𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalmu alaikum, Mene ne hukuncin Mutanen da sukeyin Sex-Chat, wato hirar batsa ta hanyar rubutun Text ko ta hanyar rubutu a Social-Media musamman ta WhatsApp? Malam wallahi na Shiga bala'i Ka taimakeni Nidai mutum ne Wanda Allah ya jarabceni da karfin sha'awa Kuma ban taɓa yin zina ba To Amma wannan WhatsApp ɗin ya haɗani da mutanen banza an shigar dani wani group na batsa hotunan banza da videos ɗin banza Duk ina ganinsu Rana ɗaya sheɗan yayi tasiri a kaina wlh Malam wata yarinya da muka haɗu da ita har hoton farjinta ta turomin nima na tura mata nawa, Sai da na Riga na aikata hakan Abin yaketa damuna Na tuba Malam Allah zai yafe min kuwa? Sannan kuma Malam wane abu zan dage da yi Wanda Allah bazai kamani da laifin ba Wallahi nayi nadama.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuhu
To itadai hirar da akeyi ta
batsa atsakanin Namiji da Mace ta hanyar Ƙiran
Waya ko rubutaccen saƙo
kamar yadda aka fi saninta da sunan Sex-Chatting, ko Shakka babu wannan wata
Musibace da Fitina wacce ta addabi Al'ummar wannan Zamani damuke cikinsa, tun
daga kan Maza har Mata, masu aure da marasa aure, wasuma daga cikinsu za ka samu
cewa Ɗaliban Ilimine, danhaka al'amarin dai
sai wanda Aʟʟαн ( ﷻ
) Ya tsallakar kawai, itadai wannan hirar batsa takasune gida biyu.
1. ko da yakasance Namiji zai
yi irin wannan hirarne da Matarsa itama Mace tayi da Mijinta.
2. Kokuma ya kasance Mutum zai
yi irin wannan hirarne da Matar da ba tasaba ko Mijin da ba nataba
Idan ya zamana Mutum zai yi
irin wannan hirarne da Matarsa ko Mace tayi da Mijinta, to yakan iya zama Halal
amma Saida Sharuɗɗa guda biyu:
1. Sharaɗi
nafarko yakasance babu wani Mutum akusa dasu ta yadda zai iyajin hirar dasukeyi
atsakaninsu idan yazamana suna hirarne ta hanyar Ƙiran
Waya, idan kuma ta hanyar rubutune to ya kasance sunkiyaye ta yadda babu wani
wanda zai iyaganin hirar dasukayi acikin rubutun, kokuma yaga irin hotunan
sassan jikinsu da suka aikawa junansu, balle kuma Mutum yace zaije ya nunawa
abokansa ko ita ta nunawa ƙawayenta
irin hirar da sukeyi.
2. Sharaɗi
nabiyu, ya kasance tsakanin Matar da Mijin dukkansu sun aminta da kansu cewa
wannan hirar da sukeyi bazata kaisu ga aikata dukkan wani abu ta hanyar wasa da
jikinsu wanda hakan zai iya kaisu ga sunfitar da Maniyyinsu ba, wato abinda da aka
fi sani da suna istimna'i (Masturbation) idan waɗannan
Sharuɗɗa
guda biyu suka cika to ya halatta ma'aurata suyi atsakaninsu, amma idan hirar
zata iyasa wani daga cikinsu kokuma suduka sukai ga sunkasa iya mallakar kansu
harsai Mutum yayi abinda zai sashi yafitar da Maniyyinsa to anan suma kansu
ma'auratan yazama haramun suyi irin wannan saboda wancan mummunan aikin da
hirar zata iya kaisu ga aikatashi, domin a Shari'ance akan iya Haramta abinda
yake Halalne idan yakasance zai iya kai Mutum ga aikata Haramun, amma idan
yakasance hirace kawai sukeyi atsakaninsu har Sha'awar Mutum takai Ƙololuwa yayi Inzalin-Maniyyi batare da
yayi amfani da hannunsa ba ko wani abu dabam to wannan babu laifi ya halatta,
Amma idan yakasance ita
wannan hirar ta batsa maisuna Sex-Chatting, tana gudanane atsakanin waɗanda
ba ma'aurataba wanda kuma dama galibi ita wannan hirar anfi yintane ko da tsakanin
Samari da 'Yammata, ko Samari da Matan aure, ko Maza masu aure da 'Yammata,
kokuma Mazan aure da wasu Matan auren da ba nasuba, danhaka wannan ko kokwanto
babu akancewa yin wannan hirar Haramunne Ƙaulan-Wahidan,
danhaka wajibine akan masu wannan aiki suyi gaggawar tuba zuwa ga Aʟʟαн( ﷻ
).
Maganar yafewa Kuwa: Allah
yana yafe kowanne zunubi da bawa ya ke aikatawa, idan ya tuba, amma banda
shirka wato hadashi da Wani bawansa wajan bauta. Kamar yanda Ayoyi da hadisai
ingantattu da dama Suka nuna, Amma akwai sharudan tuba:
1. Dena zuzunubi.
2. Nadama Akan saɓon.
3. Ya Qudurci niyyar, bazai
sake aikata aikin ba.
Idan aka rasa ɗaya
daka cikin ukun nan tuba bai tabbata ba. Sannnan kuma banda hakki mutane iyaka
hankinka tsakaninka da Allah. Sannan kuma kadege da neman gafarar Allah, ka
nesanci duk abinda zai kai ka ga aikata zantukan da zasu tada maka sha'awa,
Sannan ka lizimci azumin lafila saboda sha'awa da take damunka, da ya waita
istgfari.
Allah ya tsaremu.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.