Ticker

6/recent/ticker-posts

Murtala Mamsa Jos - Wakar APC I

MURTALA MAMSA JOS - WAƘAR APC I

Jagora: Da na je taron jari,

 Na gano abin mamaki al’umma

Amshi: mu ji mansan waka,

 Wai dawa da wa kaje,

 Ka gano kafada mana

 

Jagora: janar Buhari ya zo taro

Bola tunubu ya zo taro

Amshi: To

 

Jagora: Asuwaji ya zo taro

 Almakura ya zo taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Okorocha ya zo taro

El-rufa’i ya zo taro

Amshi: To

 

Jagora: Adam Oshumole ya zo taro

 Baba tunde ya zo taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Fashola yazo taro

 Eke odoma yazo taro

Amshi: To

 

Jagora: Christ ngege yazo taro

 Ogunnaye yazo taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Obita yazo taro

Jolabi ya zo taro

Amshi: To

 

Jagora: Ane okonko yazo taro

 Dom okibe yazo taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Abdulsalami yazo taro

Audu obe yazo taro

Amshi: Too

Jagora: John ogege yazo taro

 Kasiru gaya yazo taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Shekarau yazo taro

A halliru yazo taro

Amshi: Ehe

 

Jagora: Bafarawa yazo taro

 Garda gadi yazo taro

Amshi: Too

 

Jagora: Tod abiti yazo taro

BubaGaladima gun taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Enginiya bajoga a taro

 Hadi sirika yazo taro

Amshi: Too

 

Jagora: Ebike Amos yazo taro

 Kayode Fayomi gun taro

Amshi: Ehe

 

Jagora: Gwamna Rufa’i yazo gun taro

 Ibrahim gaidam gun taro

Amshi: Uhm

 

Jagora: Kashim shattima yazo taro

 Tunde bakari yazo taro

Amshi: Eye

 

Jagora: Sun taru ne su ceto yan Najeriya

 Sabuwar jam’iyya ,

 APC mai ceton Najeriya

Kowa ya bi.

Amshi: Sabuwar jam’iyya APC

 Gaskiya ta zo

 

Jagora: Ku zo mu kama gaskiya

 Ta zo Najeriya

Amshi: Gaskiya ta zo

 Mun karɓe ta

Mun riƙa hannu biyu yan Najeriya,

da hannu bi-biyu.

Jagora: Mun karɓeta hannuwa bi-biyu

‘Yan Najeriya, kowa ya bi

Amshi: Sabuwa ta zo,

APCnmu mun amince

‘Yan Najeriya,

Sabuwa tazo

Jagora: Sabuwa ta zo

Mun karɓeta mun amince

‘Yan Najeriya kowa ya bi

Amshi: Gaskiya ta zo mun karɓeta

Ƙauyuka, birni Najeriya, Kowa ya bi

Jagora: Mun amince ‘yan Najeriya

Mun karɓe ta hannu bi-biyu

Amshi: Gaskiya ta zo, mun karɓe ta

Mun amince ‘yan Najeriya Kowa ya bi

Jagora: Ubangiji Allah Sarki taimake ni

Yau na ɗauko baituka

Wajibi ne Sarki yau ya sami

Ƙwarkwara ya yi sa-ɗaka

Taimakamini Sarki Allah

Tabara wahid kai mani ɗaukaka

Zan yi waƙar jam’iyyar nan

Da za ta ceto yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora; Na kira Allah sarkin nan

 Da yai saman nan har da qasan bakwai

 Na sako Manzon Allah

 Xan Amina wanda ya bi ka saman bakwai

 Kwanakin nan Allah ne

 Duk ya yi su in ka qirga su bakwai

 Taimakonka muke neman Juljalalu

 Talakawan duk Najeriya.

Amshi; Sabuwa ta zo

 APCnmu mun amince ‘yan Najeriya

 

Jagora‘Yanuwa ‘yan Najeriya muna ta bacci

Ta sako gangara

Riƙon amana ba ɗan kishiya

Wanda yai haka sai ya kassara

Maƙiyan talakawa sun take mana

Iska sai mu yi hattara

Ba rashin kunya ba manyan kasarmu

ba sa aikin gaskiya

Amshi: Sabuwar jam’iyya APCnmu

 Mun amince ‘yan Najeriya

 

Jagora: Tun tana ƙarama Najeriya

Tarawa ke yi mata hassada

Ta zamo ingarma ta girma

Sannu dutse gatan ɗanbura

Sun buga sun bar ta tana nan

A yanzu har sun gaji da hassadar

Ta zamo kafuwar Allah

Rabbana yana kallon ku a duniya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Babatu na zuga ba

Mai son karo ya zo

Ga rago a kara

Kaji giwa bukkan daji kin wuce harbi

Koko tokara

Sannu maliya baki ƙafewa dukkan ruwa

A cikinki ya tattara

Jam’iyyar talakawa APC mun amince ‘yan najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Dole ne mai tarkon tsuntsu ya kau da

Kai ya bi sa da lalama

In ya ci da zucci tsuntsu ya gan shi

Tashi za sui sama

Dole ne in ya da maɗaci na je

In ɗauko mai ƙwaryar zuma

Jam’iyyar APC, Allah ya bamu mui

Kishin Najeriya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Sannu maliya ba ki ƙafewa duk jama’a

Sun ɗiba sun bari

Shi manomi ƙauye shi za ya ba mu

Labarin ɓarnar biri

Wai ina sunan mugun da yassai ashana

Yab baiwa biri

Mun shiga uku ‘yan Najeriya ɗan Neja

Kai ka dafa mana taliya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Duka jam’iyyun Najeriya sun haɗa kai

Talakawa kun jiya

Tun da sun haɗa kai talakawa mu bi su

Kar mu yi tambaya

Kar mu yarda da duk wani wanda za ya

Zo ya ce muna shi ne ɗan’iya

Sabuwar jam’iyyar ta zo mubi ta

bai ɗaya ‘yan Najeriya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Shi biki ka san mai zuciya ake gaya ma

Ko ɗan zai zo maka

Ka kira mai naira wawa idan ya zo

Naira zai sammaka

Kuma in ka karɓa bawa yake ganin ka

a kullum don haka

Kurciya kukanki jawabi akwai cikinta

ga ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Tafiyar yanci talakawa mu kama APC Najeriya

‘yan amana sun haɗa kansu sun fito da jam’iyya mai tarbiya

Kun ji wancan ma babban cikinsu y ace da tasu bat a da tariya,

Su da kansu suke furucin haka ba ta zuwa

na zauna lafiya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Zan kira Manyan Jam’iyyar na karrama su

na yo masu jinjina

Zan kira babban jirgi mai riƙon amana

Sarkin dangana

Ga ni fa alaramma ba kuskure idan na yi

Ku yi mana magana

Innallaha Ma’assabirina ya fi son wannan

mai duniya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Janar Buhari ikon Allah ka zudda

Kwallakan Najeriya

Kun ci zaɓe an murɗe mana hayaniya

Za mui kai ka tsaya

Ka hana mu mu ɗau doka a hannu

Al’ummar Najeriya

Lokaci in ya yi uban kuturu kaɗan ya yi

yai mana fariya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Ɗan amana yau na zo gare ka ga shi zan

doka maka tambura

Ka riƙe Allah Sarkin aiki El-Rufa’i

yau ka gagara

Maƙiyanka suna ta fushi El-Rufa’i ka

sa duk sun tunzura

El-Rufa’i minista ne a lokacin su wancan

Kai an gauraya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Ka riga ka kai sama duk maƙiyanka

Gwamna sun koma ƙasa

Ga shi kun yi sake ɗan zaki ya girma

dole ku dudduƙa masa

Tun da ya riƙe Allah ‘yan Jahar

Nasarawa suna gode masa

Tanko Almakura ‘yan Jahar Nasarawa

mun zauna lafiya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Yau Jahar Nasarawa mun sami

Lafiya ga aiki kai mana

Kai kaɗai ne tilo gwamna a jam’iyyar

Sarki mai dangana

Kafi mai allo da ƙafafunsa basu

mai rana sai jingina

Ba batun son kai na yi ba,

Nasarawa dole mu zauna lafiya.

 

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

 

Jagora: Kuma duk haɗamar mai handama

Wallahi bai iya ɗaukar duniya

Mai yawan bacci in ya sha hura ku duba

kar ku yi tambaya

Wadda ya yi biyayya haƙƙin uwa, uba

ya zauna lafiya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu,

Mun amince ‘yan Najeriya.

Jagora: Yau ina Sardauna Sir Ahmadu Bello

Gamji ka ji firimiya

Yau ina gwarzo Nnamdi Azikiwe

duk sun bar duniya

Sir Abuabkar Tafawa Balewa shi ma ya bad duniya

Mun yabawa Akintola ‘yan ƙasa

mu dudduba Najeriya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Wai ina takwara Janar Murtala Ramat ya bar duniya

Ba su Awolowo, Aminu Kano, Bakin zuwo

Sun bar duniya

Da a ce mun kwaikwayi tsarinsu da

Ƙasa ta zauna lafiya

Dole zan koka Najeriya ƙasa ta gado

Ta hau kan ƙaya.

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Zamfarawa AbdulAziz Yari ya yi komai

Allah taya maka

Mai amana ne Ahmad Sani ɗan Yarima

Allah taya maka

Manya gatan wasa Sanata Yarima mun ta yaba maka

Ka yi komai mun gode maka

Al’umma duk Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Kariga kai riba ka samu duniya Saura ma lahira

Kui ta cizon yatsa ya sha gabanku jikokin yan gambara

Tun da ka yi minista birnin Abuja

Allah yai maka Sutura El-Rufa’i ka taka

Je ko’ina muna bayanku da gaskiya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Bazawara wa zai mata lalle

Budurwa aka wa ba a daɗi

Sabuwar Jam’iyya tamu ce ta kira kowa don sun faɗi

Manyanmu suna lasan zuma talakawa su ko sai maɗi

Taimaka mana APC zo ki karɓi mulkin ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Tun da ka riƙe Allah mai gaskiya siyasa ya ce ba daɗi

In ka hau mulki ga shawara janar

ɓarayi kai masu damƙar biri

In ka hau mulki na tabbata masu saɓon ma su bari

Duk rashin kunyar marashi kunya idan ka

hau mulki tilas zai sunkuya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Sanata Bola Ahmad na Tinibu yau ku ne Najeriya

Baka tsoron wancan bakinsa sai ka ce mashin ɗin taliya

Gaskiya daɗi sanata Asuwaju Ahmad ba ya fariya

Duk rashin kunyar marar kunya idan ya zo tilas zai sunkuya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Aniyar farko APC ta ce karatu kyauta kun jiya

Ga garaɓasa ta zo sai mu zo mu kama ‘yan Najeriya

Mai kamar zai je aka aika don zuciyarmu ta zauna lafiya

Gaskiya ta zo al’umma farin ciki duka ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Wanda ya riƙe Allah Sarki ba ya shirka, baya tagaiyara

Tafiyar mesa bisa tsandari ya yi tatata ko jangora

An yaba da haɗin jam’iyyun ƙasarmu don ceton Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Tattalin daɗi haka mai haƙuri yakan ɗau dutsi yai miya

Dole ne mai son Najeriya ya ɗauki APC Najeriya

Yan uba sun ɗau Najeriya ƙasarsu ce talakawa kun jiya

Ban da zalunci a ƙasar nan, manyan macuta ne Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Ba tsaro a ƙasar nan ɗansanda yana tsoron saka yuniform

Mun shiga uku ‘yan Najeriya ga ƙasarmu tana fama daba

Wasu na hotel kwana bakwai sukan yi

Kwanta katifa vitaform

Ya ki zo jam’iyyar APC ki taimaka wa ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Tambaya zan yo wa ye za ya ba da amsar wannan tambaya

