𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam khamis Mene ne hukuncin barin yanka ragon suna ga wanda yake da ikon yankawa?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuhu
Yanka rago a ranar
suna (wanda ake kira ‘Aƙīƙah) ibada ce mai karɓuwa a Musulunci, kuma tana da babban lada.
Amma hukuncinta ba dole ba ne, sai dai Sunnah mu’akkadah ce — wato sunnah mai ƙarfi wadda Annabi
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya dage da ita.
Annabi (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya ce: "Kowane yaro ana jingina masa aƙīƙah. A yanka masa ita
a rana ta bakwai, a aske masa kai, a sa masa suna." (Tirmidhi, Abu Dawud,
Ibn Majah)
Haka kuma, Annabi
(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi aƙīƙah ga jikokinsa HASAN
da HUSAIN.
Idan mutum yana da
ikon yankawa (wato yana da hali), amma ya bar yin aƙīƙah saboda sakaci ko
rashin kulawa, to ya bar sunnah mai ƙarfi, kuma ya rasa
lada mai girma. Amma ba ya samun zunubi, domin ba farilla ba ce. Idan kuma bar
yin aƙīƙah saboda talauci ko
rashin hali, to babu laifi a kansa gaba ɗaya.
Ana son a yi yankan a
rana ta bakwai bayan haihuwa. Idan ba a samu damar yin ta ba a wannan rana, ana
iya yin ta a rana ta 14, ko 21, ko duk lokacin da Allah Ya ba mutum iko.
NAMIJI: raguna biyu
masu kamanni.
MACE: rago guda ɗaya.
Babu laifi a yankawa
yaron da aka haifa akuya guda ɗaya, kamar dai yanda mafi yawan malaman fikihu suka fada,
hakan ya wadatar ga abin da aka haifa, shin namiji ne ko mace, domin haka
Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya aikata, saboda abin da aka ruwaito daga
Ibn Abbas Allah ya kara masa yarda, cewa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam),
ya yanka wa HASAN da HUSAINI kowannen su rago guda-guda, Abu Daud.
Amma idan mutum ya
yanka akuyoyi biyu ga namiji, ita kuma mace ya yanka mata akuya guda daya, to
wannan shi yafi.
Barin aƙīƙah ga wanda yake da
hali makaranci ne (ya bar sunnah mai ƙarfi) amma ba zunubi
ba ne. Idan kuma babu hali — babu komai a kansa.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.