Kowa ya san irin rawar a zo a gani da Malaman al'umma suke takawa don ganin al'umma ta tsira a Duniyanta da Lahiranta. A kullum su suke koya wa al'umma Addini, suke koya musu Mu'amalar harkokin Duniya gaba daya, tare da koya mata kyawawan dabi'u. Su suke tsoratar da al'umma game da fitunu, musamman wadanda suke da nasaba da siyasa, wadanda tun tuni Annabi (saw) ya yi bayani a kansu kuma ya tsoratar. Su suke zamowa fitila ga al'umma a lokacin da ta dimauce take neman mafita.
To, a game da Malaman
Al'umma irin wadannan, wadanda suka zama madubi ga Al'umma, an samu wasu
bangarori biyu masu hamayya da juna, wadanda su kuma babu wadanda suka rena
kamarsu.
Wadannan bangarori kuwa su
ne Kungiyar Salafiyyun "Madakhilah" da kuma Kungiyar Ikhwan da
rassanta da 'ya'yanta..
Kungiyar Ikhwan ta rena
Malaman Al'umma, suna sukarsu, suna cewa; ba su da "Fiqhun Waki'i",
suna nufin ba su san harkokin siyasa da jihadi ba, ba su san siyasar Duniya ba.
Don haka ba za a karbi Fatawa ko wani ilimi game da harkokin siyasar Duniya da
jihadi da abin da ya shafi matsalolin Al'umma, kamar ta Falasdinawa da ire -
irensu daga gare su ba, saboda -wai- su jahilai ne a wannan fanni. Su kawai sai
dai a karbi fatawan tsarki da Sallah daga gare su, shi ya sa ma suke kiransu da
Malaman jinin haila da nifasi, don batanci da suka. Kai, akwai lokacin da har
suke sukarsu da sunan Malaman fada "علماء
السلاطين", kai, har lamarin ya kai ga kiransu
da sunan Munafukai, sai su yi ta janyo Ayoyin Munafukai suna dorawa a kansu.
Saboda kawai su wadannan Malaman ba sa goyon bayan tafo-mu-gama da gomnatoci da
masu mulki, saboda guje wa fitintunun siyasar da Annabi (saw) ya tsoratar da
Al'ummarsa game da su.
To a daya bangaren kuma,
akwai wata kungiyar da take yi wa Kungiyar ta Ikhwan inkari a kan wannan
mummunan tafarki, wato su ne Kungiyar Salafiyyun, wadanda suka shahara da sunan
"Madakhilah".
To amma kash! Ita ma wannar
kungiya tana da nata salo na rena wadancan Malamai, inda take kiransu da
Malaman da ba su san "Manhaji" ba. Sun yarda wadancan Malaman masana
ne a Shari'a, sun san Fiqhu da Aqida, amma sun jahilci "Manhaji".
Saboda suna ganin babu wanda ya san "Manhajin" sai Shugaban kungiyar
tasu da wasu 'yan tsirarun Na'ibansa. Kuma wannan "Manhaji" ya fi
komai a wajensu, don shi wata kololuwar martaba ce da sai mutum ya zama Musulmi
Ahlus Sunna mai ingantacciyar akida kafin ya isa inda zai zama mai
"Manhaji" mai kyau. Wato idan ya shiga kungiyar tasu. Don haka su a
wajensu, kasancewarka mai bin Akidar Salaf bai wadatar ba, har sai ka hada da
bin "Manhaji", wanda hakikaninsa shi ne shiga kungiyarsu da bin
shugabanninta sau da kafa.
Wannan ya sa sai ka ji suna
sukar manyan Malamai, suna cewa ba su san "Manhaji" ba, don haka a yi
hattara da su. Duk da kasancewarsu jagororin Al'umma a ilimin Shari'a da akidar
Sunna.
To in an lura, duka wadannan
bangarorin biyu sun yi tarayya cikin sukar manyan Malaman Sunna da aibanta su,
da nuna cewa su kungiyoyin biyu suna da wasu mahanga game da siyasa (a wajen
Kungiyar Ikhwan), da "Manhaji" (a wajen Kungiyar Salafiyyun) sabanin
abin da Malaman Shari'a suka sani.
A takaice, ya kai dan uwa
Ahlus Sunna, kar ka rudu da wadanda kungiyoyi guda biyu. Ka yi riko da Malaman
Al'umma, wadanda suka shahara da karantar da kai Addini, ka sani Shari'ar
Muslunci ta kunshi komai, ka sani cewa, Malaman Al'umma su ne masana siyasa da
matsalolin Al'umma da abin da ya shafi siyasar Duniya, fadakarwarsu da
nasihunsu da fatawowinsu su ne abin dauka ba maganganun Yan taratsi ba, masu yi
wa Al'umma turin-jeka-ka-mutu. Kowa ya shaida abin da ya faru a zanga-zangan
kasashen Larabawa.
Haka kuma a Addini babu wani
abu -wai- shi "Manhaji" da wadancan Malamai jagororin Al'umma da ba
su sani ba. In kuwa akwai to kirkirarre ne, ba a cikin Addini yake ba. Ma'ana;
ba shi da asali a cikin abin da Annabi (saw) ya zo da shi, kuma ya bar
Sahabbansa a kansa.
Don haka ya kamata ka san
cewa; a kullum gaskiya tana tsakanin karya guda biyu ne, shiriya tana tsakanin
bata guda biyu. Hanya madaidaiciya tana tsakanin kungiyoyi guda biyu.
✍️ Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.