𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum warahmatullah wabarakatuh malam. Tambaya nake da ita, shin ya halatta amarya taƙiyin sallah a ranar da aka daura mata aure saboda yawan aikace-aikace da rashin lokaci, ko kuma a daren amarci sai na ki yin sallar asuba, shin hakan ya halatta? Malamai ina so aja ma amare kunne akan hakan domin gaskiya mata da yawa basayin sallah a daren amarci saboda wani dalili na daban, Allah ya saka maku da Alkhairi.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam
warahmatullah wabarakatuh.
A'a bai halatta ba ga
amarya ta bar sallah a ranar daurawa aurenta ko daren amarci saboda aiki ko
rashin lokaci. Rashin lokaci ko yawan hidima ba sa zama dalilin barin sallah, kuma
Fara rayuwar aure da saɓon Allah yana janye
albarka daga auren.
Sallah tana ɗaya daga cikin
rukunai na Musulunci da babu rangwame a kansu matukar mutum yana da hankali da
lafiya.
Magana ta gaskiya ita
ce wajibi ne a gareku Amarya da Ango su sallaci sallolin su na farillah da
Allah ya wajabta ma musulmai yin waɗannan salloli.
An tambayi commitee
na malamai masu bada fatawa na kasar saudiyya cewa "Yaya hukucin yin
sallah ga mace a daren amarci?
Sai suka Amsa da cewa
" Ya wajaba a gareta ta sallaci sallolin ta na farillah saboda babu wani
sassauci akan barinta wai saboda daren amarci, sai dai idan da wani dalili da
zai hanata sallah kamar tana a halin haila (jinin dabi'a) ko kuma jinin
haihuwa"
Domin neman karin
bayani duba acikin littafin (LAJNATUD-DAA'IMAH 7/343)
Wajibi ne Amarya da
Ango ku kasance kun sallaci sallolin ku a ranar da aka daura maku aure, kuma ku
nisanci saɓon Allah maɗaukakin sarki, ku
kiyaye daga dukkan wani aiki da zai kai ku zuwa ga saɓa ma Allah, lallai
babu wani dalili na daban wanda shari'a batayi magana akansa ba da zai hana
mace yin sallah, matukar ba waɗannan da aka lissafa ba, kai kuwa Ango dolene baka da
wani dalili Don haka dukkan wanda ya nisanci sallah to sheɗan yayi galaba akansa,
irin waɗannan ma'auratan sai
ayi masu nasiha, musamman iyayenmu sai suyi kokarin kwaɗaitar dasu dangane da
gyara tsakanin bawa da mahaliccin sa.
'Yar uwata kiji
tsoron Allah maɗaukakin sarki ki
sallaci sallolin ki, kaima Ango kaji tsoron Allah maɗaukakin sarki domin
kuwa Allah yayi tanadi na azaba ga wanda yabar sallah da gangan, Allah maɗaukakin sarki ya
shiryar damu, Allah yasa mudace.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu. . .
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.