Tambayar biyu ce ku haɗa sai ku bani amsa in har kun iya

Kun ga mulki Allah shi ne ka bai wa wanda ya so ba tambaya

Kin riga-fata kun ce ƙaddara jarabta ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Shimfiɗar fuska ai ta fi a shimfiɗa maka sabon darduma

Kun ga jam’iyyar nan ta zo da gaskiya to sai mai azzama

Ko a tarihi an yo Adam ku bincika mini sam ba Adama

Ƙirƙiren wani duk mai bincike a rayuwa shirme ne fariya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Shi kiran Sallah kurma ai ba zai ba donn bakin ba hikima

Rabbu ne ya hana masa in wani ne da kurma asha rigima

Da makaho ga kurma sun haɗa kai wai za su yi rigima

Kai kake bai wa mara gata mai sama Allah ga Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Sannu Maliya ba ki kafewa duk jama’a sun ɗiba sun bari

Sannu baya goya marayu da mai Uwar ma sam ba ka bari

Tafiyar nan tamu da nasara da damina ne sai ga hadari

Tafiyar APC al’ummar ƙasarmu kowa sai yai lafiya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Sannu ƙangi wan ganga mai buga ka sai an nemi mai ciki

Jam’iyyar APC ke za ki mai da sojojin nan bariki

Wanga mulkin soja suke yi koko farar hula ke shamaki

Yan uwana ‘yan Najeriya soja suna mulkin Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Mun ji komai mun gano tsiyarku ‘yan ƙasa fifti-fifti suke

Su suna tatsar nonon, shi gwanin ƙaho suka ce mashi ya riƙe

Kun shiga uku yan Najeriya shugaban na ƙasa ko ya yaƙe

Jam’iyya ta zo ta gamayya ke za ki ƙwato ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Mutuwa rigar kowa ce da zan iya tau kam da na kwaɓe

Mutuwa yankan ƙauna ta wuce da gwarzo Chuba Okadibo

Da ruwa yashi ko ka dunƙule kasan hannu sai ya rabe

Jarqasa APC ta dunƙule rabewa babu daliliya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Ga shi taro yay taro duniya gidan daɗi inji mai kwabo

Lahira ta ɗau baƙi maza suna can chuba Okadibo

Da ana dawowa taron ga ‘yan uwa sai kun ga Okadibo

‘Yan uwa APC ta zo ki zo ki ceto ‘yan Najeriya

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Jagora: Sabuwa ta zo APC mu mun amince ‘yan Najeriya

Zamfara ma ta bi, Abdulaziz Yari yai komai kuma mun yaba

Fashola ya zo Jihar Lagos ki taso ai tuni mun yaba

Jahar Ogun ta bi, Amos Adekunle shi ma ya zo mun yaba

Jahar Oyo sun bi, Kayode Fayomi shi ma ya zo mun yaba

Jahar Osun sun bi, Ra’uf Aribe ya zo shi ma mun yaba

Edo ma ta zo, Adam Ashomole shi ma ya zo mun yaba

Imo ma sun bi, Rochas Okorocha Shi ma ya zo mun yaba

Yobe ma ta zo, Gaidam Ibrahim ya zo mun yaba

Barno ma ta zo, Kashim Shattima ya zo shi ma mun yaba

Nasarawa ma ta zo, Tanko Almakura shima ya zo mun yaba

 

Amshi: Sabuwa ta zo APCnmu

Mun amince ‘yan Najeriya

Ku zo mu kama gaskiya ta zo Najeriya

Jagora: Gaskiya ta zo

Amshi: Mun karɓe ta ƙauyuka birni Najeriya hannu bi-biyu

Jagora: Mun karɓe ta hannuwa bi-biyu Najeriya

Amshi: Kowa ya bi

Jagora: Sabuwar Jam’iyya APC

Amshi: Gaskiya ta zo

Jagora:/ Ku zo mu kama gaskiya ta zo Najeriya

Amshi:

Jagora: Gaskiya ta zo ku zo mu karɓe ta hannu bi-biyu Najeriya

Jagora:/ Kun karɓe ta hannuwa bi-biyu Najeriya kowa ya bi

Amshi

Post a Comment

0 Comments