Ticker

6/recent/ticker-posts

Sunan Shaidan Kafin Allah Ya La'ance Shi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum malam KHAMIS. Barka da sallah. da fatan an dawo idi lafiya. Dan Allah ya sunan shedan kafin Allah ya la'ance shi? shin Shaiɗan yana cikin jinsin aljanu ne Ko Mala'iku kuma Da me Allah zai yiwa shaidan azaba a ranar alkiyama?

SUNAN SHAIƊAN KAFIN ALLAH YA LA'ANCE SHI

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu

Malaman tafsiri sun bayyana cewa Sunan Shaiɗan (Iblis) na asali kafin Allah Ya la'ance shi, shi ne: AZAZIL ko AZAZILU wanda ke nufin "Bawan da Allah ya daukaka" ko kuma "Mafi kusa da mala'iku a bauta da ilimi".

Malaman addinin Musulunci sun bayyana cewa shaiɗan yayi girman kai, ya ƙi yi wa Annabi Adamu sujada, Bayan Allah Ya halicci Annabi Adam, Ya umurci Mala'iku su yi masa sujada don girmamawa. Mala'iku duka sun yi biyayya, amma Iblis ya ki, yana mai ganin kansa a matsayin wanda ya fi Adam saboda shi an halicce shi daga wuta, yayin da aka halicci Adam daga ɓako (danko/ƙasa).

Wannan rashin biyayya da girman kai sun sa Allah Ya kore shi daga rahamarSa, Ya la'ane shi, kuma Ya sanya shi cikin tsinannu har zuwa Ranar Kiyama.

A cikin Alƙur'ani mai girma, Allah SWT Ya yi bayanin wannan lamari dalla-dalla, musamman a cikin Suratul A'raf (aya ta 11 zuwa 18).

Sunan shaidan ya koma Iblis ne bayan da Allah Ya kore shi daga rahamar Sa sakamakon rashin biyayya. Allah Ya kore shi daga Aljanna Ya la'ance shi. Daga nan ne aka sauya sunansa zuwa Iblis, wanda ma'anarsa a harshen Larabci ke nufin yanke kauna (daga rahamar Allah), wato wanda aka kora, aka kuma hana shi duk wata alheri. A kan kira shi da suna Shaidan, ma'anar kuma ita ce mai nesa da gaskiya, mai tawaye, ko dukkan wani abu da ya kauce wa tafarkin Allah.

Malaman tafsiri sun yi saɓani game da cewa Shaiɗan yana cikin jinsin aljanu ne Ko Mala'iku zuwa maganganu guda biyu:

1. Shaiɗan yana daga cikin mala'iku, saboda faɗin Allah a cikin suratul Bakara aya ta 34:

وَإِذْ قُلْنَا لِلْمَلَائِكَةِ اسْجُدُوا لِآدَمَ فَسَجَدُوا إِلَّا إِبْلِيسَ أَبَىٰ وَاسْتَكْبَرَ وَكَانَ مِنَ الْكَافِرِينَ

Kuma a lõkacin da Muka ce ga malã'iku: ''Ku yi sujada ga Ãdam,'' Sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa ya ƙi, kuma ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai. (suratul Bakara aya ta 34).

Wannan ya nuna shaiɗan yana daga cikin mala'iku ne.

2. Shaiɗan Aljani ne, saboda faɗin Allah maɗaukakin sarki:

وَإِذْ قُلْنَا لِلْمَلَائِكَةِ اسْجُدُوا لِآدَمَ فَسَجَدُوا إِلَّا إِبْلِيسَ كَانَ مِنَ الْجِنِّ فَفَسَقَ عَنْ أَمْرِ رَبِّهِ أَفَتَتَّخِذُونَهُ وَذُرِّيَّتَهُ أَوْلِيَاءَ مِن دُونِي وَهُمْ لَكُمْ عَدُوٌّ بِئْسَ لِلظَّالِمِينَ بَدَلًا

Kuma a lõkacin da Muka ce wa malãiku, ''Ku yi sujada ga Ãdamu.'' Sai suka yi sujada fãce Iblĩsa, yã kasance daga aljannu sai ya yi fãsiƙanci ga barin umurnin Ubangijinsa, To fa, ashe, kunã riƙon sa, shi da zũriyarsa, su zama majiɓinta baicin Ni, alhãli kuwa su maƙiya ne a gare ku? Tir da ya zama musanya ga azzãlumai. (Suratul Kahf Aya ta 50).

Wannan ayar ta bayyana cewa shaiɗan daga aljanu yake.

Zance mafi inganci shi ne Shaiɗan aljani ne, saboda an halicce shi ne daga wuta, su kuwa mala'iku an halicce su ne daga haske, kamar yadda hadisin Muslim mai lamba ta: (2996) yake nuni zuwa hakan.

Sannan Shaiɗan yana da zuriyya, wacce take hayayyafa, mala'iku kuma ba sa haihuwa, wannan sai ya nuna ba daga cikinsu yake ba, Wannan yasa za'a ɗauki ayar suratul Bakara a matsayin tana nufin yana daga cikinsu ta fuskar zaman tare, amma ba ta fuskar halitta ba, sannan mala'iku ba sa saɓawa Allah, shi kuma shaidan (Iblis) yana saɓawa Allah.

Don neman Karin bayani duba: Tafsirin Ibnu-jarir 1/507 da Jami'u lada'if attafsir 1/278.

Dalilin da yasa wasu ke tunanin shaidan (Iblis) Mala'ika ne saboda ya kasance mai yawan bauta wa Allah sosai tun yana ƙarami, wanda hakan ya sa aka ɗaukaka shi har ya dinga zama da Mala'iku. Lokacin da Allah Ya umarci Mala'iku da su yi sujjada ga Annabi Adamu, an shigar da shi cikin umarnin ne saboda yana cikin su, amma lokacin da ya ƙi yin sujjadar saboda girman kai, sai asalin halittarsa ta Aljani ta fito fili.

A ranar alkiyama babban hukunci da Allah Ya tanadarwa Shaidan shi ne jefa shi cikin wuta madawwamiya. A cikin Suratu Sad (Aya ta 84 zuwa 85), Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi rantsuwa da cewa:

لَأَمْلَأَنَّ جَهَنَّمَ مِنْكَ وَمِمَّنْ تَبِعَكَ مِنْهُمْ أَجْمَعِينَ

"Lalle ne zan cika Jahannama da kai (Iblis) da wanda ya bi ka daga cikinsu gaba ɗaya."

Ya Allah muna neman tsarinka daga sharrin shaidan da tarkonsa.🤲

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments