𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum malam barka da warhaka muna godiya sosai a kan kokarin da ake yi a kanmu Allah ya saka da mafificin alkhairi, dama malam tambaya ta ita ce ina son in san ranakun da Allah ya ambata acinkin al'qur'ani mai gima na gode Allah ya kara basira
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuhu
A cikin Alƙur'ani Maigirma,
Allah (SWT) ya ambaci sunayen wasu takamaiman ranaku a cikin mako, da kuma wasu
kwanaki masu alfarma waɗanda suka shahara
wajen bauta da ambaton Allah. Ga jerin ranakun da ayoyin da suka ambace su:
RANAKUN MAKO
(AYYAAMUS USBU'I): A cikin Alkur'ani mai girma, ayoyi da yawa suna nuna cewa
Allah Maɗaukaki ya halicci
sammai da ƙasa da abin da ke tsakaninsu a cikin kwanaki shida. Daya
daga cikin shahararrun ayoyin da ke tabbatar da wannan ita ce a Suratu
Al-A'araf Aya ta 54:
إِنَّ
رَبَّكُمُ اللَّهُ الَّذِي خَلَقَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٍ
ثُمَّ اسْتَوَىٰ عَلَى الْعَرْشِ يُغْشِي اللَّيْلَ النَّهَارَ يَطْلُبُهُ
حَثِيثًا وَالشَّمْسَ وَالْقَمَرَ وَالنُّجُومَ مُسَخَّرَاتٍ بِأَمْرِهِ ۗ أَلَا
لَهُ الْخَلْقُ وَالْأَمْرُ ۗ تَبَارَكَ اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ
Lalle ne Ubangijinku
Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwãnaki
shida, sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, Yanã
sanya dare ya rufa yini, yanã nẽman sa da gaggawa,
kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar
kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana! (Surah:
Al-A'raaf, Ayat: 54).
Wadannan ayoyi sun
hada da Suratul Yunus aya ta 3. Da Suratul Hud Aya ta 7. Da Suratul Al-Hadid
Aya ta 4. wadanda dukkansu ke jaddada cewa Allah ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwanaki
shida. Malaman tafsiri sun bayyana cewa wadannan "kwanaki" na iya
nufin lokuta na daban, ba wai awanni 24 na duniya ba.
RANAR JUMA'A (YAUMAL
JUMU'AH): Ita ce rana mafi girma a cikin mako wadda Allah Ya kebance ta da
sallar jam'i ta musamman da kuma huduba. Ana samun ambatonta a cikin Suratul
Jumu'ah Aya ta 9:
يَا
أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِذَا نُودِيَ لِلصَّلَاةِ مِنْ يَوْمِ الْجُمُعَةِ
فَاسْعَوْا إِلَىٰ ذِكْرِ اللَّهِ وَذَرُوا الْبَيْعَ ۚ ذَٰلِكُمْ خَيْرٌ لَكُمْ
إِنْ كُنْتُمْ تَعْلَمُونَ
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni!
Idan anyi kirã zuwã ga salla a rãnar Jumu'a, sai ku yi aiki zuwa ga ambaton
Allah, kuma ku bar ciniki. Wancan ɗinku ne mafi alhẽri a gare ku idan kun
kasance kunã sani. (Surah: Al-Jumu'a, Ayat: 9).
RANAR ASABAR: Allah
Ya ambaci "Ranar Asabar" da sunanta a cikin ayoyi da dama, musamman
wajen bayyana labarin Yahudawa da kuma jarabawar da Allah Ya musu:
وَاسْأَلْهُمْ
عَنِ الْقَرْيَةِ الَّتِي كَانَتْ حَاضِرَةَ الْبَحْرِ إِذْ يَعْدُونَ فِي
السَّبْتِ إِذْ تَأْتِيهِمْ حِيتَانُهُمْ يَوْمَ سَبْتِهِمْ شُرَّعًا وَيَوْمَ لَا
يَسْبِتُونَ ۙ لَا تَأْتِيهِمْ ۚ كَذَٰلِكَ نَبْلُوهُمْ بِمَا كَانُوا يَفْسُقُونَ
Kuma ka tambaye su
daga alƙarya wadda ta kasance kusa ga tẽku, a lõkacin da suke
ƙẽtare
haddi a cikin Asabar, a lõkacin da kĩfãyensu, suke je musu a rãnar Asabar ɗinsu jẽre. Kuma a rãnar da
ba su yi Asabar ba, bã su zuwa gare su; Kamar wancan ne Muke jarraba su da abin
da suka kasance sunã yi na fãsiƙanci. (Surah: Al-A'raaf, Ayat: 163).
