Ticker

6/recent/ticker-posts

Shawarar Zama Da Miji Mai Wulakanta Matarsa

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam. Barka da wuni. da fatan kana lafiya. Malam dan Allah a ba ni shawara. Ƙanwata ce a gidan mijinta. Amma zaman babu daɗi sakamakon Yana yi mata wulaƙanci. Kalakala. Amma dai mijin cewa akayi yazo ya nemeta. sabida yabawa da hankalinsa da akayi, dama makobtan juna ne. Kuma yace Yana sonta. Harma sun haifi Yaya. To Amma wulaƙancin yayi yawa. Ahalin yanzu ita matar ta haɗe kayanta awaje ɗaya. Har tana maganar wai ta haƙura. Gidansu zata. To don Allah malam atemaka mana da Shawara..

SHAWARAR ZAMA DA MIJI MAI WULAƘANTA MATARSA

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikis salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.

Abu na farko dai amatsayinki na yayarta, ki yi mata nasiha tare da jan hankalinta game da muhimmancin hakuri da juriya, da kuma girman ladan da Allah yake bayarwa ga masu hakuri.  Misali kamar ayoyin da Allah yake cewa : "HAKIKA LALLAI ALLAH YANA TARE DA MASU HAKURI".

Sannan ki nusar da ita game da girman hakkin mijinta dake kanta ta ɓangaren ladabi, biyayya da kyautata ta kowacce fuska. Ki gaya mata kuma yin hakuri da yanayin halayensa gwargwadon iko yana daga cikin kyautatawar da Allah yake so mace ta yiwa mijinta. Kamar yadda suma mazajen Allah ya umurcesu da yin hakuri da kyautata zama tare da iyalansu cikin adalci.

Domin hakika bayan ayyukan farillai irin su sallah, zakkah da azumi da aikin hajji, babu wata hanya mafi saurin shigar da mace zuwa ga samun rahamar Allah fiye da kyautata zamantakewa da miji..

Kada ki goya mata baya wajen kokarin kashe aurenta. Domin hakika akwai bala'o'i da jarrabobi masu yawa acikin mutuwar aure. Musamman idan kika dubi cewa za ta fita ne ta bar 'ya'yanta har guda biyu.

Kiyi bakin kokarinki wajen fahimtar da ita, sannan ki tuntubi mijin nata amatsayinki na yayar matarsa, ku zauna ki saurari nashi bayanin. Watakil itama akwai laifin da take yi masa. Sai ki bashi hakuri ki tarasu su biyun ki basu shawarwari da nasihohi.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam acikin wani hadisin da Bukhariy da Muslim suka riwaito ta hanyar Sayyiduna Abu Hurairah (radhiyalLahu anhu) Da yake bayanin kofofin samun lada, yace "Yin sulhu atsakanin mutum biyu shima sadaƙah ne".

Acikin irin wannan aikin na sulhu atsakanin Ma'aurata, ya halatta gareki ki fadi duk abinda zaki fada wanda zai kawo gyara atsakaninsu. Koda ta hanyar fadar abinda za'a iya cewa 'Karya' ne. Domin hakika manyan Malaman Musulunci da dama sun nassanta cewa yin karya yakan halatta ga mai yin sulhu tsakanin Mutum biyu.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments