Ticker

6/recent/ticker-posts

Fitowar Mace Takarar Majalisa

Cikin kwanakin nan ana ta tattaunawa a kan mas'alar halasci ko rashin halascin fitowar mace takarar kujerar majalisa, inda aka hakaito fatawar wasu Malamai da suka tabbatar da halasci, sai kuma aka samu wani Malami ya saɓa musu, har ya wallafa takarda, yana mai yi musu raddi, ya kuma karantar da takardar da ya rubuta.

Ni a iya bincike na, na fi gamsuwa da rashin halascin fitowar mace takaran kujerar majalisa, balle kuma kujerar Gomna, balle kuma Shugaban ƙasa. Saboda dalilai da suke nuni da cewa; harkar shugabanci na maza ne ba na mata ba. Shi ya sa Malamai da yawa suke ƙirga "الذكورية" wato kasancewa namiji a cikin sharaɗin shugabanci.

To amma ni abin da ya ja hankalina a cikin raddin da Malamin ya yi wa waɗancan Malaman shi ne, yadda ya sanya saɓani a kan mas'alar -wai- saɓani ne tsakanin Ahlus Sunna da ƴan bidi'a, alhali mas'alar babu Nassi a kanta. Kuma ban san wata Aƙida ta bidi'a da aka gina a kanta ba. Kuma ba a san wata ƙungiyar bidi'a da ta yi fice da hakan a tsakanin sauran Musulmi ba.

Saboda haka iya abin da za a ce shi ne; wannar mas'ala ce "Ijtihadiyya", saboda babu Nassi a kanta. Saboda Hadisin Abu Bakrah (ra):

"لن يفلح قوم ولّوا أمرهم امرأة".

صحيح البخاري

"Duk al'ummar da suka shugabantar da mace a kansu ba za su rabauta ba".

Nassi ne a kan babban shugabanci, kamar Shugaban ƙasa ko Gomna. Saboda "ولاية" (Wilaya) da ke cikin Hadisin ba dukkan nau'o'i na shuganbanci ba ne, kamar na ƴan majalisa, saboda idan mun duba ma'anar da Malamai suke bai wa "Wilaya" za mu ga ƴan majalisu ba su da ita. Malamai suka ce:

"الولاية هي القدرة على إنشاء العقود والتصرفات النافذة، من غير توقف على إجازة أحد".

الموسوعة الفقهية الكويتية (٧/ ٢٠٥)

"Mulki shi ne samun iko a kan kulla yarjejeniya da zartas da aiyuka, ba tare da jiran sahhalewan wani ba".

Shi ya sa Ibnul Atheer ya ce:

"الولاية تُشعر بالتدبير والقدرة والفعل، وما لم يجتمع ذلك فيها لم ينطلق عليه اسم الوالي".

النهاية في غريب الحديث والأثر (٥/ ٢٢٧)

"Mulki yana nuna gudanarwa da iko da aiki, duk mulkin da waɗannan ba su haɗu a cikinsa ba to ba za a kira shi da shugaba mai mulki ba".

Idan mun lura da wannan ma'ana ta "Wilaya" za mu ga cewa; ba za ta dace da kowa ba cikin kujerun da ake takara a kansu sai kujerar Shugaban ƙasa ko Gomna. Amma ƴan majalisa ba su da wani zartarwa da suke yi a kan talakawa, shi ya sa wani ɗan majalisar, idan an zaɓe shi ya tafi Abuja, ba za a ƙara ganinsa ba sai lokacin wani zaɓen.

Ala ayyi halin, wannar mas'ala mas'ala ce "Ijtihadiyya", mas'ala ce da babu laifi idan an yi saɓani a kanta. Duk wanda ya yi Ijtihadi ya yi fatawa da halasci, to wanda ya yi Ijtihadi ya yi fatawa da haramci ba zai zargi wanda ya yi fatawa da halascin ba. Saboda ba a zargi a mas'alolin Ijtihadi. Wanda ya dace yana da lada biyu, wanda ya yi kuskure yana da lada ɗaya.

To saboda haka, wani dalili ne zai sa a taƙaice mas'alar tsakanin Ahlus Sunna da ƴan bidi'a?

Har jahilai da yara, ko Malamai marasa wara'u su fara zargin wanda ya saɓa musu, suna bidi'antar da shi?!

Saboda haka yana da kyau a bi a hankali, a ajiye abubuwa a muhallinsu.

~ Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)

Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments