Ticker

6/recent/ticker-posts

Ilimin Taurari, Hassada Da Kambin Ido

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-salamu Alai-kum. MLM Dan Allah Ina da tambaya. masu ilimin taurari da suke fadawa mutane cewa taurarinsu sun disashe ko suna haskawa ko Wani Al-khairi zai sami mutum kokuma mutane sunawa Wani Hassada, ko akwai ido ma'ana kambin ido Akan mutum Kuma ma Hassadan suyimasa yawa nakusa dananesa, gaskiya suke fada Kuma taurarin sunayin haka Dan Allah malam ayimana bayani yadda zamu fahimta Kuma ataimaka mana da Addu'ar dazatayi maganin wannan matsalar.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu

A cikin Shari'ar Musulunci, hukuncin ilimin taurari ya kasu kashi biyu, ya danganta da yadda mutum ya yi amfani da shi. Akwai sashe da yake Haramun ne (Bokanci da duba), sannan akwai sashe da yake Halal ne (Kimiyya da lissafi).

1. ILIMIN TAURARI DA YAKE HALAL (علم الفلك - ASTRONOMY):

Wannan shi ne nazarin taurari da duniyoyi a matsayin cikakken ilimin kimiyya, kamar lissafin tafiyarsu, kusancinsu, da yadda canjinsu yake shafar lokuta. Wannan fanni Ya halatta (Halal), kuma yana iya zama faralul-kifaya (wajibi akan al'umma) don amfanin addini da rayuwa.

2. ILIMIN TAURARI DA YAKE HARAMUN (التنجيم - ASTROLOGY).

Wannan shi ne neman sanin gaibu ko hango abubuwan da za su faru a nan gaba ta hanyar tafiyar taurari, motsinsu, ko rarrabuwar gidajensu (kamar duba, shiga shafukan Zodiac Signs, ko karanta tauraron ɗan adam na ranar haihuwa). Wannan fanni Haramun ne kuma yana kasancewa babban zunubi (ko shirka).

Shari'a ta bayyana cewa Allah ne kaɗai masanin gaibu. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Wanda duk ya debo wani ɓangare na ilimin taurari (don sanin gaibu), to ya debo wani ɓangare ne na sihiri..." (Abu Dawud).

Yin amfani da taurari don gano kaddara, sa'ar aure, arziki, ko masifa dabi'a ce ta bokaye da 'yan tsubbu.

A koyarwar Musulunci, taurari ba su da ikon juya rayuwar dan adam, ba su san gaibu ba, kuma ba sa kawo alkhairi ko sharri. Allah kadai ya san abin da zai faru nan gaba. Masu fadin tauraron mutum ya disashe ko yana haskawa ba gaskiya suke fada ba, hasashe ne da yaudara. Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya hana zuwa wajen masu duba ko masu duba na taurari. Duk wanda ya yarda da abin da suke fada, to ya kusa fita daga koyarwar addini.

Malamai kamar su Imamu Ƙatadah sun takaita amfanin taurari da Allah ya ambata a Alkur'ani zuwa abubuwa guda uku:

1. ADO GA SARARIN SAMANIYA: Kamar yadda yake a Suratul Mulk, aya ta 5:

وَلَقَدْ زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِمَصَابِيحَ وَجَعَلْنَاهَا رُجُومًا لِلشَّيَاطِينِ ۖ وَأَعْتَدْنَا لَهُمْ عَذَابَ السَّعِيرِ

Kuma lalle Mun ƙawãta samar farko da fitillu, kuma Muka sanya su abin jifa ga shaiɗanu, kuma Muka yi musu tattalin azãbar Sa'ĩr. (Suratul Mulk, aya ta 5)

2. KARIYAR SAMANIYA: Jifan shaidanu kangararru da suke son satar jiyya daga sama.

3. ALAMOMIN GANE HANYA: Kamar yadda Allah ya ce a Suratu An-Nahl aya ta 16:

وَعَلَامَاتٍ ۚ وَبِالنَّجْمِ هُمْ يَهْتَدُونَ

Kuma da waɗansu alãmõmi, kuma da taurãri sunã mãsu nman shiryuwa (ga tafiyarsu ta fatauci) (Suratul An-Nahl Aya ta 16).

