Kalubale da Matsalolin Yawaitar Barace-Barace Musamman na Ƙanana Yara a Ƙasar Hausa."

📌Arc. Ahmed Musa Dangiwa, FNIA, FCIB, Jarman Kankia

Arc. Ahmed Musa Dangiwa, FNIA, FCIB, Jarman Kankia

Sunansa Arc. Ahmed Musa Dangiwa, FNIA, FCIB, Jarman Kankia shi ne Shugaba kuma Jagoran Gidauniyar Adabi ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa (Arc. Ahmed Musa Dangiwa Literary Foundation), wadda ke ɗaukar nauyin shirya Gasar Gajerun Labarai ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, domin bunƙasa adabin Hausa da ƙarfafa matasa masu baiwar rubutu.

Haifaffen Ƙaramar Hukumar Kankiya ne a Jihar Katsina, Arc. Ahmed Musa Dangiwa ƙwararren masani ne a fannin Tsara da Zanen Gine-gine (Architecture). Ya samu digirin farko da na biyu a wannan fanni daga Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ya yi fice wajen neman ilimi da ƙwarewa.

Ya fara aikinsa ne a matsayin malami a Hassan Usman Katsina Polytechnic, kafin daga bisani ya tsunduma cikin harkokin kasuwanci, inda ya yi aiki da kamfanoni daban-daban, har ya kafa nasa kamfani wanda ya samu nasarori masu yawa.

A fagen shugabanci da hidimar jama'a, Arc. Ahmed Musa Dangiwa ya riƙe manyan mukamai a matakan jiha da tarayya. Daga cikin mukaman da ya riƙa akwai Shugaban farko na Jam'iyyar APC a Jihar Katsina, Manajan Darakta na Bankin Bayar da Lamunin Gina Gidaje na Ƙasa (Federal Mortgage Bank of Nigeria), Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, sannan kuma ya rike matsayin Ministan Gidaje da Raya Birane na Tarayyar Najeriya.

Arc. Ahmed Musa Dangiwa mutum ne mai matuƙar kishin ilimi da bunƙasa matasa. Daga cikin manyan gudummawar da ya bayar akwai jagorantar kafa makarantar sakandaren al'umma ta farko a garin Kankiya, domin faɗaɗa damar samun ilimi ga matasa.

Ta fuskar tallafa wa ilimi da ci gaban al'umma, a halin yanzu yana ɗaukar nauyin karatun ɗalibai 102 a matakin digiri a Jami'ar Tarayya da ke Dutsinma, da kuma ɗalibai 50 masu karatun aikin jinya da unguwar zoma a Kwalejin Horar da Ma'aikatan Jinya ta Dan Sharif da ke Kano. Haka kuma, ya ɗauki nauyin horas da matasa maza da mata sama da 500 sana'o'i daban-daban, tare da ba su kayan aikin fara sana'a da jari domin su dogara da kansu.

Ta hanyar Gidauniyar Adabinsa, Arc. Ahmed Musa Dangiwa ya nuna irin ƙudirinsa na bunƙasa adabin Hausa da ƙarfafa matasa marubuta ta hanyar gasar rubuce-rubuce, tallafawa masu basira, da samar da damarmakin da za su taimaka wajen haɓaka ilimi da al'adun Hausawa.

Arc. Ahmed Musa Dangiwa jagora ne mai hangen nesa, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimar jama'a, inganta ilimi, ƙarfafa matasa, da samar da ingantacciyar makoma ga al'umma.

📌Dr. Abdulrahman Aliyu

Dr. Abdulrahman Aliyu

Sunansa Dr. Abdulrahman Aliyu,  manazarci ne, marubuci, kuma mai bincike a fannin Nazarin Hausa. Ya kammala digirin PhD a Adabin Hausa daga Jami'ar Umaru Musa Yar'adua, Katsina.

Ya wallafa muƙalu da dama a mujallu na ilimi na cikin gida da na ƙasashen waje, tare da gabatar da takardun bincike a tarurrukan ilimi na ƙasa da na ƙasa da ƙasa. A halin yanzu, bincikensa ya fi mayar da hankali kan alaƙar Fasahar Ƙirƙirar Basira (Artificial Intelligence – AI) da Harshe, musamman yadda AI ke tasiri wajen koyarwa da bincike da fassara, da bunƙasa harshen Hausa a duniyar zamani.

Baya ga ayyukansa na bincike, Dr. Abdulrahman Aliyu yana ba da gudummawa wajen gyarawa da tace littattafai da muƙalu na ilimi, tare da jagorantar matasa masu tasowa a fannin bincike da rubuce-rubuce.

Har ila yau, shi ne Sakataren Kwamitin Shirya Gasar Gajerun Labarai ta Arc. Ahmad Musa Dangiwa, inda yake taka muhimmiyar rawa wajen tsarawa da gudanar da wannan gasa domin haɓaka rubuce-rubucen Hausa da ƙarfafa matasan marubuta.

Yana da burin ganin harshen Hausa ya ci gaba da bunƙasa ta hanyar bincike, fasahar zamani, da amfani da AI wajen samar da ingantattun hanyoyin koyarwa da adanawa, da yaɗa ilimi.

A halin yanzu, yana aiki a National Assembly Service Commission, Abuja, inda yake ba da gudummawa a fannin gudanar da ayyukan gwamnati. Duk da haka, ya ci gaba da gudanar da bincike da wallafe-wallafe a fannin Hausa.

Shi ne zai jagoranci bitar labarai 13 daga cikin wadanda suka tsallako wannan mataki

📌Malam Aliyu Abubakar Sadiq 

Malam Aliyu Abubakar Sadiq

Sunansa Aliyu Abubakar Sadiq malami ne, mai bincike (Researcher), ɗan kasuwa, kuma shugaban Almufid Islamic Foundation. Ya sadaukar da rayuwarsa wajen yaɗa ingantacciyar fahimtar Musulunci da gina tarbiyya, da bunƙasa al'umma ta hanyar ilimi, wa'azi, da ayyukan jin ƙai.

Yana da sha'awa ta musamman a fannonin Tauhidi da Da'awa da  Islamic Finance daa Zakat da Waqf, da ci gaban matasa. A matsayinsa na mai bincike, yana gudanar da bincike kan batutuwan da suka shafi tattalin arziƙin Musulunci da hanyoyin inganta rayuwar al'umma bisa koyarwar Shari'a.

A matsayin Shugaban Almufid Islamic Foundation, ya jagoranci shirye-shiryen ilimantarwa da  tarukan wa'azi da horaswa, da ayyukan taimakon al'umma, tare da amfani da kafafen sada zumunta da shirye-shiryen podcast domin isar da saƙon Musulunci cikin hikima da fahimta.

Baya ga harkokin addini da bincike, Aliyu ɗan kasuwa ne mai fahimtar muhimmancin haɗa kasuwanci da ɗabi'a, yana kuma ƙarfafa matasa su rungumi kasuwanci na halal da dogaro da kai.

Manufarsa ita ce gina al'umma mai ƙarfi wadda ta ginu kan ingantaccen Tauhidi da ilimi mai amfani da kyawawan ɗabi'u, da ci gaba mai dorewa.

Shi ne zai gabatar da bita a kan "Barace-barce a Mahangar Addini da Zamantakewar Al'umma

📌Dr. Mujaheed Abdullahi

Dr. Mujaheed Abdullahi

Sunansa Dr. Mujaheed Abdullahi fitaccen malami ne kuma masani a fannin Harshen Hausa da Adabin Hausa. Malami ne a Sashen Harsunan Nijeriya da Ilimin Harshe na Jami'ar Jihar Kaduna (Kaduna State University – KASU), inda yake koyarwa tare da gudanar da bincike da kuma bayar da gudunmawa wajen bunƙasa ilimi.

Ya shahara wajen gudanar da bincike da wallafa muƙalu a fannonin adabin Hausa da ƙa'idojin rubutun Hausa da sauran batutuwan da suka shafi ci gaban harshe da adabin Hausa. Ayyukansa sun samu karɓuwa a mujallu na ilimi da kuma tarukan ƙasa da na ƙasa da ƙasa.

Dr. Abdullahi Mujaheed na daga cikin matasan masana da suka himmatu wajen bunƙasa ilimin Hausa, tare da horas da ɗalibai da masu bincike domin su zama ƙwararru masu ba da gudunmawa ga al'umma. Ta hanyar koyarwa da bincike da wallafe-wallafensa, ya ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen adanawa da haɓaka al'adu da harshe da adabin Hausawa.

Yana da ƙwarewa sosai kan abinda ya shafi nazarin gajerun labarai da yadda suka wanzu.

Shi ne zai bayar da bita kan "Bara da Roƙo A Adabance"

📌Dr. Abu-Ubaida Sani

Dr. Abu-Ubaida Sani

Sunansa Dr. Abu-Ubaida Sani manazarci ne kuma marubuci. Ya rubuta littattafai kimanin goma sha biyar (15) da maƙalu sama da ɗari (100) waɗanda aka wallafa a mujallu daban-daban a cikin gida Nijeriya da ƙasashen waje. Yakan kuma gabatar da maƙalu a tarukan ƙara wa juna sani.

Yana da muradin ganin rubuce-rubucen Hausa sun mamaye duniya. Yana bakin ƙoƙari wajen gwagwarmayar cimma wannan mafarki ta hanyar rajin ganin Hausawa suna ɗora rubuce-rubuce masu ma’ana a kan intanet. Shi ne ya assasa kafar intanet ta Hausa da take kan gaba a duniya wajen tattara rubuce-rubucen ilimi cikin harshen Hausa (wato amsoshi.com). A bisa wannan yunƙuren ne kuma ya samar da labarai.amsoshi.com, kafar da ta shawara wajen kawo labarai cikin harshen Hausa.

Ya kasance edita a mujallu daban-daban a cikin gida Nijeriya da ƙasashen waje. A cikinsu har da Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture (Nijeria) da da International Academic Journal of Education & Literature, International Academic & Research Consortium (Kenya) da Global Academic Journal of Linguistics and Literature (Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa) da Sarcouncil Journal of Arts, Humanities and Social Sciences (India) da The Afrikanist (Amurka), da sauransu. Bugu da ƙari, shi ne ya samar sannan yake kula da kafafen intanet na mujallu kimanin goma (10).

Wani fanni da ya saka gaba shi ne aikin fassara. Ya samar kamfani mai suna Amsoshi Language Services (amlas.amsoshi.com) inda yake amfani da wannan dama domin koya wa zaƙaƙuran ɗalibai ayyukan da suka shafi kimiyyar harshe a kan intanet.

A yanzu haka yana koyarwa a Sashen Haruna da Al’adu na Jami’ar Tarayya Gusau, a Nijeriya.

Abin da ya fi burge shi, shi ne ganin al’umma suna farin ciki a dalilinsa. Mutanen da suka fi burge shi su ne waɗanda suke aikata daidai tare da rayuwa bisa gaskiya da riƙon amana, da kuma aiki tuƙuru cikin zaƙaƙuranci da buɗaɗɗiyar zuciyar karɓar gyara da datattun sauye-sauyen zamani.

Shi ne zai jagoranci bitar labarai goma daga cikin wadanda suka tsallako wannan matakin.

📌Malama Hadiza Idris

Hadiza Idris

Sunanta Hadiza Idris. Malama ce a Sashen Harsunan Nijeriya na Jami'ar Umaru Musa Yar'adua, Katsina. Haka kuma, ɗaliba ce mai neman digirin na uku PhD a fannin Adabin Hausa.

Fannonin binciken da tafi mayar da hankali a kai sun haɗa da wasan kwaikwayo da nazarin fina-finan Hausa (Drama and Film Studies). A tsawon shekaru, ta gudanar da bincike tare da wallafa muƙalu da suka shafi rubutattun wasannin kwaikwayon Hausa, da kuma nazarin yadda ake aiwatar da baddala a cikin Adabin Hausa.

Ta kuma wallafa littafi mai taken Baddalawa a Wasan Kwaikwayon Hausa, wanda TETFund ta ɗauki nauyin wallafawa a shekarar 2024.

A halin yanzu, tana gudanar da bincike kan rayuwar mace a ƙarni na ashirin da ɗaya, inda take nazarin yadda ake gina hoton mace a cikin fina-finan Hausa masu dogon zango.

Sannan tana maraba da duk wata dama ta haɗin gwiwa a fannin bincike, da wallafa muƙalu, da gudanar da sharhi kan batutuwan da suka shafi rayuwar mata, Adabin Hausa da wasan kwaikwayo, da nazarin fina-finai.

Za ta jagoranci bitar labarai goma daga cikin wadanda suka tsallako wannan mataki.

Post a Comment

0 Comments