Wadannan ayoyi da
Allah ya ambaci Ranar Asabar sun hada da Surah Al-Baqara, Aya ta 65. Da Surah
An-Nisaa, Aya ta 47. Da Surah An-Nisaa, Aya ta 154.
RANAR KIYAMA (YAUMUL
QIYAMAH): Ita ce babbar ranar da Allah Ya yi alkawarin tattara dukkan halittu
domin hisabi da sakamako. Ana samun ambatonta a cikin ayoyi da dama, kamar
Suratul Qiyamah Aya ta farko da kuma Suratul Baqarah Aya ta 85.
لَا
أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِ
Bã sai Nã yi rantsuwa
da Rãnar Ƙiyãma ba.
ۖ وَيَوْمَ الْقِيَامَةِ
يُرَدُّونَ إِلَىٰ أَشَدِّ الْعَذَابِ ۗ وَمَا اللَّهُ بِغَافِلٍ عَمَّا
تَعْمَلُونَ
Kuma a Rãnar kiyãma
ana mayar da su zuwa ga mafi tsananin azãba. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba
daga barin abin da kuke aikatãwa. ( Surah: Al-Baqara, Ayat: 85).
KWANAKI MASU ALFARMA
(AYYAAMUN MA'LUMAAT): Baya ga ranakun mako, Alƙur'ani ya ambaci wasu
muhimman kwanaki da Allah Ya keɓance su da falala da tsarki:
KWANAKI GOMA NA FARKO
NA WATAN ZUL-HIJJAH: Allah (SWT) yana cewa: "Kuma su ambaci sunan Allah a
cikin kwanaki sanannu..." Suratul Hajj Aya ta 28:
لِيَشْهَدُوا
مَنَافِعَ لَهُمْ وَيَذْكُرُوا اسْمَ اللَّهِ فِي أَيَّامٍ مَعْلُومَاتٍ عَلَىٰ
مَا رَزَقَهُمْ مِنْ بَهِيمَةِ الْأَنْعَامِ ۖ فَكُلُوا مِنْهَا وَأَطْعِمُوا
الْبَائِسَ الْفَقِيرَ
Dõmin su halarci
abũbuwan amfãni a gare su, kuma su ambãci sunan Allah a cikin 'yan kwãnuka
sanannu sabõda abin da Ya azurta su da shĩ daga dabbõbin jin dãɗi. Sai ku ci daga
gare su, kuma ku ciyar da matsattse matalauci. (Surah: Al-Hajj, Ayat: 28).
Malaman tafsiri sun
yi ittifaqi cewa waɗannan su ne kwanakin
goma na farkon Zul-hijjah, waɗanda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce babu
wasu ayyukan alkhairi da suka fi su falala.
GOMAN KARSHEN WATAN
RAMADAN: Duk da ba a ambaci su da kalmar "kwanaki" ba kai tsaye a
cikin ayoyi, Allah Ya ambaci darensu da falalarsu, musamman daren Lailatul-Ƙadri, wanda ya fi
watanni dubu albarka (Suratul Ƙadr).
لَيْلَةُ
الْقَدْرِ خَيْرٌ مِنْ أَلْفِ شَهْرٍ
Lailatul kadari mafi
alheri ne daga wasu watanni dubu. (Surah: Al-Qadr, Ayat: 3).
RANAR ARAFA: A cikin
Alkur'ani Mai Girma, Allah (S.W.T) ya ambaci kalmar "Arafat" kai
tsaye a cikin Suratu Al-Baqarah Aya ta 198:
لَيْسَ
عَلَيْكُمْ جُنَاحٌ أَنْ تَبْتَغُوا فَضْلًا مِنْ رَبِّكُمْ ۚ فَإِذَا أَفَضْتُمْ
مِنْ عَرَفَاتٍ فَاذْكُرُوا اللَّهَ عِنْدَ الْمَشْعَرِ الْحَرَامِ ۖ وَاذْكُرُوهُ
كَمَا هَدَاكُمْ وَإِنْ كُنْتُمْ مِنْ قَبْلِهِ لَمِنَ الضَّالِّينَ
Bãbu laifi a kanku ga
ku nẽmi falala daga Ubangijinku. Sa'an nan idan kun malãlo
daga Arafãt, sai ku yi ta ambatar Allah a wurin Mash'aril Harãmi kuma ku tuna
Shi kamar shiriyar da Ya yi muku kuma lalle ne kun kasance a gabãninsa, haƙĩƙa, daga ɓatattu. (Surah: Al-Baqara, Aya ta 198).
Wannan rana ce wadda
take tana daga cikin "kwanaki sanannu" na watan Zul-hijjah, kuma a
cikinta ne Allah Ya cika addinin Musulunci.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.