A musulunci, Hassada da Kambin Baka (ko Kambun Ido) abubuwa ne guda biyu da suke da tabbas kuma addini ya tabbatar da akwai su da kuma cutarwarsu ga rayuwar ɗan Adam. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi kashedi mai tsanani game da su tare da koyar da hanyoyin kariya.

HASSADA: Ita ce mutum ya ji zafin wata ni'ima (kamar dukiya, ilimi, ko lafiya) da Allah ya yi wa wani bawanSa, tare da burin daddale ko gushewar wannan ni'imar daga gare shi. Hassada dabi'a ce ta zunubi da ke cinye kyawawan ayyukan mutum.

KAMBIN IDO (Al-Ayn): Wannan shi ne cutarwa da ke samun mutum, dabba, ko dukiya sanadiyyar sha'awa, mamaki, ko kallon keta da wani ya yi masa. Kambin Ido (Al-Ayn): Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Kambin ido gaskiya ne." Yana iya fado da mutum daga matsayinsa ko ma ya kai shi ga halaka.

Maimakon zuwa wajen masu taurari, ga addu'o'i da matakan da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya koyar da suke maganin HASSADA da KAMBIN IDO:

1. Karanta Surori Uku Na Karshe (Al-Mu'awwidhatayn) wato Suratul Ikhlas (Ƙul Huwallahu Ahad) Suratul Falaƙ (Ƙul A'uzu bi Rabbil Falaƙ) Suratun Nas (Ƙul A'uzu bi Rabbin Nas). Wannan tana maganin hassada. Ka rinka karanta wadannan surori sau uku safe da yamma da lokacin kwanciyar bacci kuma ka shafa a daukacin jikinka.

2. Karanta Ayatal Kursiyyu. Ka karanta ta duk bayan sallah, kafin ka kwanta barci, da kuma safe da yamma. Tana tsare mutum daga dukkan sharri.

3. Karshen Suratul Baƙarah: (Ayar karshe guda biyu) wato Amana Rasulu, ka karanta daddare.

4. Addu'ar Kariya Daga Kambin Ido Zaka iya fadin wannan addu'ar sau da dama:

أَعُوذُ بِكَلِمَاتِ اللَّهِ التَّامَّةِ، مِنْ كُلِّ شَيْطَانٍ وَهَامَّةٍ، وَمِنْ كُلِّ عَيْنٍ لَامَّةٍ.

Ma'ana: Na nemi tsari da kalmomin Allah cikakku, daga dukkan shaidan da dabba mai dafi, da kuma kowane ido mai cutarwa.

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kasance yana neman wa jikokinsa (Hasan da Husaini) tsari da wannan addu'ar:

MATAKAN KARIYA NA RAYUWA:

1. BOYE SIRRI: Kar ka rinka tallata dukkan alkhairinka ko nasarorinka ga kowa, musamman a kafafen sada zumunta (social media). Yana da kyau mutum ya fadi ni'imar Allah gare shi, amma musulunci ya halatta mutum ya boye wasu sirrika ko nasarori na rayuwarsa ga mutanen da yake zargin suna da hassada ko kishinsa, har sai abin ya tabbata (Kamar yadda Annabi Ya'ƙub ya shaidawa Annabi Yusuf a cikin Alƙur'ani).

2. AMBATON ALLAH: Duk lokacin da kaga wani abu ya burge ka na kanka ko na wani, fadi "MASHA'AALLAH, TABARAKALLAH" don kar ka kwashe da ido. Idan ka ga wani abu mai kyau a gurin dan'uwanka, ko jikinka, kada ka tsaya murna kawai. Fada: "MASHA'ALLAH, TABARAKALLAH" ko "ALLAHUMMA BARIK". Wannan yana kore tasirin kambin ido nan take.

Idan an tabbatar mutum ya kamu da kambin ido, akwai hanyoyi guda biyu na magani

1. Idan an san wanda ya yi kambin, za a umarce shi ya yi alwala ko ya wanke hannunsa da fuskarsa a cikin kwanon ruwa. Sai a dauki wannan ruwan a zuba shi a bayan wanda aka yi wa kambin daga bayansa. Da izinin Allah zai warke nan take.

2. Yin Ruƙyah: Karanta ayoyin Alƙur'ani (kamar Fatiha, Ayatul Kursiyyu, da Kulhuwa da Falaki da Nasi) a cikin ruwa a ba wanda yake da cutar ya sha kuma ya yi wanka da shi.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

  ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments